Rukayya
126 stories
INDO SARƘA COMPLETE by AmeeraAdam60
AmeeraAdam60
  • WpView
    Reads 79,058
  • WpVote
    Votes 5,550
  • WpPart
    Parts 57
Cikin dare lokacin ƙafa duk ta ɗauke banda kukan tsuntsaye ba abunda yake tashi, alokacin ta farka daga bacci kayan wajen Goggo tasa ta ɗauko zumbulelen farin hijabin tasa, kwandon kayan kwalliyarta da shafe sati bata buɗeshi ba, ta buɗe ta ɗauko hoda ta zazzaga ta shafe fuskarta, hannu da ƙafafuwa Ludayin miyar Baba Huwaila da tun rana ta ɓoyeshi ta ɗauka ta sa a hijabi, ƴar fitilarta ta ɗauka ta fito daga ɗaki saɗaf-saɗaf ta je wajen bakin ƙofa ahankali ta zare sakata ta fice, kamar Aljana ita kaɗai ce a waje haka ta samu ta ƙarasa bayan katangar gidan Mai Gari ( _Dake gida huɗu ne tsakanin gidana Baba Huwaila da na Mai Gari_) ta kamata ta ɗane ta dirga. A hankali ta ɗaga labulen ɗakin Mai Gari ta shiga ta same shi a kwance baccinsa yake hankali kwance, toshe bakinta tayi tana dariya ƙasa-ƙasa musamman da ta tuna irin muguntar da zata yiwa Mai Gari, sai da tayi ta gama ta koma saitin kan Mai Gari ta zaro ludayin miyar ta dai-dai ci kan sa ta bashi ƙwaaal, azabure Mai Gari ya tashi yana susar gurin baya yaja ganin mutum tsaye cikin fararen kaya. Indo canja murya tayi shigen ta Goggo sannan ta fara magana, " Ni ce Goggo Kakar Indo Sarƙa nazo tafiya kai cen makwancina tunda cin Amana zakayi " Mai Gari cikinsa ne ya juya baiyi aune ba sai ji yayi ɗumi na bin wandonsa, Indo na ganin Fitsari na bin ƙafar Mai Gari ta gimtse Dariyarta ta kuma cewa.....🥱
FATU A BIRNI (Complete) by suwaibamuhammad36
suwaibamuhammad36
  • WpView
    Reads 74,640
  • WpVote
    Votes 2,361
  • WpPart
    Parts 18
"I promise you Mami, zan nemo miki ƴar'uwarki a duk inda take a faɗin ƙasar nan. SULTAN promises you that." Sultan ya shiga ya fita, har ya aikata abunda ba'a tsammani domin ya cika wannan alƙawari da ya ɗaukawar mahaifiyarshi, aka yi dace ya gano inda take. Wani abun takaici shine a maimakon ya samu ƴar'uwar Maminshi kamar yanda ya ci buri, sai ya haɗu da ƴarta kwalli ɗaya tak da ta haifa a duniya ta bari cikin ƙauyanci da kuma rashin wayewa. Baƙin cikinshi bai tsaya a nan ba, domin dattijon da yake riƙe da ita a take ya aura masa yarinyar ba tare da ya iya kaucewa wannan mummunan ƙaddaran ba. Ya tafi ya barta ba tare da ya sake waiwayarta ba, ya kuma tafi da wani kaso na zuciyarta ba tare da ya sani ba. Fatu (Fatima) ta ji haushi, sannan tana cikin baƙin cikin tafiyar da mijinta yayi ya barta. Tun tana tsumayinshi tana fatan ya dawo ya ɗauketa, har zuciyarta ta daskare da tsantsar tsanarshi na wofintar da ita da yayi, da kuma banzatar da igiyar aurensa dake kanta. Tayi alƙawarin ɗaukan fansa, ta kuma yi alƙawarin raba tsakaninsu ko da duniya zasu taru su hanata. Sai ta nemo shi a duk inda yake. Ta shiga cikin Birni nemansa, a nan kuma ƙaddara ya gifta tsakaninsu suka haɗu a lokaci da kuma yanayin da basu yi tsammani ba. Shi kuma ganin kyakkyawar baƙuwar fuska mai ɗauke da kamala, ya sashi faɗawa cikin sonta dumu-dumu ba tare da ya shiryawa hakan ba, kuma ba tare da ya gane cewa Matarsa ce ta Sunnah ba, Halal ɗinsa. Me zai faru idan Fatu ta haɗu da mutumin da ta ƙullata tsawon shekaru a yayin da shi kuma yake jinta a zuciyarsa tamkar ruhinsa? Me kuma zai faru Idan wasu sirrikan suka bayyana a lokacin da ba'a shirya musu ba? Fatu mace ce ɗaya mai hali mabanbanta; Fatu- Matar Sultan. Fatima- Budurwar Sultan.
MAMANA CE  by HauwauSalisu
HauwauSalisu
  • WpView
    Reads 20,438
  • WpVote
    Votes 1,121
  • WpPart
    Parts 30
littafine da ke dauke da rayuwar wata yarinya bakauya da wani dan sarki , mahaifiyarta mahaukaciyar ce kuma kurma ce , babanta Makaho ne sannan kuma gurgu ne . Tun hduwarsu ta farko suka aikata ma junansu laifin da ba wanda zai iya yafema wani har suka girma da burin daukar fansa ,duk da sunyi rayuwar Abokan taka batare da sunsan sune makiyan nan ba masu burin daukar fansa ga junansu . ku dai bibiyi wannan labarin dan ganin yanda zata kasance tsakaninsu
FURUCI NA NE by HauwaAUsmanjiddarh
HauwaAUsmanjiddarh
  • WpView
    Reads 55,171
  • WpVote
    Votes 3,770
  • WpPart
    Parts 37
"Baba meyasa kazama boka bokanci fa haramun ne kuma k'arya ne shirka ne Allah baya yafewa mushirki..... "ke Izza ki kiyayeni idan kika nemi d'agamin hankali abin bazai miki kyau ba dan ni zan iyayin komai akan cikar burina na kashe Faida ma balle ke zaki kawo min maganar banza yanzu kinga wani abin da ya Dan ganci bokan ci ne atare dani na dena aikin ki kad'ai zan cigaba dayi shima idan burin mu yacika kika auri daya daga ahalin gidan nan zan bari na tuba meye Allah baya yafewa nide nasan zai yafemin". shiru tayi can ta nisa tace'' to shikenan Baba ance idan zaka sha giya shata dubu ni megaba dayan nake so Nasuru din". dariya yayi yace"shegiya Naira ba babba ba yaro ni kai na naso haka naso ace Nasara kika mallaka amma sam taurari sun nuna ba al'kairi taurarin ku basu hadu ba ba aure a tsakanin ku da Nasara shine na hakura amma ina lefin Aiban ko Agrif din'." tace'' amma Baba nafison Agrif din dan shine akusa da Nasara kaga yafi sauran sanin sirrin komai na dukiyar ". murmushi yayi yace"yanda kike so haka za ayi wa gareni inba keba".
'YAR HUTU (LABARIN KAUSAR DA BINTA) Editing by Ishamoha
Ishamoha
  • WpView
    Reads 296,838
  • WpVote
    Votes 23,595
  • WpPart
    Parts 74
Ta taso a gidan hutu, gidan da ko tsinsiya bata dauka tsabar hutu, soyayya takeyi mai tsafta da masoyin ta kuma sanyin idaniyarta wanda da za'a bude kirjin ta se anyi mamakin irin son da take mishi amma sedai kash HUTU ya sangartar da ita ya kuma hanata kula da sanyin idaniyarta yanda ya kamata, shin wannan soyayya zata dore? Bakar wahalan da takesha ba karami bane a hannun matar uba, tsabar tsana da rashin son ganin er baiwar Allahn da ko shekara sha hudu bata karasa ba zata turata birni kuruwanci bayan tanada masaniyar cewar mafiyarta ta tsine mata duk ranar da ta bawa wanda ba maharraminta ba jikinta, shin tazayi abinda aka tura yi kokuwa ?
TUBALIN TOKA by SalmaMasudNadabo
SalmaMasudNadabo
  • WpView
    Reads 12,666
  • WpVote
    Votes 779
  • WpPart
    Parts 21
bana tunanin zan iya rayuwar aure da bagidajiya d'iyar qanwar mahaifina wadda mahaifina ya za6a min a matsayin matar aure bayan ina da nawa za6in, ya rayuwata zata kasance zaman aure da mashayi manemin mata wanda sam baya so na bayan ina da nawa za6in nabi za6in iyaye na, wace irin rayuwar aure zanyi da mutunan ba sa son tallaka da wanne zan ji uwar miji na ko mijina?
LAMRAT  by nimcyluv
nimcyluv
  • WpView
    Reads 37,295
  • WpVote
    Votes 1,673
  • WpPart
    Parts 30
story of young girl and luv crises
'YAR SHUGABA by rahmakabir
rahmakabir
  • WpView
    Reads 51,767
  • WpVote
    Votes 3,129
  • WpPart
    Parts 40
*'Yar Shugaban k'asa ce* Queen Basma, ta hakimce a seat d'in baya ita kad'ai, sai Meena 'yar Governor Kaduna ce ita ke driving, sai Leema 'yar Sarkin Kano wacce take gefen Meena. K'aran wak'ar Music na Larabawa ke tashi a motan, dukkan su suna bin wak'ar tamkar sune suka rerata, sunayi suna rawa da jinsu da kad'a kai, kana ganin su kaga 'ya'yan gata, cike suke da farin ciki fal da nishad'i, domin ba suda wata damuwa ko matsala a rayuwansu. Motan baya itama na bodyguard ne, suke marawa motan Queen baya. Wani Matashin Saurayi wanda bai wuce shekara Talatin ba (30yrs), yake tafiya cikin sauri domin ya amso wa Ummansa nik'an masara da k'anwarsa Khadija ta kai ta aje, saboda zata wuce tallan kwai, hankalinsa yayi nisa sosai cikin tunani, baisan yahau kan titi ba. Meena ce taja mugun burki, ji kake k'iiiii kad'an ya rage ta buge shi, Aryan tsayawa yayi cak ya runtse ido yana fad'in *Innalillahi wa inna ilaihir rajuun* jira yake motan ta bigeshi domin ya riga ya sadak'ar motan zata kad'eshi, Cikin b'acin rai Queen Basma, Leema, Meena duk suka fito a motan, haka bodyguard suka yi parking akan hanya suka fito rik'e da bindigogi, cikin k'ank'anin lokaci suka had'a gosilo, mutane suka fara taruwa, ganin bindiga ne yasa kowa ya kama kansa, Queen Basma ta k'arasa kusa da Aryan bodyguard suka take mata baya, tsadadden k'amshin turarenta ne ya dawo da hankalin Aryan jikinsa, domin ji yayi wani k'amshi na ratsashi, bud'e ido yayi a hankali yayi tozali da kyakkyawar fuskan Queen wanda saida gabansa ya fad'i, nan take tsoro ya ziyarce shi, kallon k'asa da sama Queen Basma ta bisa dashi cike da jin haushinsa, kyamansa taji saboda wani irin warin zufa dake tashi a jikinsa, tattaro miyon bakinta tayi ta tofa masa a jikinsa tare da toshe hancinta da hankacif.
DUNIYA BIYU!!!  by jeeedorhh
jeeedorhh
  • WpView
    Reads 4,963
  • WpVote
    Votes 270
  • WpPart
    Parts 12
Gefen wasu samari uku da suke ta faman tada hayaki kamar tashin duniya ta rakube, ta mikawa Bangis -mai shagon- kudin hannunta. Tace, "magi mai tauraro zaka bani na talatin da aji-no-moto na ashirin". Ya zuba mata a leda fara ya mika mata. Ta juya, wani daga cikin matasan ya fesar da hayakin daya busa, ya sauka akan fuskarta. Ta sanya hannu tana kore hayakin, tana tarin daya sarketa sakamakon shakar tabar da tayi har cikin makoshinta. Ta bude idanunta dake mata zafi, babu mamaki ma sunyi ja, ta saukesu akan wanda ya aikata mata wannan ta'addanci. Babu abinda ya dauki hankalinta a tattare dashi sai idanunshi, irin idanun dake nuna wuya da tsananin duhun rayuwa da suka gani, suka kuma jure. Duk rashin kunyar mutum, karya yake yace zai tsaga tsakiyar idanun mutumin nan yace zai mishi rashin kunya. Don haka ne yasa ta kame bakinta, 'yar Allah Ya isa din data dauko daga cikinta zata yi, ta tsaya a makoshinta. Ta sadda kai ta kara rabawa ta gefensu ta wuce. Bata sani ba, wani abu game da wannan bakon mutumi da bata taba gani ba, seems nagging. Ta kasa fitar dashi daga cikin ranta. Dai-dai zata karya kwana, ta juya tana kara kallon tiredar. Yanzu ya fito daga cikin tiredar, yana tsaye daga waje. Sai dai kaifafan idanuwan nan nashi suna kanta kyam. Wata irin kunya da faduwar gaba suka rufeta, musamman dan guntun murmushin da taga yana yi mata. Tayi saurin yin kasa da kanta, wani dan karamin murmushi itama yana ziyartar bakinta, kafin ta juya da sauri ta karya kwanar.
wata miyar by leematrimi
leematrimi
  • WpView
    Reads 4,898
  • WpVote
    Votes 402
  • WpPart
    Parts 41
labarinl ne daya faru akan yarinya qarama Mai qarancin shekaru da Wanda ahalin da Suka wadata zuciyarsu da son zuciya da kwadayi