AishaMaaruf1
Cikin ɓacin rai Aabid ya ɗago kan shi a karo na farko ya ce"da mai kuɗi da talaka duk Allah ne yayi su, kuma a dare ɗaya mai kuɗi zai iya rasa dukiyar shi haka zalika talaka zai iya zama mai kuɗi, ki yi haƙuri idan kalamaina sun ɓata miki rai ", ya ƙarasa maganar shi tare da miƙewa ya fice daga parlorn, saurin miƙewa Bibi ta yi ta bi bayan shi tana kiran sunan shi, Uffan Ummi ba ta ce ba ta miƙe ta nufi ɗakinta, sam ba ta san auren nan amman kuma babu yadda ta iya, haka kawai take jin wani feeling na daban a cikin zuciyarta, most expecially idan ta kalli yaron...............
Wani murmushin mugunta Mummy ta yi ta gyara zamanta, kallan ta Halima ta yi ta ce"mai yasa zaki faɗi haka Mummy?, i think this is what you want?", miƙewa Mummy ta yi ta jefa cingum a bakinta tana tauna shi a hankali fuskarta ɗauke da murmushi idanta a kan Halima ta ce"komai na duniya da dabara ake yin shi, sabida haka ki zuba ido ki sha kallo", ta ƙarasa maganarta tare da juyawa ta bar parlorn, bin ta da kallo Halima tayi har ta ɓacewa ganinta.......................
Tura ƙofar ɗakin ta yi babu ko sallama ta shiga, daga nan baƙin ƙofa ta tsaya ta tokare hannunta da ƙofar tana wani makirin murmushi ta ce"ya kika ga wasan?", share hawayen da ke kan fuskarta Ammi ta yi amman kuma wasu na bin wasu, cikin ƙarfin hali da dakiyar zuciya ta ce...................................
masu karatu mu haɗu da ku a cikin sabon littafina mai suna "JINI ƊAYA", kar ku bari a baku labari, wanda ya karanta ne kawai zai iya bada labarin shi, is going to be super interesting in sha Allah......................
29/05/26
Friday.
Posted on Arewapen
02/08/26
Sunday.