KOMAI DAGA  ALLAH NE!!!( ARZIKI & ILIMI)

KOMAI DAGA ALLAH NE!!!( ARZIKI & ILIMI)

  • WpView
    Reads 2,356
  • WpVote
    Votes 114
  • WpPart
    Parts 15
WpMetadataReadOngoing1h 16m
WpMetadataNoticeLast published Sat, Feb 27, 2021
Rayuwa komai daga Allah ne. Mutum baya cika cikkanken mumini har sai ya yadda da kaddara Mai kyau ko akasinta. Komai ya same ka daga ALLAH NE! Babu Mai baka sai Allah. Sannan babu Mai maka illa sai da sanin Allah. Rayuwa cike take da jarabawa kala kala. Hakuri, rikon gaskiya da amana da tsoron Allah na Kai wa nasara. Yan uwa musani babu Mai mana sai ALLAH. Malami ko Boka bazai amfane ka da komai ba. Mu mika wa Allah lamarinmu Mai komai Mai kowa. Allah shi ya halicci duniya da lahira da abunda suke cikinsu. Mu kiyayi sallolonmu Biyar akan lokaci. Mu lazimci istigfari da salatin annabi. Azumin litinin da Alhamiz Sallar dare Sadaka Karatun Alkur'ani Sun ishe mu. Xamani ya lalace Allah kadai zai iya mana ba malami ko boka ba. Littafin nan zaizo da wata salo na daban. Rayuwa da jarabawar da take ciki. Yadda hakuri da rikon Allah da manzonsa da rikon gaskiya da amana kai kaiwa ga nasara. Illar kazamtacciyar soyayya . Tsaftatacciyar soyyaya da nasaran ta. Ku bini da sannu cikin wannan kirkirarriyar labarin nawa mai cike da abubuwan tausayi da daukan darasin .
All Rights Reserved
#1
mulki
WpChevronRight
Join the largest storytelling communityGet personalized story recommendations, save your favourites to your library, and comment and vote to grow your community.
Illustration

You may also like

  • AURE UKU(completed)
  • SAWUN GIWA...!🐘
  • KWANTAN ƁAUNA
  • NADIYA!
  • BAYA DA ƘURA
  • FATU A BIRNI (Complete)
  • RAYUWAR BADIYYA ✅
  • Kawaranai kimi ni..
  • KOWA YA GA ZABUWA...
  • AL'AJABIN SO

DR UMAIMAH USMAN BULAMA,Mace yar kimanin shekara ishirin da tara , Babbar surgeon A asibitin CITY TEACHING HOSPITAL , Aure Uku, ƴaƴanta uku . Mace mara san hayaniya wadda tasan kan Aikinta ,babu abunda tasa a gabanta illa bawa Aikinta babban muhimmanci kana yaranta wadda kaɗdarar samunsu ta rarraba mata Aure . Kalma ɗaya zaka faɗa ta bata mata rai shine kushe mata Aikinta ko nuna wasa a duk wani abu da ya shafi Aikinta . Ita ɗin kwarariyace kuma gogaggiya akan duk wani abu da ya safi surgery,ba kasar ta ba hatta a wasu kasashen tana zuwa aiki. Bangaren soyayya fa? Bata dauki soyayya a bakin komai ba tunda dukkan Aurenta guda ɗaya ne tayi na soyayya kuma shima bai karbe ta ba wanda hakan yasa ta yanke shawarar saka soyayya a ƙwandan shara duk da kuwa tayin da ake kawo mata ,ta gama yanke imani da soyayya akan duk wani ɗa namiji wanda haka yasa mutane da dama ke mata kazafi da mata take so duba da ƙin mazanta karara a fili. Amma menene dalilin tsanar tasu da tayi? Menene yasa ta cire mazan daga tunaninta da zuciyarta baki daya? Shin zata faɗa soyayyar wani ɗa namiji ko a'a? Idan zata faɗa wanenen wannan mai sa'ar?. DR IMAM MUKTAR PAKI, Saurayi dan kimanin shekaru Ishirin da tara ,bai taba Aure ba, Dalibi wanda yake neman sake gogewa akan Aikin surgery ,shekara ɗaya wadda kareta ne kaɗai zai bashi kwali da kuma lasisin Fara yin surgery ,kaddara itace tayi aikinta ta ɗauko sa kan kachakar ta kawosa CITY TEACHING HOSPITAL inda yake ƙarkashin jagorancin likitar da kowa ke tsoro da shakka, Mene zai faru idan shi bai ji wannan feelings ɗin ba sai wani daban wanda shi kansa bazaya iya fassarawa ba? Shin ya wannan kaɗdarar tasu zata kasance? Shin Wanne irin chakwakiya Imam ke shirin ɗaukowa kansa domin wannan likitar da ya ke kan giyar so AURENTA UKU ,Ƴaƴanta uku a yayin da shi ko na fari bai taba yi ba. Ku biyo ɗiya jamilu domin jin yarda wannan labarin na IMAM da UMAIMAH zai kasance !

More details
WpActionLinkContent Guidelines