Najma da Mahir

Najma da Mahir

  • WpView
    Reads 10,320
  • WpVote
    Votes 600
  • WpPart
    Parts 18
WpMetadataReadOngoing2h 5m
WpMetadataNoticeLast published Fri, Nov 5, 2021
"Ga wannan sunanshi 'Dan aike' domin ko in ya je dawowa ya ke, an hadashi ne da majinar damisa mai mura,jelar'beran da bai taba satar daddawa ba,da kuma hakorin muzuru mai kimanin kwana cassa'in, ya yarda ke tun bai san miye yarda ba,a coffee za ki 'diga, 'digo biyu ina jaddadawa!!!, ki bawa Anisa ita zata hada ta kai masa, ba so ba ko zuciyarshi ce a jikanta ba zai aure ta ba, Anisa zai aura,amma duk ranar da Najma ta furta mai da kanta tana son shi ki Kuka da kanki don babu Ruwan Boka Mugu" Ya fada yana zare idonshi da ya sha farin kwalli. *** Gishiri ya ji a bakinshi mai hade da ruwa, lokacin ne ya gane ba ita take bu'katar handkerchief din da ya bata ba shi ke bukata, yaushe rabon da ya yi kuka? Tun ranar da ta yi wani ciwon ciki mai cike da azaba, ya bawa kanshi amsa yana goge majinar da ta samu damar zubo masa, zuciyar sa ce ta kuma tarwatsewa a karo na ba adadi jin kalaman da ke fitowa daga bakinta dukda cewa a wurinshi sun fi kama da aman wuta mai zafi, so yake ya ce mata 'I love you ' kalmomin da tun bata fahimtar magana yake fada mata saidai yau ya kasa,wani abu mai kama da Zuma rock ya danne masa harshensa da zuciyarshi kuma sai bitarsu yake kamar almajiri ya rike allonsa. Dumm zuciyarshi ta buga a karo na uku tun bayan da ta fara magana,bakin shi ya bude wanda ya yi sanadiyyar zubowar yawun da bai san da shi ba a yayinda ya cigaba da kallonta kamar wanda ya ga Tinkiya da'Ture ka ga tsiya' daurin yan mata masu ji da kansu. *** "Haba Yayana 'dan baki!Ya kake so in yi da rayuwata ne?Na san ba Anisa kake so ba ni kake so ba sai ka fada min ba wallahi na sani, amma ka ki ka nemi aurena tun tuni? Mai kake jira? Hmmm, Ya Mir me ya sa ka canza min gaba daya? na yi ta kokarin in jure na kasa saboda zuciyata ba zata iya ba,Nisanta kanka da kake yi da ni 'kara tarwatsa min zuciya yake, Ka yi sake har Abbu ya hada aurena da Ya Jamil,gobe za a daura tunda haka ka zaba you have 24 freaking hours to decide, abinda na sani shi ne I LOVE YOU WALLAHI DA GASKE..."
All Rights Reserved
#7
kishi
WpChevronRight
Join the largest storytelling communityGet personalized story recommendations, save your favourites to your library, and comment and vote to grow your community.
Illustration

You may also like

  • KUSKURE
  • NANA AMINATU 2022
  • Kupu-Kupu Jangan Pergi [18+ End]
  • BAHAGON TUNANI
  • BAKAR WASIKA
  • GADAR ZARE
  • KAUTHAR!!
  • RAYUWAR BADIYYA ✅
  • FERGANDE ND'EMGAL (Tuntuben harshe)
  • HAIRAN🔥💥♥️
KUSKURE

Hannu na karkarwa yake, jiki na har bari yake, saboda tun da nake Rai na Bai taba baci ba kamar yau, ban taba tunanin Baba zai iya abin da yayi yau ba, na saka hannu na na toshe kunne na saboda na daina Jin muryar shi, Amma tamkar a gaba na yake ihun, tamkar ni din yake yiwa masifa "...Saboda ke Baki da mutunci, ke ba yar mutunci bace ba, har ni zance kiyi Abu ki kiyi, to se de ki bar min gida na yau dinnan, ki fito ki hada kayan ki ki bar min gida na, ni ba shashan namiji bane ba..." He kept on saying, ya cigaba da fada Yana yarfa zagi, na zata zagi na Yan kauye ne, na zata ana yin zagi ne ga mutanen da ba su da ilimi, se gashi Baba ne yake zagin Mama a tsakar gida, a gaban mu, gaban kishiyar ta, gaban almajirai, masu aiki yake mata wannan cin mutuncin, nasan ya taba, ba sau daya ba, ba sau biyu ba Amma Bai taba cin mata mutunci irin na yau ba, a gani na ko Babu komai ya kamata taci albarkacin mu, ya kamata ya daga mata kafa saboda mu, se naji zuciya ta tana zafi, tana zugi na kasa hakuri na fito daga dakin, Kai a lokacin ma it's as though I'm possessed saboda wallahi kwakwalwa ta bata tare da ni, zuciya ta ce kawai ke fada min kada na bari, kada nayi shiru cin mutuncin yayi yawa, na kuwa fito tsakar gidan, gidan yayi tsit saboda Baba ya gama ya wuce dakin shi, se almajiran mu biyu suna yiwa Amarya shanyar labule da suka wanke mata, na wuce su na nufi dakin shi fuska ta tayi Wani irin ja, hatta wata vein da nake da ita a goshi na ta fito, tabbacin Rai na ya baci, Yana zaune na same shi a parlon shi, na kalle shi saboda ko sallama banyi ba shi ma ya kalle ni nace "Baba! Me yasa zaka dinga cin zarafin Maman mu a gaban mu, a gaban kowa a gidannan, me tayi maka?" Se ya dago ya kalle ni, I can see the amazement in his eyes, saboda yayi mamaki, baiyi tunanin bakar zuciya ta har ta Kai haka ba... Inaaya

More details
WpActionLinkContent Guidelines