Shafi na 2

193 18 0
                                    

*•••SANADIN MAHAIFINA•••*
        _[ILLAR FURUCI]_
       _Story by SaNaz_deeyah_

*KARAMCI WRITERS ASSOCIATION*📚
_[Karamci tushen mu'amula ta gari]_

Visit to like our page on facebook https://www.facebook.com/110308337320465?referrer=whatsapp

On Youtube https://youtube.com/channel/UC1cigRjL8UfjxSLNtt-x4MQ

_Gajeren labari da yake nuna illar mummunan furucin iyaye ga ƴaƴansu._

'''Sadaukarwa ga Asmiey Abdul(Husnah Sojah)'''

         Shafi na 2

Hannatu kuwa gaba ɗaya ta saki baki tana kallon Jannat. "Dama an kusa aurenki baki faɗa mana ba, mu tanadi wani abu" ƴar dariya tayi tare da faɗin "Haba Umma me zaku tanada, aini zuwanku kaɗai ya wadatar" Sa'ad kuwa gaba ɗaya jikinsa ya mutu, ya kasa cewa komai.
Umma ta lura da hakan, kuma ta tausaya masa amma sai ta share dan kada Jannat ta gane duk  sun shiga damuwa.

"To Hannatu wannan shine na ƴammata, ga na kamu, ga na dinner yanzu kin ga dole kije gidanmu ko?"

Murmushin ƙarfin hali tayi sannan tace "Ai zanzo kafin bikin ma. Yaushe ne bikin kuma nawa ne ankon?"

"Saura wata biyu bikin, anko kuwa kyauta nayi miki.Wannan ma Mommy ce tace a kawowa Umma ankon iyaye."

"Haba dai irin wannan wahala haka, ku bar mu kawai muyi da kanmu" Cewar Umma.

"Umma taya za'a bari kuyi da kanku? Gaba ɗaga ƴan gida kyauta aka musu anko, kuma kuna daga cikinsu"

"To mungode Allah ya saka da alkhairi"

"Amin Umma amma kunfi ƙarfin haka a gurina"

Godiya suka ƙarayi sannan ta miƙe tana faɗin "Umma ni zan wuce sai na ƙara leƙowa"

"To Jannat mun gode ki gaida ƴan gidan"

"Zasuji, ke kuma Hannatu, ina nan ina jira ki cika alƙawari, karki damu idan zanzo ai zan kiraki a waya"

"To shikenan." ta faɗa sannan ta saka kai ta fita. "Yaya ka bita ka faɗa mata kana sonta."

"Amfanin hakan ya wuce" Umma ta faɗa tare da cewa "Kaje ka rakata bakin mota mana."

Jikinsa gaba ɗaya ya mutu haka ya tashi ya fita. Tana ganinsa ta saki murmushi. "Naga duk jikinka ya mutu"
Ajiyar zuciya yayi sannan yace "Jannat yanzu idan kika yi aure shikenan ba zamu sake ganinki ba."

Dariya tayi tare da cewa "Oh wai wannan dalilin ne ya saka ka tashi hankalinka?"

"Eh mana domin na san ba lallai mijinki ya yarda ki riƙa zuwa ba"

Rufe baki tayi tana dariya "Dan Allah kada ka damu kanka kaji, kuma fa ƴan gida ne, kuma na san babu yadda za'ai Khalil ya hanani zuwa nan, domin kuwa ya san yadda na ɗaukeku, dan haka ka kwantar da hankalinka kaji, insha Allahu babu abinda zai rabani daku"

"Shikenan Jannat amma...." Sai kuma yayi shiru.
"Amma me? Dan Allah ka faɗa min abinda ke damunka domin nasan ba wannan kaɗai bane, kuma akwai abinda kake son faɗa min ka kasa"

"Babu komai Jannat kinsan babu ɓoye-ɓoye tsakani na dake"

"To Allah yasa da gaske kake, zan tafi domin su Safina suna jira na za muje gidan kakannin mu"

"To shikenan ki gaida ƴan gidan"
"Zasu ji" shiya buɗe mata ƙofar ta shiga ya rufe.

_*Bayan Wata ɗaya da sati biyu*_

Yana zaune a kan tabarma da aka shimfiɗa a tsakar gida, kallo ɗaya zaka masa ka gane akwai damuwa a tattare dashi. Hannatu tazo ta zauna gefensa tare da faɗin "Yaya dan Allah ka fidda soyayyarta a cikin zuciyarka tunda ka san bazaka taɓa samun ta"

SANADIN MAHAIFINA (ILLAR FURUCI) DONE✅Where stories live. Discover now