MATAR SHEIKH

MATAR SHEIKH

  • WpView
    Reads 78,909
  • WpVote
    Votes 3,502
  • WpPart
    Parts 12
WpMetadataReadComplete Tue, May 7, 2024
"Nasan I zuwa yanzu kowa na unguwarku yasan wacece ke, yar maye, yar shaye shaye? Duk wanda suka zaba yayi. Nasan iyayenki ma yau zasu kore ki saboda sun gano ko ke wacece. Shi kuma Sheikh din da kika same shi a tafin hannunki, bayan ko wacce salihar mace da ma mara tarbiyyar neman soyayyar sa take ruwa a jallo. A yau dai ina da tabbas din ya sullube daga hannunki. Domin kuwa idan yazo bincike, zai tarar ashe miskilar yarinyar, yar maye ce. Ki huta lafiya. Ops na manta ban gabatar miki da kaina ba. Haha. Nice wadda zata riqe tambarin MATAR SHEIKH ko kin so ko baki so ba." #1 in soyayya on 8th may 2022.
All Rights Reserved
#6
wife
WpChevronRight
Join the largest storytelling communityGet personalized story recommendations, save your favourites to your library, and comment and vote to grow your community.
Illustration

You may also like

  • BA GIRIN-GIRIN BA
  • TAMBARIN SHAHARA....🌹
  • NAYI DACE✔️
  • SO KO W@H@L@L@H ?
  • NOORUN NISA
  • GOBE NA (My Future)
  • ᎠᎪႮᏞᎪᎻ.. 𝘉𝘐𝘠𝘜!!!   dynasty's
  • SULTANA...
  • HASKEN RANA✔️
  • ƳAR BAƘA

BAN YARDA A YI COPYING DAGA NAN ZUWA KO INA BA, YIN HAKAN SHIGA HAKKIN MALLAKA NE ANA IYA MANA HISABI AKAN HAKAN Burin dukkan iyaye shi ne su aurar da ya'yansu da sun taka munzalin aure musamman ya'ya mata. Hakan ya kasance daga cikin Addini da Al'adunmu. Rashin aure kan haifar da damuwa a zukatan iyaye da su kan su ya'yan amma kamar yanda addini ya koyar da mu cewa "Komai da lokacin sa" shi ma auren ya shiga sahun "komai" ɗin. Gaggawa da kwallafa ran akan sai anyi aure ya sa da yawa daga cikin jinsinmu yin KUSKUREN da har su mutu suna nadamar sa. Jinkiri kan sa mutane su rasa tauhidinsu na duk abin da zai faru a doron kasa ya kan faru ne a bisa ga ikon Allah, in bai so ba hakan ba zai faru ba, kuma komai rubutacce ne, kuma alkaluma sun bushe. Sai su zama su na takurawa wanda aurensu ya zo da jinkiri da kalaman "Yaushe za ki yi aure?" ko kuma "Kin ki aure ko" abin tambaya ga duk wanda ya ke ɗaukan aure a wani hanyar nuna Darajan mutum shi ne "mai ya hana musu mutuwa" don kuwa aure, haihuwa da mutuwa lokutansu rantsattse ne. Babu abin takaici kamar a ce mace don ba ta yi aure ba, sai ma su kiran ta ki aure su zagayo suna neman ta da lalata don a ganinsu tun da ta ki aure toh mazinaciya ce. Wacce gaggawa ya dibe ta sai ta ba da kai bori ya hau don a tunanin ta hakan zai sa su aureta. Wasu daga cikin kawayensu kuma kan ɗauki rashin aure dalilin yanke zumunci da su, saboda a ganinsu babu kaskanci kamar rashin aure ko da kuwa auren da za'a rike zai kai su ga wuta ne ba Aljannar da kowa ke yin aure don nemansa ba. Tsabagen son aure ya sa tun yarinya na kwailar ta ake dasa mata ra'ayin duk abin da za ta yi don farin cikin wani ɗa namiji ne ba wai don kanta ko farin cikin mahallicinta ba. Sai ka ga don yarinya ta ci kwalliya ba za'a nuna mata tayi kyau don ta ji daɗi ba sai dai a nuna mata tayi kyau za ta burge wani ɗa namiji. A haka za ta taso in ba'a taki sa'a ba sai ta kai ga siyar da mutuncin ta duk don ta birge namiji.

More details
WpActionLinkContent Guidelines