CHAKWAKIYA

CHAKWAKIYA

  • WpView
    Reads 10,735
  • WpVote
    Votes 941
  • WpPart
    Parts 40
WpMetadataReadOngoing6h 35m
WpMetadataNoticeLast published Fri, Jan 15, 2021
Binafa tana zaune a tsaƙar gida daga ita sai wani gajeren wando daya wuce gwiwarta sai wata riga wacca taɗan matseta kaɗan kanta babu ɗan kwali gashin kanta ya sauka har gadan bayanta, tana zaune tana jujjuya abincin ta kasaci, ta lula tunanin duniya, jin anyi sallama yasata ɗago da kanta ta amsa, ganin Safwan yasata zabura murmushi ɗauke a fuskarta ta tashi tazo inda yake da gudu, murmushi shima yayi mata tare da buɗe hannayansa alamun tazo inda yake, tunda ta fara gudun ko ina na jikinta yake motsawa, Ahmad runtse idanunsa yayi, ganin da gasken gaske Safwan rungume Binafa zayyi yasa Ahmad saurin matsar da Safwan gefe Binafa ta kusan faɗuwa, wani kallo ya wurga mata yace "Kije ki saka Hijab"
All Rights Reserved
#3
yaudara
WpChevronRight
Join the largest storytelling communityGet personalized story recommendations, save your favourites to your library, and comment and vote to grow your community.
Illustration

You may also like

  • SAWUN GIWA...!🐘
  • NADIYA!
  • 🌸RAYUWAR MU A YAU🌸
  • WASIYAR AURE😭❤❤complete
  • KAUTHAR!!
  • KOWA YA DAKA TA BADO...
  • SIRRIN MU
  • KOWA YA GA ZABUWA...
  • Kaine Rayuwata😭❤❤ Complete
  • MURADIN ZUCIYA

"Dallah gafara can malama, har ke kin isa ki mana abunda Allah bai mana shi ba? Akanki ne aka Fara irin hakan? Ko kuwa akanki ne za'a daina? Sai wani ciccika bak'in banza kike awurin kamar zaki iya tabuka abun kirki idan har mukayo gaba da gabanta, Ke kin sani sarai ba yabon kai ba ammh wallahi tsab zan tumurmusheki anan wurin kuma in zauna lfy lau agidan Mijina, Kuma ki saurareni dak'yau, halinki ne ya jaza miki wannan cin amanar, Ke kowacce mace tana mafarkin samun miji kamar naki ammh ke Allah ya baki salihin mutum mai tsoron Allah, Sai ke kuma kikai amfani da hakan kina muzguna masa? Bashi da iko da gidansa sai yadda kikai? Babu wata muryar da yake tsoro da shakka face naki? To wallahi ki sani da'ace ayau bani da aure ne to Kinji nace Allah mijinki zan aura, zan shawo kansa kuma dole ya saurareni don kowacce mace da salon nata kissar, balle ma idan yaga ina masa abunda ke baki masa shi, kin san Zuciya nason mai faranta mata, ke mahaukaci kankat kenan yana kaunar mai faranta masa balle mai hankali, Hajiya Sa'a kiyi kuka da kanki ba dani ba don iya allonki ne yaja miki Faruwar hakan." Kuka sosai Hajiya Sa'a ke rerawa don ta kasa Furta komai kuma, Hajiya Aisha ta gama kashe mata jiki, Kama baki Hajiya Aishar tayi tana Fadin"Ai baki ma soma kukan ba, nan gaba kadan zakiyi wanda yafi wannan, kuma ki saurareni dak'yau, ga 'yata nan amana, Ku Zauna lfy ke da ita don wallahi kika sake naji ance ko ciwon kai kin sakata Allah saina lahira ya fiki jindadi, don kwarai zan cire kunyar Surukuta da amintar dake tsakaninmu musa wando kafa daya dani dake, Sabida haka ki kiyaye sannan Kuma akyalesu su sha amarcinsu Cikin kwanciyar hankali, don wallahi Hajiya Sa'a tashin hankalinsu kema tashin hankalinki, Tun wuri ki iya takunki don karki ce ban fada miki ba, Suhaila ita kadai ce 'yar da Allah ya bani sabida haka zan iya yin komai akanta, Ki huta lfy."

More details
WpActionLinkContent Guidelines