Binafa tana zaune a tsaƙar gida daga ita sai wani gajeren wando daya wuce gwiwarta sai wata riga wacca taɗan matseta kaɗan kanta babu ɗan kwali gashin kanta ya sauka har gadan bayanta, tana zaune tana jujjuya abincin ta kasaci, ta lula tunanin duniya, jin anyi sallama yasata ɗago da kanta ta amsa, ganin Safwan yasata zabura murmushi ɗauke a fuskarta ta tashi tazo inda yake da gudu, murmushi shima yayi mata tare da buɗe hannayansa alamun tazo inda yake, tunda ta fara gudun ko ina na jikinta yake motsawa, Ahmad runtse idanunsa yayi, ganin da gasken gaske Safwan rungume Binafa zayyi yasa Ahmad saurin matsar da Safwan gefe Binafa ta kusan faɗuwa, wani kallo ya wurga mata yace "Kije ki saka Hijab"