Haulat2's Reading List
2 stories
DUBU JIKAR MAI CARBI by AmeeraAdam60
AmeeraAdam60
  • WpView
    Reads 9,112
  • WpVote
    Votes 276
  • WpPart
    Parts 14
Da sauri Yaya babba ta matsa baya tana zaro ido ta ce, "Dubu me nake gani kamar aski akanki." Dubu ta rushe da kuka ta ce, "Inno wallahi aski ya mini kuma wallahi ɗan iska ne." Cak Yaya Babba ta tana ƙarewa Dubu kallo sannan ta ce, "Dubu je ki can mu gani." Dubu ta tashi tana ƙobare ƙafafuwa saboda irin gwale-gwalen da ta sha. Ba su yi aune ba sai ga ni suka yi Yaya babba ta faɗa ɗaki ta rushe da kuka. Da sauri suka bi bayanta saboda kusan kowa bai ji daɗin abin da Aseem ya yi ba musamman Mahaifinsa, faɗa yake yi masa sosai sannan suka shiga ɗakin. Yaya babba kallonsu ta yi fuska a murtuke ta ce, "Garba ka tara mini ƴan uwanka saboda wannan ba maganar tsaye ba ce. Kuma idan har Aseem ya farke mini Dubu na rantse da Allah ba ita kaɗai ya yi wa illa ba, ya fi kowa shiga uku domin babu makarin maganin ƴan shafi mu lerar da za a bashi. Kai ni wallahi ban lamince ba ke Nafisa ke ce uwarsa wuce ki je ji bincike shi tas, don wallahi Idi ɗan wanzan ya mutu babu wani magani da zai karya laƙanin aikin, saboda aikin har da haɗin ƴan shafi mu lera." Tana gama maganar ta fisgo Dubu tana shafa mata suɗaɗɗen kanta ta ci gaba da cewa, "Ka ga yanda Kan Dubu ya sulle kamar bayan sulba. To kwarankatsa dubu idan har ka farketa kaima haka wurin zai shafe kamar bayan silba." Kallon-kallon aka fara yi da juna, jikin Hajiya Nafisa ya yi sanyi dukda ta san a tarbiyyar da suka bawa Aseem ba zai taɓa yi wa Dubu fyaɗe ba. Amma shaidar ɗan yau bata da tabbas, domin ɗa ne ka haifshe baka haifi halinsa ba. Babban abin da ya fi ɗaga hankalinta da ta ji an ce Aseem ɗin ta ya koma kamar bayan silba. Ita da take yi masa tanadin Yusra ƴar aminiyarta ya aura.
Lawh-Al-Mahfouz by TajawwalAlRuwh
TajawwalAlRuwh
  • WpView
    Reads 3,254
  • WpVote
    Votes 702
  • WpPart
    Parts 17
Ina hanya? Ina mafita? Ina zata bi ta ga haske a rayuwar ta? Ya zama dole tayi zabi tsakanin rayuwar ta da kuma abunda ta dade tana so da muradi a rayuwar ta. Ya zama dole tayi zabi tsakanin rayuwar ta da kuma farin cikin wanda ta fi so fiye da kowa da kuma komi a kaf fadin duniya. Koh a mafarki, Hadiza bata taba tunani irin wannan rana zai zo ba a rayuwar ta; bata taba tunanin zata sama kan ta a cikin rudun da take ciki ba sai dai kuma ta san cewar duk abunda ke faruwa a cikin rayuwar ta rubataccen lamari ne, wanda Allah ya riga ya rubuta faruwar shi tun kan ta zo duniya. Tana da tabbacin cewar da za a buda takardan Lawh-Al-Mahfouz, toh tabbas za a sama abunda ke faruwa da ita ta a cikin shafin da aka ware musamman dan rayuwar ta. Lawh-Al-Mahfouz is a story of pain Of sacrifice Of strife Of longing A story of undying love.