CHAKWAKIYA

CHAKWAKIYA

  • WpView
    Reads 10,737
  • WpVote
    Votes 941
  • WpPart
    Parts 40
WpMetadataReadOngoing6h 35m
WpMetadataNoticeLast published Fri, Jan 15, 2021
Binafa tana zaune a tsaƙar gida daga ita sai wani gajeren wando daya wuce gwiwarta sai wata riga wacca taɗan matseta kaɗan kanta babu ɗan kwali gashin kanta ya sauka har gadan bayanta, tana zaune tana jujjuya abincin ta kasaci, ta lula tunanin duniya, jin anyi sallama yasata ɗago da kanta ta amsa, ganin Safwan yasata zabura murmushi ɗauke a fuskarta ta tashi tazo inda yake da gudu, murmushi shima yayi mata tare da buɗe hannayansa alamun tazo inda yake, tunda ta fara gudun ko ina na jikinta yake motsawa, Ahmad runtse idanunsa yayi, ganin da gasken gaske Safwan rungume Binafa zayyi yasa Ahmad saurin matsar da Safwan gefe Binafa ta kusan faɗuwa, wani kallo ya wurga mata yace "Kije ki saka Hijab"
All Rights Reserved
#2
yaudara
WpChevronRight
Join the largest storytelling communityGet personalized story recommendations, save your favourites to your library, and comment and vote to grow your community.
Illustration

You may also like

  • NADIYA!
  • MIJIN TSOHUWA
  • AL'AJABIN SO
  • KOWA YA GA ZABUWA...
  • WASIYAR AURE😭❤❤complete
  • 🌻🌻MATSALAR GIDAN MIJI🌻🌻(GIDAN AURENA) BOOK 1.
  • KAUTHAR!!
  • Dr Azeema
  • TAFIYAR MU (Completed)
  • 🌸RAYUWAR MU A YAU🌸
  • KAICO NAH
  • MURADIN ZUCIYA
  • KUSKURE
  • MATAR SADAM
  • Kaine Rayuwata😭❤❤ Complete
  • NANATOOU (DIYAR KAKA)
  • KOWA YA DAKA TA BADO...
  • SAWUN GIWA...!🐘
  • SIRRIN MU
NADIYA!

'Ta dan juya kanta cike da mamaki, tace, "Daddynka kuma? wanene shi?" Yace, "Habib Abdullahi Makama?!" cikin sigar tambaya. Jin sunanshi kadai ma sai daya sanya taji bugun zuciyarta ya canza. A duka kwanakin da suka wuce tun bayan daya ajiyeta a kofar gidansu ya wuce, karya take yi tace babu wata rana da zata fito ta koma ga mahaliccinta bata tunano wannan mutumin ba. Abin har ya kusa zame mata jiki, yin tunaninshi a lokacin da taje yin kwanciya barci. Wasu dararen kuwa har da mafarkinshi da tunanin wannan daddadan kamshi nashi, wanda ta lalubo turaren da yake amfani dashi cikin wadanda ya bata, itama ta mayar dashi nata turaren. Yaudarar kanta take, da take cewa wai tuni ta manta da sha'aninshi da kurar data kwasoshi. Ita tasan karya take yiwa kanta. Duk kuma yadda taso abinda ke tukarta a zuciya kada ya bayyana, sai daya bayyana din. Ta rasa fara'ar kirkirowa tayi koda ta yake ce kuwa, haka bugun zuciyarta ya ki saisaituwa duk yadda taso ta saisaita shi kuwa. Ta daure dai da kyar tace, "ok, na ganeshi. Yana ina yanzu?" Ya dan daga kafada, "ban sani ba nima. Kawai dai yace in zauna a wajenki zai dawo ya daukeni." Ita abin ma sai ya girmame mata, mamaki ya hanata motsi. To ita kuma a su wa? Kuma da wane dalili? Da zai dauko danshi ya kai mata?..." To domin sanin dalilin, don me, kuma me yasa? Sai ku biyoni Ni Jeeddah Lawals tare da Nadiya a wannan tafiyar tamu.

More details
WpActionLinkContent Guidelines