Story cover for KISHIN MATA by Hafnancy01
KISHIN MATA
  • WpView
    Reads 3,007
  • WpVote
    Votes 28
  • WpPart
    Parts 16
  • WpHistory
    Time 3h 21m
  • WpView
    Reads 3,007
  • WpVote
    Votes 28
  • WpPart
    Parts 16
  • WpHistory
    Time 3h 21m
Ongoing, First published Dec 25, 2019
"Don girman Allah Suleiman karka sakeni,ka tuna fa igiya ɗaya ce ta saura atsakanina dakai,ka tausayamun karka maidani bazawaran ƙarfi da yaji..." afusace yace"baki son ah sakeki shine kike kunsa mun baƙin ciki akodayaushe...?yanzu menene dalilin shigowa dakin ƴar'uwarki ah irin wannan lokacin bayan na tabbata kin kwana da sanin cewa mijinta yana ciki...?har uwar ɗaka fa kika biyomu Hafsa...?kuma har kike neman illatamu akan baƙin kishinki...."Haɗiye miyan takaici yayi yana jin yadda zuciyarsa ke masa radaɗi,itama ɗin afusace ta miƙe tana fadin"so kake in ƙyaleku kuci amanata don bani da wayau...? yau fa ake cike kwanaki ashirin da uku da aurenmu amma sbd baƙin halinku na maza wai ace Suleiman har ka yo man kishiya? Jamilar ce wawiya data zauna take kallonka har ka mata kishiyoyi biyu, toka sani ni bazanyi shiru in tsaya kallonka kana aikata abunda kaga dama da wannan kucakar yarinyar bayan ni anawa daran farkon ma ko hannuna baka taɓa ba, shin baka ma ji kunya ba da kake kokarin haɗa shimfiɗa da ƴar cikinka...?"sauran taran numfashinta yayi yace azuciye"menene abun kunya aciki ina ce dai matata ce wacce dubban jama"u suka shaida daurin auranmu...?fine yanzu na gano dalilin shigowarki har cikin ɗaka,so kike kiga yadda zan raya sunnar ma"aiki da matata,shikenan Hafsa yau zan baki mamaki,zan nuna miki cewa bake kadai ce kika iya fitsara da rashin kunya ba akwai shugabanki anan, Zan................."
All Rights Reserved
Sign up to add KISHIN MATA to your library and receive updates
or
#1ummah
Content Guidelines
You may also like
GADAR ZARE by HauwaAUsmanjiddarh
80 parts Complete Mature
A firgice ya mik'e daga inda yake zaune, yana kallon sauran abokanan nasa fuska cike da hawaye idonsa yayi ja sosai Buga kansa ya fara yi ajikin bango yana ihu yana cewa " sun kashe min kowa bani da kowa yanzu, zaman dirshan yayi a k'asa, yana ihu yana yarfa hannunsa, zumbur ya mik'e ya nufi fridge ya d'auko robar ruwa ya bulbulawa kansa "Akan ido na suka k'one gidan mu, mahaifiya ta, mahaifi na, k'anne na duk suka mutu akan kunne na ina jiyo ihun su *************** "Cikin waye wannan a jikin ki? uban waye yayi miki ciki? bazaki fad'a ba saina kashe ki, wayyo na shiga uku duk irin tarbiyyar dana baki abinda zaki saka man dashi kenan, cikin kuka tace " wallahi Aunty ban sani ba, idan za'a kashe ni ban san wanda yayi min cikin nan ba, nima ganin shi kawai nayi ajiki na, tafiya tayi ta bud'e durowa ta d'auko Qur'an ta d'ora akan ta tace " na rantse da wanda raina ke hannunsa bansan wanda yayi min ciki nan ba. Kanta tayo gadan-gadan tana nizaki rainawa hankali, ta shak'e ta idonta suka kakkafe ************** A cikin gidan yarin yake ihu yana kuka yace " sunci Amana ta, sunyi min butulci, na yarda dasu amma sun ci min amana sun had'a min GADAR ZARE Amintattu nane suka yi silar zuwa na gidan yarin, sun raba ni da kowa nawa sun raba ni farin cikina,cikin matsanancin kuka yace " wallahi koda zan rasa komai na rayuwata bazan kyale su ba. Sun mun sharri, sun had'a man makirci da GADAR ZARE ************* "Koken a cikin kayana kuma, kafin ya k'ara sa maganar dubbun police sun kewaye shi da bindugogi, Ana cikin haka wayarsa ta fara ringing, dakyar ya samu ikon d'agawa, ji yayi muryarsa ta tintsere da dariya yace " nine, d'an uwanka, kaga yadda nayi wasa da hankalinka ko, na nuna maka halin 'yan Adam Cikin rawar murya yace " mai yasa kaci amanata? " saboda ina santa, ita rayuwa tace kuma mallakina , Wani irin mahaucin ihu ya saki tare da buga wayar da k'asa .
HAIRAN🔥💥♥️ by Shatuuu095
23 parts Complete
Tunda Anty ta fara magana, Prof yake kallon ta, idan ka kalle shi ba zaka taba fahimtar a yanayin da yake ciki ba, ba zaka fahimci emotions din shi ba, Amma yadda yake kallon Anty, da yadda ya bata dukkan hankalin shi, Abu ne da zai tabbatar maka cewar maganar babba ce. Anty ta gama bayanin ta tsaf sannan tayi shiru tana jiran ganin hukuncin da Prof zai yanke. Cikin nutsuwa yace " A Ina ta samu?" Shi ne tambayar da yayi ma Anty, maimakon tayi masa bayani se cewa tayi " Ai na Gama nawa professor, abin da ya rage kaji ta bakin HAIRAN kawai!" "Me yasa Anty?" Cike da nutsuwa tace " Saboda zaka ga kamar kare ta nake, Amma idan tayi maka bayani Ina Jin zaka fi gamsuwa da kyau!" Daga haka Prof yayi shiru Yana son ya auna nauyin Abubuwan da Anty ta fada Masa, se kawai ya Mike yayi ma Anty sallama ya fita. Kunsan yadda tsumma yake idan aka tsoma shi cikin ruwa ko? To haka Prof yayi, gaba daya jikin shi ya saki, yayi shiru tamkar wani kurma, ya bude mota ya shiga ya kifa Kan shi akan steerer wheel, shi yasa take fada Masa lallai lallai se sun rabu kenan? To Ina ta samu shi ne tambayar da take zuwa Masa... *** Shigowa ta kenan daga lecture, na gaji, gajiya kuwa matuka saboda shirin exams da muke, har lokacin bana cikin dadin rai, Abu ya kusa wata daya Amma still nukurkusa ta yake Yi. Ina Zama Saman gado Ina kallon Nuriyya da ta dakko wani gari tana kokarin kwaba shi da ruwa nace " Me zakiyi?" Tace "Kunun aya Mana!" Se nace " Kunun Aya Kuma, gaskiya Kin iya bawa Kai wahalar, ana shirin exams din!" Tayi dariya tare da daga min wata transparent ziplock tace " Waye zai Baki wani wahala, wannan ai is outdated, halan Baki San Islah foods ba ko? To ita take siyarda wannan garin na kunun Aya, yours is just to make little effort se ki Sha!" Nayi murmushi Amma kafin nayi magana se Naga Kiran Anty na shigowa cikin waya ta, da sauri nayi excusing Kai na sannan na mike Dan fita
KUSKURE by Shatuuu095
15 parts Complete
Hannu na karkarwa yake, jiki na har bari yake, saboda tun da nake Rai na Bai taba baci ba kamar yau, ban taba tunanin Baba zai iya abin da yayi yau ba, na saka hannu na na toshe kunne na saboda na daina Jin muryar shi, Amma tamkar a gaba na yake ihun, tamkar ni din yake yiwa masifa "...Saboda ke Baki da mutunci, ke ba yar mutunci bace ba, har ni zance kiyi Abu ki kiyi, to se de ki bar min gida na yau dinnan, ki fito ki hada kayan ki ki bar min gida na, ni ba shashan namiji bane ba..." He kept on saying, ya cigaba da fada Yana yarfa zagi, na zata zagi na Yan kauye ne, na zata ana yin zagi ne ga mutanen da ba su da ilimi, se gashi Baba ne yake zagin Mama a tsakar gida, a gaban mu, gaban kishiyar ta, gaban almajirai, masu aiki yake mata wannan cin mutuncin, nasan ya taba, ba sau daya ba, ba sau biyu ba Amma Bai taba cin mata mutunci irin na yau ba, a gani na ko Babu komai ya kamata taci albarkacin mu, ya kamata ya daga mata kafa saboda mu, se naji zuciya ta tana zafi, tana zugi na kasa hakuri na fito daga dakin, Kai a lokacin ma it's as though I'm possessed saboda wallahi kwakwalwa ta bata tare da ni, zuciya ta ce kawai ke fada min kada na bari, kada nayi shiru cin mutuncin yayi yawa, na kuwa fito tsakar gidan, gidan yayi tsit saboda Baba ya gama ya wuce dakin shi, se almajiran mu biyu suna yiwa Amarya shanyar labule da suka wanke mata, na wuce su na nufi dakin shi fuska ta tayi Wani irin ja, hatta wata vein da nake da ita a goshi na ta fito, tabbacin Rai na ya baci, Yana zaune na same shi a parlon shi, na kalle shi saboda ko sallama banyi ba shi ma ya kalle ni nace "Baba! Me yasa zaka dinga cin zarafin Maman mu a gaban mu, a gaban kowa a gidannan, me tayi maka?" Se ya dago ya kalle ni, I can see the amazement in his eyes, saboda yayi mamaki, baiyi tunanin bakar zuciya ta har ta Kai haka ba... Inaaya
🌸RAYUWAR MU A YAU🌸 by faizamurai
40 parts Complete Mature
Bai furta mata komai ba kawai ya ɗago wuyan ta da wani irin ƙarfi ya kafa mata a baki bata Musa ba kuwa ta haɗiye ta duk wadda ya juye mata a baki saboda tana da ɗan yawa har tana ɗan zuba a gefen bakin ta. Wadda ta zuba a gefen bakin na ta ya fara lashe wa kamar wani maye kafin a hankali ya zare rigar jikin ta ya fara tuttula mata madarar. A hankali yake bin jikin na ta da ya tsiyaya madarar yana lashewa tare da wadda ke ƙoƙarin sauka a jikin ta kamar wani tsohon maye.Nadiya kuwa an samu abun da ake so sai ƙara gantsarewa take yi tana sakin ƙananan nishi bai daina ba sai da ya suɗe ta tass sannan ya koma kan lips ɗin ta suma Nadiya kuwa take ta fara mayar masa dan haka kawai ta samu kanta da kasa mayar masa kamar yadda suka saba tun kafin Auren su da kuma kasa aiwatar da komai kamar yadda ta sanar wa da ƙawayen su da shawarar da suka bata da ɗaura ta akan mugun saiti.Wani irin zut zut take ji a jikin ta wanda lokaci ɗaya wata irin buƙata ta taso mata maganin da ya saka mata a madarar ya fara ta siri.Jin sabon salon da ya ɗauka hakan ya sa ta kasa haƙuri ta fara sakin wani irin Shegen kuka mai tayar da tarzoma.Ai ko kamar ta ƙara ma Tanim ƙaimi.Jin jikin ta ya fara saki hakan ya sa babu Addu,a babu komai ya afka mata kamar wani Akuya haka yake mu,amalantar ta Nadiya kuwa ta kasa kuka duk da azabar dake ratsa ta sai dai maganin yana son ya rinjaye ta Dan ma tana da karfin Jini ne. A wannan dare ne Tanim ya cika burin sa ya kore ƙishin sa akan Nadiya,ƙishin da ya daɗe yana Dannewa ƙishin da ya lulluɓe da sunan soyayya,ya tsinci kanshi cikin farin ciki domin kusan zaucewa yayi zagayen da yayi akan ta kuwa ya kusan bakwai kasancewar ya sha maganin da yafi ƙarfin jinin sa shima.Dukkanin su sun jigata sai dai hakan bai hana komai ba saboda
FATU A BIRNI (Complete) by suwaibamuhammad36
18 parts Complete
"I promise you Mami, zan nemo miki ƴar'uwarki a duk inda take a faɗin ƙasar nan. SULTAN promises you that." Sultan ya shiga ya fita, har ya aikata abunda ba'a tsammani domin ya cika wannan alƙawari da ya ɗaukawar mahaifiyarshi, aka yi dace ya gano inda take. Wani abun takaici shine a maimakon ya samu ƴar'uwar Maminshi kamar yanda ya ci buri, sai ya haɗu da ƴarta kwalli ɗaya tak da ta haifa a duniya ta bari cikin ƙauyanci da kuma rashin wayewa. Baƙin cikinshi bai tsaya a nan ba, domin dattijon da yake riƙe da ita a take ya aura masa yarinyar ba tare da ya iya kaucewa wannan mummunan ƙaddaran ba. Ya tafi ya barta ba tare da ya sake waiwayarta ba, ya kuma tafi da wani kaso na zuciyarta ba tare da ya sani ba. Fatu (Fatima) ta ji haushi, sannan tana cikin baƙin cikin tafiyar da mijinta yayi ya barta. Tun tana tsumayinshi tana fatan ya dawo ya ɗauketa, har zuciyarta ta daskare da tsantsar tsanarshi na wofintar da ita da yayi, da kuma banzatar da igiyar aurensa dake kanta. Tayi alƙawarin ɗaukan fansa, ta kuma yi alƙawarin raba tsakaninsu ko da duniya zasu taru su hanata. Sai ta nemo shi a duk inda yake. Ta shiga cikin Birni nemansa, a nan kuma ƙaddara ya gifta tsakaninsu suka haɗu a lokaci da kuma yanayin da basu yi tsammani ba. Shi kuma ganin kyakkyawar baƙuwar fuska mai ɗauke da kamala, ya sashi faɗawa cikin sonta dumu-dumu ba tare da ya shiryawa hakan ba, kuma ba tare da ya gane cewa Matarsa ce ta Sunnah ba, Halal ɗinsa. Me zai faru idan Fatu ta haɗu da mutumin da ta ƙullata tsawon shekaru a yayin da shi kuma yake jinta a zuciyarsa tamkar ruhinsa? Me kuma zai faru Idan wasu sirrikan suka bayyana a lokacin da ba'a shirya musu ba? Fatu mace ce ɗaya mai hali mabanbanta; Fatu- Matar Sultan. Fatima- Budurwar Sultan.
RAYUWAR BADIYYA ✅  by Aishatuh_M
61 parts Complete
"Tun ina yarinya kike zagin mahaifiyata, tun bansan menene maanar kalmomin wulakanci da muzgunawa ba nakejin kina fadarsu ga mahaifiyata, ina cikin wannan halin wani azzalumi yaje ya kashe min mahaifiya, a gaban idona kika hana a tafi dani inda zanji dadin rayuwata, babu yadda na iya haka na biyoki inda kika doro mani karan tsana, kullum sai kin zage kin dukeni, sunan mahaifiyata kuwa ya zama abun zagi a gareki a koda yaushe, kin hanani abinci, kin sakani wanka da ruwan sanyi lokacinda ake matukar sanyi, kin cuceni iya cutuwa, a haka Allah ya rayani. Sai ke yau dan rana daya kince zakici uwata nace nima zanci taki shine zakiyi kukan munafurci? Ni kin taba laakari da irin kukan danake cikin dare kullun? Dukda mahaifiyata ta rasu hakan bai hanaki zaginta ba. To na fada da babbar murya, wallahi duk kika kara cewa zakici uwata to sai naci taki uwar nima, and that's final!" Zuwa yanzu duk bakin cikin dake zuciyar Badiyya saida ya fito, kuka take kamar ranta zai fita, mahaifiyarta kawai takeda bukata, bakin ciki ya mata yawa, batada wanda zai saka ranta yayi sanyi bayan Momynta, amma tayi mata nisan da yakeda wuyar isa. Ta buda baki zatayi magana kenan Ahmad ya wanke ta da marika kyawawa guda biyu, ta dama da haggu, rike wajen tayi tana kallonshi. Magana ya fara cikin tsananin bacin rai, "Yanzu Badiyya a gabana kike cewa zakici uwarta? Uwata kenan fa Badiyya! To ko Yaya kika zaga bazan kyaleki ba balle wadda ban taba gani ba, dan haka wallahi zakiyi mugun dana sani," ya fada cikeda tsananin fushi, yana kara kai mata mazga saman kai. Kukane ya kara kwace mata "Kai kenan da baka taba ganin taka ba, nifa? Nifa Dady?! Na taba ganinta, nasanta, nasan dadin uwa, amma haka wani azzalumin ya raba ni da ita, sannan kai da nake tunanin zaka share min hawaye kaine kake kara sakani kuka, me na maka? Me Momyna ta maka?" Ta tambaya tana kureshi da idanu. _______ Me zai faru a rayuwar yarinya yar shekara goma data rasa mahaifiyarta? Wace irin rayuwa zatayi a gidan yayar mahaifinta?
NANATOOU (DIYAR KAKA) by AishaMaaruf1
20 parts Ongoing
Labari ne akan wata Yar kauye da aka sangarta ta, Duk kauyen su ta addabi kowa ba mai iya tsawata mata, tun daga yara, matasa, yan mata, tsoffi, hatta da sarkin garin duk ta addabe su........................ wani matshin saurayi da baze wuce shekara sha takwas ba ya ce"ya ana miki magana kin miyar da mutane yan iska". kallan Shi tayi Sama da kasa tana gyara dan kwalin ta sai wani murgude murgude take ta ce"ba yan iska ba karuwai da kwartaye na mai da ku ko kuma ka ce yan goguwa ta fada tana murgude baki tare da hararar shi". Keh ni za kiwa rashin kunya, ganin yanda ya harzuka yasa ta ja da baya tana shirin ko ta kwana, dan ubanki ni zaki zaga, ja da baya ta yi ta tattare zanin ta ta ce" ba dai ubana ba sai dai ubanka mln salisu mai wankin hula". Toh wallahi ubanki zan ci idan na kama ki, sai na karya kasusuwan ki dan duk dangin ku ba sa'a na. Wani wawan birki ta ja har tana kokarin faduwa ta ce"kaiiiiiiii! Amman kai mugun makaryaci ne, tsabar raini da rashin ta ido ni zaka kalla kace min duk dangin mu ba sa'an ka, toh ina ka aje aboki balle kuma yaya mugu ehhhhhh!, ko dai abinda ka ke sha ne ya fara dagula maka lissafi, kun san ku samarin zamanin nan ba a raba ku da aaaa, ta fada tana gwada mishi yanda ake shan taba". Iya kuluwa ya kulu ya dade yana jin irin rashin mutunci da takewa mutane, abin yau yazo kan shi, dutsen dake kusa da shi ya raruma zai Jefe ta da shi tsohon dake tsaye yana kallon su ya ce"kul dan nan kar ka kuskura", bata ko san suna yi ba dan tuni ta yi gaba............................ Mu haɗu da ku a cikin labarin..... Started Fri sep/12/2025 Finish................
SAWUN GIWA...!🐘 by Hafnancy01
18 parts Complete
"Dallah gafara can malama, har ke kin isa ki mana abunda Allah bai mana shi ba? Akanki ne aka Fara irin hakan? Ko kuwa akanki ne za'a daina? Sai wani ciccika bak'in banza kike awurin kamar zaki iya tabuka abun kirki idan har mukayo gaba da gabanta, Ke kin sani sarai ba yabon kai ba ammh wallahi tsab zan tumurmusheki anan wurin kuma in zauna lfy lau agidan Mijina, Kuma ki saurareni dak'yau, halinki ne ya jaza miki wannan cin amanar, Ke kowacce mace tana mafarkin samun miji kamar naki ammh ke Allah ya baki salihin mutum mai tsoron Allah, Sai ke kuma kikai amfani da hakan kina muzguna masa? Bashi da iko da gidansa sai yadda kikai? Babu wata muryar da yake tsoro da shakka face naki? To wallahi ki sani da'ace ayau bani da aure ne to Kinji nace Allah mijinki zan aura, zan shawo kansa kuma dole ya saurareni don kowacce mace da salon nata kissar, balle ma idan yaga ina masa abunda ke baki masa shi, kin san Zuciya nason mai faranta mata, ke mahaukaci kankat kenan yana kaunar mai faranta masa balle mai hankali, Hajiya Sa'a kiyi kuka da kanki ba dani ba don iya allonki ne yaja miki Faruwar hakan." Kuka sosai Hajiya Sa'a ke rerawa don ta kasa Furta komai kuma, Hajiya Aisha ta gama kashe mata jiki, Kama baki Hajiya Aishar tayi tana Fadin"Ai baki ma soma kukan ba, nan gaba kadan zakiyi wanda yafi wannan, kuma ki saurareni dak'yau, ga 'yata nan amana, Ku Zauna lfy ke da ita don wallahi kika sake naji ance ko ciwon kai kin sakata Allah saina lahira ya fiki jindadi, don kwarai zan cire kunyar Surukuta da amintar dake tsakaninmu musa wando kafa daya dani dake, Sabida haka ki kiyaye sannan Kuma akyalesu su sha amarcinsu Cikin kwanciyar hankali, don wallahi Hajiya Sa'a tashin hankalinsu kema tashin hankalinki, Tun wuri ki iya takunki don karki ce ban fada miki ba, Suhaila ita kadai ce 'yar da Allah ya bani sabida haka zan iya yin komai akanta, Ki huta lfy."
NANA AMINATU 2022 by UmmuDahirah
56 parts Complete Mature
Maganganun ta tamkar saukar kibiya take jin su a zuciyarta duk idan ta tuna, suna sukan ta su hana ta sukuni, suna tarwatsa ta su saka ta taji ita ƙasƙantanciya ce wacce bata kai ɗin ba kamar yadda take cewa, tana ganin baƙin kanta a koda yaushe a wacce bata kai ba, ko kaɗan bata taɓa saurara mata ba, ya za'a yi ta dena kallon kanta ta daban a cikin mutane yayinda take tuna duk wata kalma ta ɓatanci da take bin ta dasu a kullum ranan duniya? tun sanda ta buɗe idanuwanta da wayon ta take jin waɗannan munanan kalaman da ke tarwatsa mata duk wani farin ciki da jin daɗin ta. Sai dai kuma a duk sanda take jiyo kalaman sa sai ta ji ƙwarin gwiwa har ta kalli kanta a wacce ta kai kuma ta isa, ashe akwai ranan da zata yi farin ciki haka? Akwai ranan da wani zai iya yabon ta har ya nuna mata tana da matsayi fiye da sauran Mata? She can't believe that... Shi ne Mutum na farko da yake faɗa mata kalaman da idan ta ji su take ganin ta kai Mace, ta kai Mace cikakkiya ba wacce ta rako Mata ba, a kullum ganin kanta take yi a bata kai matsayin ba, ita bata kai Macen da zata iya fitowa ayi gwagwarmaya da ita a matsayin ta na ɗiya Mace ba. Shin wane ne shi wannan ɗin? Tabbas Ƙaddara kowa da irin tasa, wasu tana zuwar musu da sauƙi wasu kuwa akasin hakan, ba wai don wani ya fi wani bane a wurin Allah hakan ke faruwa, a'a, sai dai don Allah na gwada ko wanne bawa ta hanyar ɗaura masa tashi ƙaddaran, walau me sauƙi ko akasin sa, ko wanne bawa da tashi ƙaddaran kuma kowa yana fatan ace ya tsallake ƙaddaran da Allah ya ɗaura masa. Haka itama NAANA AMINATU tayi fafutuka a cikin rayuwar ta domin ta ga ta cinye nata ƙaddaran da ta kasance babba a gare ta. Na san Kuna so ku bibiyi labarin ta domin ku ji mene ne ya faru a rayuwar ta, to ku bi Ni sannu a hankali Zan warware muku komi a cikin sauƙi, ina fata labarin zai zame muku darasi a cikin rayuwa.
RUHI BIYI (a gangar jiki daya) by Abdul10k
24 parts Complete
Hakan ya furta cikin kasar zuci,amma ko cikin karfi irin ta tsatsuba Nainah ta saurari komi....... Gajeriyar murmushi tayi,daga karshe ta hade fuska......nanfa ta soma tunano abinda ya faru a wancen lokacin.....da kuma abinda yayi sanadin sumewar Harun. A yayin da Harun ke Yunkurin taba kafadar wannan halittar data diro masa a gaba..... sai bakaken aljanun nan suka sake bayyana inda suka aika sakon tsafi....wacce tayi sama da Harun din ta kuma bugasa da kasa..... Cikin kankanin lokaci ya sume....Nainah da ganin haka ta hade rai hade da cewa.... "Kai kananun masharranta mai kuke takama dashi da har zaku sumar da wanda nake karewa...."?? *Karku shige rudani _readers_ dan wannan wanda ta diro gaban harun ba kowa bace illa Nainah....* Dajiyo batun nata ko daya daga cikin bakaken aljanun ya koma bayan babban nasu yace dashi...... "Yaya Gafur.....ninasan hatsarin wannan Yarinyan.... Itace fa wannan gimbiya danake baka labarin wato Nainah.........ita tayi sanadiyar mutuwar Gwarzon mayakan Bakaken aljanun na saman tsauni...." Dajiyo hakan ko Gafur ya fashe da muguwar dariya hade kuma da kyakyatawa....cikin murya uku uku Sannan yace da dan uwan nasa........ "ba gimbiya take ba...ko itace sarauniyar aljanun duniya,tunda dai ta shigo gonata saina koya mata hankali" Haka kannen nasa sukayi ta kokarin tsayar dashi amma yaki sauraron su... Dukda ma kannen nasa akayima abin amma hakan ta matukar hassala shi... Nainah ko....motsawa batayi ba,ta wani bushe kim guri guda... Nanfa gafur ya umurci kannen nasa da su basa guri.... Sannan yaja layi ya soma aika sakon tsafi iri iri...
AURE UKU(completed) by Chuchujay
32 parts Complete
DR UMAIMAH USMAN BULAMA,Mace yar kimanin shekara ishirin da tara , Babbar surgeon A asibitin CITY TEACHING HOSPITAL , Aure Uku, ƴaƴanta uku . Mace mara san hayaniya wadda tasan kan Aikinta ,babu abunda tasa a gabanta illa bawa Aikinta babban muhimmanci kana yaranta wadda kaɗdarar samunsu ta rarraba mata Aure . Kalma ɗaya zaka faɗa ta bata mata rai shine kushe mata Aikinta ko nuna wasa a duk wani abu da ya shafi Aikinta . Ita ɗin kwarariyace kuma gogaggiya akan duk wani abu da ya safi surgery,ba kasar ta ba hatta a wasu kasashen tana zuwa aiki. Bangaren soyayya fa? Bata dauki soyayya a bakin komai ba tunda dukkan Aurenta guda ɗaya ne tayi na soyayya kuma shima bai karbe ta ba wanda hakan yasa ta yanke shawarar saka soyayya a ƙwandan shara duk da kuwa tayin da ake kawo mata ,ta gama yanke imani da soyayya akan duk wani ɗa namiji wanda haka yasa mutane da dama ke mata kazafi da mata take so duba da ƙin mazanta karara a fili. Amma menene dalilin tsanar tasu da tayi? Menene yasa ta cire mazan daga tunaninta da zuciyarta baki daya? Shin zata faɗa soyayyar wani ɗa namiji ko a'a? Idan zata faɗa wanenen wannan mai sa'ar?. DR IMAM MUKTAR PAKI, Saurayi dan kimanin shekaru Ishirin da tara ,bai taba Aure ba, Dalibi wanda yake neman sake gogewa akan Aikin surgery ,shekara ɗaya wadda kareta ne kaɗai zai bashi kwali da kuma lasisin Fara yin surgery ,kaddara itace tayi aikinta ta ɗauko sa kan kachakar ta kawosa CITY TEACHING HOSPITAL inda yake ƙarkashin jagorancin likitar da kowa ke tsoro da shakka, Mene zai faru idan shi bai ji wannan feelings ɗin ba sai wani daban wanda shi kansa bazaya iya fassarawa ba? Shin ya wannan kaɗdarar tasu zata kasance? Shin Wanne irin chakwakiya Imam ke shirin ɗaukowa kansa domin wannan likitar da ya ke kan giyar so AURENTA UKU ,Ƴaƴanta uku a yayin da shi ko na fari bai taba yi ba. Ku biyo ɗiya jamilu domin jin yarda wannan labarin na IMAM da UMAIMAH zai kasance !
You may also like
Slide 1 of 20
MENENE MATSAYINA... cover
BAHAGON TUNANI  cover
GADAR ZARE cover
HAIRAN🔥💥♥️ cover
KUSKURE cover
🌸RAYUWAR MU A YAU🌸 cover
SIRRIN MU cover
FATU A BIRNI (Complete) cover
💤A MAFARKI NASANTA💤( I know her in my dream ) cover
RAYUWAR BADIYYA ✅  cover
NANATOOU (DIYAR KAKA) cover
KWANTAN ƁAUNA cover
SAWUN GIWA...!🐘 cover
NANA AMINATU 2022 cover
RUHI BIYI (a gangar jiki daya) cover
AURE UKU(completed) cover
MAI ƊAKI...! cover
NADIYA! cover
KOWA YA GA ZABUWA... cover
𝐔𝐒𝐓𝐀𝐙 𝐃𝐀𝐘𝐘𝐀𝐍 𝐙𝐈𝐐𝐑𝐈  cover

MENENE MATSAYINA...

51 parts Complete

"Don ubanki wanki dana barmiki kimin shine kika kiyimin Kika zauna kika rungume wannan shegiyar d'iyar taki wallahi koki aje ta ko kuma yanzu jikin ki ya gayamiki nafada miki banza..." Fuskar jike da hawaye ta d'ago ta kalleshi cikin kyarmar murya tafara Magana Haba! Noor...marin dataji a fuskar ta ne yasa bata Ida fadar Abinda ke bakin ta ''shegiya tun yaushe na haneki da furta wannan sunan gareni wallahi duk ranan danaji kin kara Ambata ta da wannan sunan na lahira sai yafi jikin dadi jaka kawai ball..yayi da ita daga ita har d'iyar dake hannun ta goshin ta ya bugu da bango d'iyar dake hannunn ta tsayanra kuka tare da Ambatar Umme... ''Kafin nadawo gidanan ki tabbatar da kimin wanki sannan kingyara min dakina nafada Miki.."" Juyawa yafita yabarta rushewa tayi dawani matsanancin kuka mai tattare da tausayi hannu taji da fuskar ana share mata hawaye "Ummee kidaina kuka kitaci mutafi gun Umman ki ko Uncle Abdul..." Rungume ta tayi.."zamuje Basmah Amma inaje gunsu *MENENE MATSAYINA..?* "............ _Menene matsayina? Labari mai cike da tausayi fadakarwa.. butuulci #Soyaya #Shakuwa #Tausayi #