ZULLUMI
  • WpView
    Reads 224
  • WpVote
    Votes 20
  • WpPart
    Parts 11
WpMetadataReadOngoing1h 16m
WpMetadataNoticeLast published Sun, Feb 7, 2021
WpInfo
Fiction
Action and Thriller
Tags00am
Cikin kuka Aisha tace "Rayuwata acikin kwana ɗaya tak ta jirki ce ayayin da ZULLUMI yayimin diran mikiya ZULLUMIN nan shine kullum ke ƙara mamayemin hasken rayuwata duhu na ƙara bayyana " Cikin tausayawa Aqad yace "Ki daina cewa haka Allah na sane da ke mucu gaba da gaya masa sannan da kike cewa haka kinsan ma anar rana ɗaya kuwa? hakan yana nufin muna da sa'oi ashirin da huɗu mintina dubu ɗaya da dari huɗu da arba'in,Allah yariga da yagama tsara komai mu zuba ma sarautar Allah idanu.
All Rights Reserved
#3
00am
WpChevronRight
Join the largest storytelling communityGet personalized story recommendations, save your favourites to your library, and comment and vote to grow your community.
Illustration

You may also like

  • SAWUN GIWA...!🐘
  • KWANTAN ƁAUNA
  • ISMUHA ZAINAB Completed
  • 🌸RAYUWAR MU A YAU🌸
  • Penghulu Bidadariku S2 : Aisyah Humaira
  • BAYA DA ƘURA
  • MAI ƊAKI...!
  • NANATOOU (DIYAR KAKA)
  • 💤A MAFARKI NASANTA💤( I know her in my dream )
  • RUFAFFEN DUMA

"Dallah gafara can malama, har ke kin isa ki mana abunda Allah bai mana shi ba? Akanki ne aka Fara irin hakan? Ko kuwa akanki ne za'a daina? Sai wani ciccika bak'in banza kike awurin kamar zaki iya tabuka abun kirki idan har mukayo gaba da gabanta, Ke kin sani sarai ba yabon kai ba ammh wallahi tsab zan tumurmusheki anan wurin kuma in zauna lfy lau agidan Mijina, Kuma ki saurareni dak'yau, halinki ne ya jaza miki wannan cin amanar, Ke kowacce mace tana mafarkin samun miji kamar naki ammh ke Allah ya baki salihin mutum mai tsoron Allah, Sai ke kuma kikai amfani da hakan kina muzguna masa? Bashi da iko da gidansa sai yadda kikai? Babu wata muryar da yake tsoro da shakka face naki? To wallahi ki sani da'ace ayau bani da aure ne to Kinji nace Allah mijinki zan aura, zan shawo kansa kuma dole ya saurareni don kowacce mace da salon nata kissar, balle ma idan yaga ina masa abunda ke baki masa shi, kin san Zuciya nason mai faranta mata, ke mahaukaci kankat kenan yana kaunar mai faranta masa balle mai hankali, Hajiya Sa'a kiyi kuka da kanki ba dani ba don iya allonki ne yaja miki Faruwar hakan." Kuka sosai Hajiya Sa'a ke rerawa don ta kasa Furta komai kuma, Hajiya Aisha ta gama kashe mata jiki, Kama baki Hajiya Aishar tayi tana Fadin"Ai baki ma soma kukan ba, nan gaba kadan zakiyi wanda yafi wannan, kuma ki saurareni dak'yau, ga 'yata nan amana, Ku Zauna lfy ke da ita don wallahi kika sake naji ance ko ciwon kai kin sakata Allah saina lahira ya fiki jindadi, don kwarai zan cire kunyar Surukuta da amintar dake tsakaninmu musa wando kafa daya dani dake, Sabida haka ki kiyaye sannan Kuma akyalesu su sha amarcinsu Cikin kwanciyar hankali, don wallahi Hajiya Sa'a tashin hankalinsu kema tashin hankalinki, Tun wuri ki iya takunki don karki ce ban fada miki ba, Suhaila ita kadai ce 'yar da Allah ya bani sabida haka zan iya yin komai akanta, Ki huta lfy."

More details
WpActionLinkContent Guidelines