'Ammi ya zan yi da rayuwata? Ya kuke so in yi da zuciyata? Ban taba ba...daidai da rana daya ban taba mafarkin yin rayuwar aure ba tare da Ameer ba. Na roke ku da Allah ku zuba idanuwanku kawai a kaina, ina ji da kun san yadda zuciyata ke tafarfasa a duk lokacin da kuka yi min zancen auren wani wanda ba Ameer ba da tuni kun daina...' Kuka sosai take yi, kukan da ke fitowa tun daga k'asan zuciyarta yana ratsowa tsakanin idanuwanta. 'Na sani akwai zafi da radadi Ameerah, na san miye so, na san gubarshi saboda ni ma na tab'a dandana. Sai dai Ameerah ba za mu zura miki idanuwa ba, shekarunki ashirin da takwas kenan babu aure, kina zaune jiran gawon shanu. Waye ya san inda Ameer yake yanzu? Wa ma yake da tabbacin yana da rai ko babu?'