Mahmaah_
A cikin ƙaramin gari na Nguru, Maryam yarinya ce mai manyan mafarkai-mafarkin ilimi, nasara, da canza rayuwarta. Cikin talauci da ƙaunar iyaye, wata rana ta zo da labarin da ya girgiza gidan su: ta samu scholarship zuwa jami'a.
A nesa kuma, cikin birnin Kano, Dr. Haidar-likita ne mai natsuwa, ƙwarewa da sirri a rayuwarsa. Yana ceton rayuka a asibiti, amma zuciyarsa na ɗauke da labarin da ba kowa ya sani ba.
Lokacin da kaddara ta fara saƙa labarinsu a hanya ɗaya, soyayya, jarabawa, da zabin rayuwa za su zo da tambayoyi masu nauyi:
Shin mafarki zai rinjayi zuciya?
Ko zuciya za ta hana mafarki cika?
Wannan labari ne na ilimi, ƙauna, ƙaddara da juriya-labarin da zai sa ka kasa ajiye waya har ka kai ƙarshe.