Novels ? ?
17 stories
JARIRI COMPLETE by AmeeraAdam60
JARIRI COMPLETE
AmeeraAdam60
  • Reads 17,498
  • Votes 1,086
  • Parts 25
A daren ranar da suka koma da daddare kimanin karfe biyun dare Inno ce ta fito fitsari ahanyarta ta dawowa, ta hango ƙaƙanin abu na tafiya idan yayi gaba sai ya dawo baya ya rangwaɗa kai gefe. A ɗan tsoroce Inno ta ce, "Toooo yau wacce irin ɗiban albarka nake gani da tsohon daren nan" ta ƙarasa magana tana haskashi da ƴar fitilarta. A zabure ta ja baya ganin jaririn Nusaiba ne tumɓur ko wando babu, washe mata baki yayi ya dafe ƙeya yana wani irin layi kamar wanda yasha ya maku, cikin wata irin murya ya cafe irin maganar Inno yace, "Tooo yau wacce irin ɗiban albarka nake gani da tsohon daren nan" tana faɗa yana wani irin tsalle kamar zai faɗo kan Inno, wurgar da butar tayi saboda tsoro ta fara gudu. Tsalle yayi ya caɓe zanin Inno har ya taɗe ta ta faɗi da rarrafe ta dingan rarrafawa tana ƙwala ihu, lokacin da ta ƙarasa ɗakinsu tuni ta daɗe da wurgar da zani daga ita sai ɗan fatarinta.
SO KO WAHALA by mumamnas2486
SO KO WAHALA
mumamnas2486
  • Reads 3,614
  • Votes 318
  • Parts 75
Labarin soyayya mai cike da rikici ga wani mutum mai suna Baban Mama, yana da Aure ya fara soyayya da ƴar maƙotansu yarinyar da har cikin gidansa gun matarshi ta ke shiga ,da ya ga kamar ba za'a bashi ba sai ya faɗa soyayya da abokiyar cinikinshi mai shekara sama da talatin hummm akwai cakwakiya fa
SHAFAFFU DA MAI by AmeeraAdam60
SHAFAFFU DA MAI
AmeeraAdam60
  • Reads 474
  • Votes 24
  • Parts 5
LITTAFIN GASA NE NA MATASAN MARUBUTA DAN ALLAH MASOYA KU NUNA MUN ƘAUNA AKWAI RANAR DA ZASU BAMU LINK MU BAKU ZAKU DANGWALA MANA VOTE, INA FATAN ZAKU BANI HAƊIN KAI.
HAYATUL NISA'I by Teemah-Shafyus
HAYATUL NISA'I
Teemah-Shafyus
  • Reads 21
  • Votes 7
  • Parts 1
Abubuwan rayuwar mata mabambanta wanda yashafi matan Africa da matan larabawa da sauran jinsin farare na duniya yadda suke tattalin rayuwar su wajan gyara a gargajiyance da kuma a zamanan ce
ASEELA COMPLETE by AmeeraAdam60
ASEELA COMPLETE
AmeeraAdam60
  • Reads 22,377
  • Votes 1,704
  • Parts 52
Ƙwarangwal ɗin suna tafe wani irin ruwa mai yauƙi na fita daga gaɓɓan jikinsu tamkar waɗanda aka kunna fanfo ajikinsu, daga kowanne ɓangaren hallita akwai shugabansu wanda shi ne yake kan gaba su kuma suna biye dashi abaya, hannu kowanne shugaba ɗauke yake da wani farin ƙyale da jikinsa yake da ɗishi-dishin jini, ahankali ta fara ɗaga ƙafarta tana ƙoƙarin ja da baya da niyyar guduwa sai dai nauyin jikinta shi ya hana ta gudu har suka ƙaraso inda take, mararta ce ta ɗan karta mata bayanta ya riƙe sannu ahankali ta tsugunna ta duƙa agurin wani irin azababben ciwo na cinta, jeruwa suka yi sahu-sahu sannan suka fara zagaye ta suna faɗin wasu kalmomi da sam bata fahimtar mai suke faɗa, " YAMDUMISA! YAMDUMISA!! YAMDUMISA BISRATIK KUZAR!!!, KIMBASA MIN! KIMBASA MIN!! KIMBASA MIN MAR FAZKINBAT!!! " ( BARKA! BARKA!! BARKA DAI SHUGABA!!!, DAWOWARKU NASARA CE! DAWOWARKU NASARA CE!! DAWOWARKU NASARA CE TARE DA FANSA!!! ) haka suka dinga zagayeta suna maimaita kalmomin bakinsu shugaban ɓangarori biyun masu ɗauke da farin ƙyallen nan suna zazzaga mata wannan kyalen akanta, ciwon da take ji ƙara tsananta yake banda ihu ba abinda takeyi sai kiran sunan KABEER take tana maimaitawa, idan abun ya kuma tsananta ta kuma kiran Kabeer ko Habeebee amma ko gezau basu fasa wannan surutan nasu ba kuma basu fasa zagayeta ba suna yarfa mata wannan farin ƙyallen ba, wani lokacin ma wannan ruwan mai yauƙi na ɗiga ajikinta, ita bata ma san suna yi ba saboda azabar ciwo fatanta kabeer ya kawo mata ɗauki. Ta ɗan ɗauki lokaci ahaka kamar minti talatin ahaka sai ji sukayi kukan jariri alokacin ta galabaita sosai amma ahaka take yunƙurin ɗaukar abinda ta haifa dan neman tsira daga garesu, sai dai kafin tayi wani yunƙuri tuni shugaban ƙwarangwal ɗin nan ya kai hannu yayin da shima shugaban mai mummunar hallitar shima ya kai hannunsa, atare suka suka ɗago jaririyar kowanne ya riƙe hannunta ɗaya yana faɗin, " KAGARSIN BIDA, KAGARSIN BIDA LANBISMA GIRUS " ( KA
MARWAN COMPLETE by AmeeraAdam60
MARWAN COMPLETE
AmeeraAdam60
  • Reads 21,636
  • Votes 2,356
  • Parts 35
Safwan yace, " dama inasan ganin Nazir akwai muhimmiyar maganar dana zo da ita nake san mu tattauna " yana gama faɗa mahaifiyar su Nazir ta rushe da kuka sannan tace, " Nazir baya magana hasalima baya cikin hayyacinsa baisan waye ma akansa, kallan yayan Nazir tayi ta ce, " kai je kaxo mai da Nazir " nan take ya tashi ya fice sai gashi da wheel chair da Nazir aciki sai kallan mutane yake yana zubda hawu hannuwansa da ƙafafu gaba ɗaya sun shanye, Safwan na ganinsa cikin tashin hankali yace, " Wannan ne Nazir ɗin mai ya sameshi? " wani sabon kukan mahaifiyar su Nazir ta ƙara sawa, cikin ƙarfin hali yayan Nazir ya fara magana, " aranar da mahaifinmu ya rasu Nazir yace mana zaije gidansu Maryam, to bayan y dawo muna zaune sai gani mukayi ya zabura yana ihu yana cewa bazai kuma ba, sai kuma muka ga yana ta surutai daga haka kawai sai gani mukayi ya yanke jiki ya faɗi, shikenan har yau ka ganshi ahaka kullin magani ake bashi amma ba sauƙi kullin ciwon gaba yake yi. " gaba ɗaya jikin Safwan ne yayi sanyi cikin sumutar baki Safwan yace, " tabbas Marwan ne " karaf yayan Nazir yace, " wai waye Marwan ɗin nan naji lokacin da yake ta sumbatu yana cewa Marwan kayi haƙuri, ko kuma abokin aikinsu ne dan wannan ciwon ba tantama sihiri ne. " Safwan gaba ɗaya tausayi da tsoron halin da Nazir ke ciki ya kama shi.
ƊAN BA ƘARA COMPLETE by AmeeraAdam60
ƊAN BA ƘARA COMPLETE
AmeeraAdam60
  • Reads 7,390
  • Votes 750
  • Parts 15
Salati goggo ta rafka tana ja da baya cikin tsoro take Fad'in, " me nake gani ni hansatu kamar danyen kifi ke mejidda zo ki tayani gani " mejidda atunaninta rikicin Goggo ne tana daga zaune ta cewa Goggo, " tunda kifin Kika gani ay shi d'in ne, kema Goggo Banda abinki kifin k'afa garshi da zai shigo cikin gida bama nan, idan nace kinfiye rigima kice zan gaya miki magana " ganin kifin na yi Mata murmushi yasa Goggo ta K'ara rafka wani salatin tana sakin tunkunyar tana yowa gaba, mejidda dariya takewa Goggo harda rik'e ciki tace, " Goggo wai me yake faruwa ne Dan Allah ko kunyar gudu bakiji ba? gudu kikeyi amma kamar me rawar Etigee" Goggo Bata bi ta Kan mejidda ba ta rabe ajikin katanga tana leken tunkunyar data jefar ,wani Kan kifi ta hango suna had'a ido ya K'ara kashe Mata ido daya😉 sannan ya washe Mata baki😃, daskarewa Goggo tayi cikin tashin hankali ta mik'a hannu tana nunawa Mejidda kifin, da saurinta Mejidda ta K'arasa gurin ba shiri ta dakata musamman yanda taga Kan kifin Yana wangale Mata baki, k'ank'ame Goggo tayi tana ihu cikin tashin hankali Take Fad'in, " wayyo Goggo Kan kifi Yana wangalen Baki zai cinyeni, ki taimake ni Goggo na yi gamo da Aljanin kifi ". Ita kanta Goggo abun tsoro yake Bata Amma sai ta D'an dake ta K'ara lek'awa Amma ga mamakinta sai taga tukunyar wayam, ko irin alamun jinin kifin babu. Goggo ta Jima tana kallan tukunyar Amma ko d'ishin kifi Bata gani ba, zame mejidda take Shirin yi daga jikinta caraf ta Kara k'ank'ame Goggo kamar za'a k'wace Mata ita, itama goggo Bata gama sake wa ba suna cikin Haka ba zato wani almajiri ya rafka ba ra, " Waaahiiideeeeeee " Me jidda ce ta Fad'a aguje cikin d'aki tabar goggo jikinta sai rawa yake ta Mara Mata baya, kafarta D'aya d'ingisa ta takeyi Amma alokacin Nan tuni ta take ta bata sani ba, Almajirin shi dariya ma abin ya bashi yi yake yana k'yak'yatawa, goggo dake d'aki ta cika fam Dan Jin yanda Almajiri ke b'ab'b'aka dariya, lek'awa tayi Dan tayi Masa magana
TSANTSAR BUTULCI COMPLETE by AmeeraAdam60
TSANTSAR BUTULCI COMPLETE
AmeeraAdam60
  • Reads 23,322
  • Votes 1,729
  • Parts 47
Ko daga jin sunan littafin basai na baku labarin irin BUTULCIN da za'a tafka acikinsa ba, labari ne me tab'a zuciyar me karatu ya kunshi darasi acikinsa, Kuma izna ne ga azzaluman mutane, kubiyo zasu fahimci abinda nake nufi.
YAWON SALLR HJY IYA Complete by AmeeraAdam60
YAWON SALLR HJY IYA Complete
AmeeraAdam60
  • Reads 2,959
  • Votes 476
  • Parts 26
Gudu yakeyi iya karfinsa amma saboda yanayin girma ga tsufa lokaci guda suka cin masa. A tsakiya suka saka shi suna kokarin rike hannuwan sa, dan tsoho yayi wani kukan kura cikin karaji irin yanda jariman india sukeyi idan suka fusata, yasa gwiwar hannuwan sa ya kai musu duka yana fadin, " wallahi bansan da makiya nake tafe ba sai yanxu idan kuka maidani cikin motar nan ban yafe muku ba. Ku sake ni na karasa bichi a kafa, idan kuka kaini mota wallahi alhakin mutuwata a wuyanku yake, cikin hanzari suka kara matsowa zasu kama dan tsoho, aykuwa ya yi sauri ya matsa baya hadi da buga kafa daya, ya kara kwalla kara yana fadin, " yeeeeeeeee ku matsaaaaaaaa ko in ma ke kuuuuuuu, ya karasa fada yana dunkule hannuwa har huci yake. Daya daga cikinsu ya kallin dayen yace, " wai kuwa Anya bazamu kyale tsohon nan ba yaje yayi ta tafiyarsa, tunda anasan ceton rayuwarsa yana san yayiwa mutane illa, kana ganin yanda ya kaimun duka a gefen fuska badan na kauce ba da ya gwabjeni yayi mun mahangurba, " kai haba yanxu tsohon nan ne zai gagaremu, idan aka ce mun kasa kamo shi ba muji kunya ba dan Allah rabu dashi bari kaga muma karfi zamu nuna masa, muna zuwa ciccibarsa zamuyi farat daya zamuyi masa. Aykuwa suka tunkari dan tsoho me buhu, yana ganin sunyo kansa gadan-gadan ya fara kai duka ta ko ina, yana yi yana ja baya sai kuma yayo gaba kamar zai doko wani daga cikin su, yan da kasan yana filin danbe. Basu bi ta kansa ba, sukub haka suka sun kuci dan tsoho suka mammakure hannusa a hammatarsu sai wutsul-wutsul yake da kafafuwa, yanayi yana wani karaji shi bai yarda ba dole kwacewa zaiyi daga hannunsu. Bakin motar suka karaso suna kokarin saka dan tsoho sai fisgewa yake yana ciccijewa har suka samu suka tura shi ciki, wani daga gefe ya dan leko su yana fadin, " to ita ma iya ku sata aciki man, kunga kun huta, idan fa kukayi sake tsohon nan ya kubce wallahi dawa zai shiga, dan na lura motar nan ta tsora tasu dayawa, juyawa sukayi zasu dauko hjy iya.
Being The Sheikh's Second Bride by author_BibzMina
Being The Sheikh's Second Bride
author_BibzMina
  • Reads 722,653
  • Votes 44,307
  • Parts 68
Highest In Spiritual:#1 What's Hot (4/06/2018) Aamanah is the wife to the next chief of the Al-Umair tribe,Hamza.She just found out she's barren yet she has Hamza's support but the tribe has a lot to say to her,,and its not good. Nazmeera is Aamanah's cousin and closest friend.She has not had a perfect life,she was thrown out of her father's tribe and her uncle took her in. When the question comes to not just saving the treaty of both tribes but also Aamanah's married life,what extents will Nazmeera go to save it or will she watch it all crumble? (Book Two in The Sheikh's Brides Series