TARKON AURE,,,!!!

TARKON AURE,,,!!!

  • WpView
    Reads 3,706
  • WpVote
    Votes 129
  • WpPart
    Parts 1
WpMetadataReadOngoing<5 mins
WpMetadataNoticeLast published Thu, Jan 24, 2019
TARKON AURE...-1 Cikin sanda Jamila ta ke tafiya a soron gidan, rike da takalminta. Sannu a hankali kuma tana wuwwurga idanunta a zagayen gurin. Za ta shige kenan cikin gidan ba zato ba tsammani ta ji an riko mayafinta. Gabanta ya yi wani irin yankewa ya fadi. Ta kasa juyowa bare ta yi wani kwakkwaran motsi illa sauke numfashi da ta ke yi a jigace. Birkito da ita ya yi suka fuskanci juna sosai. "A tunaninki za ki iya yaudara ta Jamila? A tunaninki zan sha wahalar kaunarki a banza?" Ya girgiza kai, "Ba zan iya ba! Ba zan iya wasa da wannan damar ba, domin ni ma Dan Adam ne da yake da jini tare da tsoka. Ban da haka tanadin da muka jima muna yi wa yaranmu ba zai tashi a wofi ba!" Jamila ta kasa rike kukan da ya taho mata, duk da ba ta ba shi damar fitar da sauti sosai ba, amma tuni hawaye ya wanke kundukukin fuskarta. "Ka yafe min Jamilu, ka yafe min... Ka yi hakuri mu karbi wannan nannauyar kaddarar. Jamilu ya dinga irgiza kai har ta rufe baki, sannan ya ce, "Na ji... Na ji... Yanzu ya ki ke so a yi?" Ta yi shiru tana sunkuyar da kanta kasa. "Kina nufin na rabu da ke, na daina sonki? Na cire ki a matsayin da na ba ki na zamowa uwar 'ya'yana? Uhum Jamila kenan, kin san Allah daya kenan ko? To wallahi ba zan iya hakura da ke ba, don haka ya kamata ki sani idan ma kin manta ni Jamilu SadeeQ M ba irin wadannan ragwayen mazan nan ba ne da ake kwace soyayya a hannunsu ta ruwan sanyi ba". Ya juya ya koma cikin dakinsa, ya barta tana share hawaye. Ta jima a gurin, yana daga dakin yana jin sautin shesshekar kukanta, wani irin tausayinta yake ji har zuciyarsa, amma ba shi da yadda zai yi, dole ya zage damtse don mallakar makullin farin cikin rayuwarsa. Motsin da ta jiyo daga cikin gidan ya sa ta saurin shanye sautin kukan nata sannan ta fara kokarin saisaita nutsuwarta. "Ah Jamila? Ai gidanku zan je". Amina kanwar Jamilun ta fada bayan ta shigo soron ta ga Jamilar.
All Rights Reserved
Join the largest storytelling communityGet personalized story recommendations, save your favourites to your library, and comment and vote to grow your community.
Illustration

You may also like

  • Khuda Aur Mohabbat
  • INCOMPLETE PROMISE  (On Hold)
  • Addiction (KID×Conan/Shinichi)
  • Chupi Mohabbat (ON HOLD)
  • RAYUWAR CIKIN AURE
  • Eyes That See All Of It || Takemichi AU ||
  • Iztiraar
  • SHAREEF 2023
  • ISHMAN
  • Arrogant Destiny

Zoya believed in her God more than herself because she thinks that God only makes our today and tomorrow, if bad happens then good also happens. Well, she is absolutely right. We should have faith in god cause he is the only one who loves us unconditionally But Everything changed when he ruined her, just one mistake she did was messing up with him. He....raped her. you heard it right, just because of a small matter he did that to her. ••• "Ho gayi meri izzat barbaad ammi." She said as her tears were flowing as if blood. (I'm destroyed mom) "Galti kardi usne, chukani to padegi." He said while smirking. (She made a mistake, now she needs to pay.) ••• "Zoya, he is very powerful, you can't do anything, Even if you send him to jail, he would come out no matter what! and then he'll not spare you." Her friend said making her anger burst. "So, what do you mean to let him go easily?. She probably yelled at her. ••• "Dekhti hun kaise niklte ho bahar, Tumhe kya lga tumhari dhamkiyon se darti hun mai? Zindagi bhar salakho ke piche he rehna, kamse kam pata To chale kisi ladki ke sath kehlne ke baad kya hota hai." she said throwing the papers. (I'll see how you come out, what do you think I'm scared of you? Stay behind the bars for lifetime at least you realize what happens after playing with a girl?) "Zindagi bhar mujhe salakho ke piche rahna padega asi dhamki di thi na? 6 ghante ke andar tumhare ghar mein, tumhare smane, tumhare itne kareeb khada hun." he said pointing his gun at her forehead . ••• what will Zoya do? will he accept his mistake or he'll make it worst? will he seek for forgiveness from khuda (god). Will zoya believe in god and let the things happen in her life? with whom her destiny will end KHUDA or MOHABBAT ? Note:- This story doesn't contain any mature scene. It's not your typical fairytale, if you're looking for an innocent and weak girl then you're wrong. I wrote this when I was 13. Nee

More details
WpActionLinkContent Guidelines