BA UWATA BACE

BA UWATA BACE

  • WpView
    Reads 69,380
  • WpVote
    Votes 5,267
  • WpPart
    Parts 47
WpMetadataReadOngoing5h 6m
WpMetadataNoticeLast published Mon, Apr 20, 2020
WpInfo
Fiction
Action and Thriller
BA UWA TA BACE Zaune take gefe guda cikin gidan nasu, tana kallon abinda Yan gidan nasu sukeyi k'awar tace Hadiza zaune gaban mamar tasu tana mata lissafin kud'i da tasamu, daga daren jiya zuwa yau da safe. Mamar sai washe hak'ora take tana murna sannan tace "Ai na fad'a Miki idan Kika bi Alhaji Hamza kwanan gida sai ya Baki mamaki." Hadiza tace gashi kuwa ya bani mamaki mama domin tunda Nike arayuwata bantab'a kama irin kud'in Dana kama yau gugu na gugur naira har dubu hamsin mama tawani wutsilo daga kugerar da take Yar tsugunne, ta fad'o k'asa sannan ta d'aga Kai ta dubi Hadiza ko zafin fad'uwar bataji ba tace da gaske kike ko da Wasa Yar nan. Hadiza tace "wallahi mama kingansu ma" ta fito dasu ta nuna mata kud'in hannu na rawa mama ta k'arbesu ta tashi tana juyi da rawa agaban d'iyar Tata. Bilkisu ji tayi k'amar ta kurma ihu Dan bak'in ciki wannan wata irin uwa ce Allah ya Basu, wasu hawaye masu zafi ya zubo mata ganin yadda ita Tata rayuwar zata Kaya kenan ga wata uwar yunwa datakeji, Amma saboda tak'i bin abinda uwar Tata takeso ta hanata, gashi ita tashin hankalinta shine idan dare yayi wani irin tuggu zasu had'a mata Dan taji mamarta da yayanta na zancen, zuwan Alhaji kamilu zuwa gareta ko tanaso ko bataso yau sai ya kwana da ita, Anya kuwa wannan ita d'in uwa ce agaresu tana cikin wannan tunanin taji k'ara bud'e kyauren gidansu na langa langa daga Kan da zatayi Dan taga Mai shigowa sai taga k'awarta ce ta biyu zainab. Shigowa tayi cikin wata irin shiga domin kayan jikinta amatse suke sosai duka sun fitar da surar jikinta rabin breast d'inta duk awaje cikin takun yauk'i da yanga tashigo, tana yatsina ko sallama babu mamarta ta k'alla sannan tace "wallahi mama yau nagaji Dan wannan d'an iskan Alhajin bak'aramin sasuk'a ta yayi ba tun dare yake abu d'aya har safe gashi bak'arami ba ga abun tashi kamar tabarya, gaskiya ya cika d'an iska
All Rights Reserved
#47
soyayya
WpChevronRight
Join the largest storytelling communityGet personalized story recommendations, save your favourites to your library, and comment and vote to grow your community.
Illustration

You may also like

  • BAHAGON TUNANI
  • GADAR ZARE
  • SAWUN GIWA...!🐘
  • SIRRIN MU
  • WASIYAR AURE😭❤❤complete
  • NANA AMINATU 2022
  • MAI ƊAKI...!
  • KAUTHAR!!
  • KUSKURE
  • NI DA ABOKIN BABA NA

_Ta ya kishiyar da ta shuka sharri ta yi tunanin girbar alkhairi_ _Ta ya kishiyar da ta tarwatsa farincikin abokiyar zamanta ta yi tunanin kwanciyar hankali zai aureta_ _HAFIZA natsattsiyar yarinya, mahaddaciyar Al'qur'ani da ta taso cikin kaɗaicin yayyenta uku da suke hannun kishiyar mahaifiyarsu,tana gana musu azaba sakamakon hatsabibiyar mallakar da ta yi ma Ubansu. Wani gigitaccen al'amari ya tilasta HAFIZA komawa wurin kishiyar mahaifiyarta sakamakon bangon da take kallo a matsayin majigini ya rushe. Kishiyar mahaifiyarta ta ci gaba ta soya musu tsakuwa a hannu yayin da ta keɓe yaranta tana shayar da su ruwan zuma. Sau biyu kishiyar mahaifiyarta na zama silar fasawan auranta ganin za ta fi yaranta jin daɗin gidan miji. Sai dai Ubangiji ya yi ikonsa,domin ta yi dacen miji ɗaya tamkar dubu wanda ya doke na sauran mazajen 'yan'uwanta,ya yi musu fintinkau a komai._ _A tunanin HAFIZA ta yada ƙwallon mangoro ta huta da ƙuda,sai dai bata sani ba tirka-tirkar da ke cin gidan auranta ya linka wanda ta baro a gidansu sau dubu. Bahagon gida ne mai cike da chakwakiya kala-kala masu matuƙar yawa da ban tsoro. Sai dai faɗin hausawa da suka ce WUYA BATA KISA. Silar zuwan HAFIZA gidan ɓoyayyun sirrikan da ke ɓoye sama da shekara ashirin da biyar sun bayyana a idon duniya. Kar na jaku da yawa🥰 ku biyo tsaftataccen alƙalamina don yi muku jagora zuwa duniyoyi biyun da tunaninku bai je ba🥰_

More details
WpActionLinkContent Guidelines