Shafi na 12

112 10 0
                                    

*•••SANADIN MAHAIFINA•••*
           _[ILLAR FURUCI]_
'''Wattpad@ SaNaz_deeyah'''

*KARAMCI WRITERS ASSOCIATION*
  _[Karamci tushen mu'amala tagari]_
     Email-Karamciwritersass@gmail.com

Visit to like my page on facebook https://www.facebook.com/110308337320465?referrer=whatsapp

On youtube https://youtube.com/channel/UC1cigRjL8UfjxSLNtt-x4MQ

On Wattpad https://my.w.tt/NuwIi6ubScb

_Sadaukarwa ga Asmiey Abdul(Husnah Soja)_

*Ina yiwa ɗaukacin al'umma barka da sallah, ubangiji ya maimaita mana, ya kuma karɓi ibadunmu amin.*

                    '''Shafi na 12'''

________________📲Cikin tashin hankali Ummu ta kira likitoci, aka zo aka fitar da Mommy daga ɗakin. Ta suma bata san a ina take ba.

Ummu waya ta ɗauko daga cikin jakarta ta sanarwa da Alhaji Ma'azu halin da ake ciki, ya ce ga shi nan zuwa.

*1 hour later*

A hankali ta buɗe idanunta, akan silin ta fara diresu kafin ta kalli mutanen da ke gefenta. Ganin Ummu da Daddy ne ya saka tayi saurin tashi zaune, dan tayi tunanin duk abinda ya faru mafarki ne, sai da ta gansu tsaye a kanta, kuma a asibiti.

Drip ɗin ta fuzge, tana ƙoƙarin sauka daga gadon. Ummu ta riƙeta tare da faɗin "Dan Allah ki bari ki samu hutu tukun"

"Hutu fa kike faɗa Hajiya Bilki? Ina naga hutu bayan yarana wanda su kaɗai na mallaka suna cikin wani hali"

Daddy ya matso jikin gadon yana faɗin "Falmata dan Allah ki nutsu, ki jira Doctor yazo domin ke ma ba cikakkiyar lafiya ne dake ba"

Ranta a ɓace ta kalleshi, sai kuma ta fashe da kuka. "Duk abinda ya sami ƴaƴana kaina sila, kaine mahaifinsu amma kuma baka son su, da kanka kayiwa ƴaƴanka baki, yanzu ga illar furucin ka nan, na tsane ka wallahi, kuma idan har na rasa ƴaƴana sai nayi shari'a da kai, domin muguwar zuciyarka ce ta jefa su ga halaka" tashi tayi da sauri ta fita ta bar ɗakin.

Daddy ya zauna kan gado tare da dafe kai.
"Wai meke faruwa ne haka da har zata ce furucina ne ya jawo?"

"A'a har yanzu ai Jannat bata farka ba, haka itama Safina tana can unconscious, bamu san abinda ya faru da Jannat ba, amma ita Safina accident ne, Hajiya Falmata ta faɗi haka ne saboda tana ganin kamar korar da kayiwa Jannat ne ya jawo mata haka, tunda Doctor ya tabbatar mana cewa fyaɗe aka mata"

"Idan korar da nayi wa Jannat ce ta jawo haka ita Safina fa? Matar da take ɗakin mijinta, wannan ƙaddara ce kawai, Allah ya basu ikon cinye jarabawarsu"

"Amin ya rabbi"

"Ina Ahmad ɗin yazo kuwa?"

"Gaskiya bamu ga Ahmad ba, ko bai sani ba, ka dai kira number tashi dan ya kamata ace ya san halin da matar shi ke ciki, nima zan kira Farhan na faɗa mata"

"A'a ki bari sai gobe kada ki tada mata hankali saboda lokaci ya ƙure ki kirata yanzu"

"To shikenan, Allah ya kaimu goben"

"Amin" ya faɗa lokacin da yake dialing number Ahmad amma a kashe.

"Wayar tashi bata shiga, bari na kira Driver sai yaje gida ya sanar masa"

"Okay ba matsala"

              ******

Atamfa ce a jikinta ɗinkin doguwar riga orange color, ta yafa babban mayafinta dark green wanda touch ɗin atamfar ne.

SANADIN MAHAIFINA (ILLAR FURUCI) DONE✅Where stories live. Discover now