Feedynbash Stories

Refine by tag:
feedynbash
WpAddbatulmamman
feedynbash
WpAddbatulmamman

5 Stories

  • GIYAR MULKI by zm-chubado
    zm-chubado
    • WpView
      Reads 163
    • WpPart
      Parts 2
    Akwai wata irin giya da idan mutum ya sha take gusar da hankali da imani. barasa ce mai sanya ƙishirwar mulki, wadda ke sa zuciya ta manta Allah, ta manta iyaye, ta manta duk wata alaƙa ta jini. GIYAR MULKI labarin Alhaji Shamsu, ɗan siyasar da naiman mulki ya rufe masa idanu ya aikata abin da duniya tayi Allah wadai da shi, wanda ko a zamanin jahiliya ba'a taɓa jin irinsa ba. Ya sadaukar da mahaifiyarsa Talatu, mace mai tsoron Allah da gudun duniya, duk a kan kujerar da ba shi da tabbacin mallakarta.
  • DA NA SANI by zm-chubado
    zm-chubado
    • WpView
      Reads 614
    • WpPart
      Parts 1
    wasu lokutan ƙaddara kan faɗawa Ahalinmu bawai don gazawarmu ba sedan kawai Allah ya jarraba imanin mu kamar yanda ya faɗawa Jameelah!! koma fiyeda hakan, a zaton mu mallakar miji me tarin dukiya da tangamemen gida da mota shine morewar rayuwa da jindaɗin duniya sedai wasu lokutan sam ba haka abin yake ba ta wata fuskar ma haɗarin dukiyar yafi talaucin illah da tashin hankali inji Jameelah
  • MURADIN RAI! by zm-chubado
    zm-chubado
    • WpView
      Reads 5,148
    • WpPart
      Parts 2
    A tsakanin duniya biyu mabanbanta, ƙaddara ta yi kutse a tsakanin rayuka biyu. Duk a ƙarƙashin kalma ɗaya. "soyayyah!" Tunaninta da duk wata nutsuwarta sun karkata ne akan yadda za ta samo masa mafita daga duhun ƙaddarar da ya dabaibaye rayuwarsa ya hanashi saƙat. sai dai a lokacin da take sanya ran cewa komai ya ƙare Yusuf zai koma ƙasarsa ta haihuwa, a wannan ranar tayi realizing cewa ta faɗa a tarkon masifaffiyar ƙaunarsa. Soyayyar mai tsanani ta ke yiwa Yusuf Hateym Al'qasrawi, kyakkyawan Balarabe ma'abocin Addinin musulunci,saɓanin ita da ta kasance KIRISTA wadda ba ta gasgata kaɗaituwa Ubangiji mahalicci ba. Abu ne mai matiƙar wahala ace Balarabe masani akan addini Musulunci ya amince da soyayyar Ahalul kitabi, duba da yadda suke nuna ƙyama ga duk wata ƙabila wadda ba ta kasance mai tsaftatacciyar nasaba irin ta su ba. Mutumin da yayi zurfi a so da ƙaunar Matarsa Yumnah Sulaiman El'ghanee,kyakkyawar Balarabiya mai kwarjini da cikakkiyar nasabar da takai a buga misali. Doctor Chioma Nonso Chukuma, ta Fahimci ba za ta iya karawa da Yumnah Sulaiman a zuciyar Yusuf Alqasrawi ba. Amma duk da haka ta lashi takobin sai ta kafa gwamnatinta a zuciyar Ɗan Mutan QASRAH, ko da hakan yana nufin za ta rasa komai da ta mallaka a rayuwarta ne gabaɗaya. Shin ya akeji idan zuciya ta zaɓi wanda Addini da Al'ada suka banbanta tsakanin ku? Soyayya ce? Ko masifa? Ƙaddara ce? Ko kuskure? Shin Yusuf Alqasrawi zai iya mantawa da matar da ya jima da mallakawa zuciyarsa ya karɓi Chioma a madadinta? Zainab Muhammad Chubaɗo 08102777485
  • RA'AYIN ZUCI... THE OPINION OF THE HEART  by zm-chubado
    zm-chubado
    • WpView
      Reads 779
    • WpPart
      Parts 10
    ta zabi Yusuf Attahiru a matsayin abokin rayuwarta na har abada, bayan ta saka ƙafa ta shure zabin iyayenta. ta biyewa ra'ayin zuciyarta kuma ta samu abinda take so, sai dai, soyayyar ba tai mata rana ba, illa jefata da tayi a cikin tarkon bala'in dangin miji!! Cikin ƙanƙanin lokaci su ka gigita mata lissafi ta dena gane komai saboda masifar su. Sai dai, a lokacin data yankewa kanta shawarar tserewa daga garesu tuni bakin alƙalami ya jima da bushewa✍️
  • SILAR KENAN by zm-chubado
    zm-chubado
    • WpView
      Reads 1,498
    • WpPart
      Parts 1
    Labarin Zuriya