Story cover for Rayuwar Nabeela by Z11AMN
Rayuwar Nabeela
  • WpView
    Reads 298
  • WpVote
    Votes 9
  • WpPart
    Parts 4
  • WpHistory
    Time 1h 8m
  • WpView
    Reads 298
  • WpVote
    Votes 9
  • WpPart
    Parts 4
  • WpHistory
    Time 1h 8m
Ongoing, First published Oct 23, 2021
Mun kasance marayu nida kanina  mun rasa  uwa tun muna da karanci shekaru,bani da kowa sai  kanina Fahad sai Dai Kash shima ya gamu da ciwon blood cancer wanda sanadin Haka rayuwa ta shiga ukubar da ta fi da...shin sadaukarwa da nayi Dan ceto rayuwar d'an uwana zai haifar da d'an me Ido??? Ki karanta labarin Rauwar Nabeela.....sai dai ki tabbatar kin ajiye tissue kusa Domin labarina ta banbanta da sauran
All Rights Reserved
Sign up to add Rayuwar Nabeela to your library and receive updates
or
Content Guidelines
You may also like
 AFRA  by Smiling_Bay
57 parts Complete
Murmushi tayi mishi wanda ya tafi da imanin sa yayin da ta juya kallonta ga duɓɓin mutanen wajen. Dogayen yatsunta biyu wanda suka sha jan lalle ta buga akan speakern dan ta ga ko yana aiki. Illai kuwa sai ta ji ƙaran bugun da tayi. Murmushi ta ƙara sakar wa mutanen da duk ita suke kallo, da mamaki a idanuwansu, kafin ta buɗe baki tafara magana kamar haka. " Assalamu alaikum " sai ta ɗan dakata kaɗan don su amsa mata, ba laifi wasu sun amsa mata wasu kuma sunyi ƙum da bakin su. " dama na zo ne don na nuna farinciki na game da taya abokin mu, kaninmu da yayen mu Salim murna " tace yayin da take kallon angon wanda tun tahowarta stage yake warwara ido kamar baƙin munafuki, gashi yanda zufa yake ta keto masa, zaka zata ba ac a wajen. Kau da idanunshi yayi kafin su hadu da nata. " amma kuma abin da ya sosa min rai game da wannan abin shine ni nafi chanchanta da a kira in zo in bada tarihin wanan bawan Allah. " ta ƙara dan dakatawa yayin da ta runsunar da kanta kamar mai wani tunani, sai kuma ta k'ara daga kanta ta kalle mutanen da duk suke yi mata kallon mahaukaciya wadda batasan abin da take ba. Budar bakin ta ne sai tace. " duk da dai an kira abokin ango yayi nasa bayanin barin in ɗan baku tak'aitaccen nawa ". " amarya Salima " tace tana kallon amaryar da tace kwalliya a cikin doguwar riga kalar ja itama, sai dai na amaryar bai kai na wannan budurwar kyau da tsaruwa ba, dan inbaka san wacce amaryar ba sai kazata itace. Salima wacce tun da yarinyar tafara magana ta ke ta faman bankamata harara, taja wani ɗan tsaki game da sake sakarmata wani hararan. Afra , yarinyar da ta ke kan stage in ta murmusa kafin tace ." ina taya ki murnar auran munafukin namiji, azzalume wanda bai san darajar mutane ba, ina kuma ƙara tayaki murnar samun daƙiƙin na namiji wanda ban da wata shakka ƙarshen sa bazai yi kyau ba, kuma ki kasa kunan ki kiji mijinko mayaudari ne, me bin mata ne kuma zan iya rantse miki fasiƙi ne " Read and find out
RAYUWAR BADIYYA ✅  by Aishatuh_M
61 parts Complete
"Tun ina yarinya kike zagin mahaifiyata, tun bansan menene maanar kalmomin wulakanci da muzgunawa ba nakejin kina fadarsu ga mahaifiyata, ina cikin wannan halin wani azzalumi yaje ya kashe min mahaifiya, a gaban idona kika hana a tafi dani inda zanji dadin rayuwata, babu yadda na iya haka na biyoki inda kika doro mani karan tsana, kullum sai kin zage kin dukeni, sunan mahaifiyata kuwa ya zama abun zagi a gareki a koda yaushe, kin hanani abinci, kin sakani wanka da ruwan sanyi lokacinda ake matukar sanyi, kin cuceni iya cutuwa, a haka Allah ya rayani. Sai ke yau dan rana daya kince zakici uwata nace nima zanci taki shine zakiyi kukan munafurci? Ni kin taba laakari da irin kukan danake cikin dare kullun? Dukda mahaifiyata ta rasu hakan bai hanaki zaginta ba. To na fada da babbar murya, wallahi duk kika kara cewa zakici uwata to sai naci taki uwar nima, and that's final!" Zuwa yanzu duk bakin cikin dake zuciyar Badiyya saida ya fito, kuka take kamar ranta zai fita, mahaifiyarta kawai takeda bukata, bakin ciki ya mata yawa, batada wanda zai saka ranta yayi sanyi bayan Momynta, amma tayi mata nisan da yakeda wuyar isa. Ta buda baki zatayi magana kenan Ahmad ya wanke ta da marika kyawawa guda biyu, ta dama da haggu, rike wajen tayi tana kallonshi. Magana ya fara cikin tsananin bacin rai, "Yanzu Badiyya a gabana kike cewa zakici uwarta? Uwata kenan fa Badiyya! To ko Yaya kika zaga bazan kyaleki ba balle wadda ban taba gani ba, dan haka wallahi zakiyi mugun dana sani," ya fada cikeda tsananin fushi, yana kara kai mata mazga saman kai. Kukane ya kara kwace mata "Kai kenan da baka taba ganin taka ba, nifa? Nifa Dady?! Na taba ganinta, nasanta, nasan dadin uwa, amma haka wani azzalumin ya raba ni da ita, sannan kai da nake tunanin zaka share min hawaye kaine kake kara sakani kuka, me na maka? Me Momyna ta maka?" Ta tambaya tana kureshi da idanu. _______ Me zai faru a rayuwar yarinya yar shekara goma data rasa mahaifiyarta? Wace irin rayuwa zatayi a gidan yayar mahaifinta?
You may also like
Slide 1 of 10
DOCTOR'S FAMILY cover
KAICO NAH cover
 AFRA  cover
MURADIN ZUCIYA cover
WATA KISSAR (Sai Mata)  cover
RAYUWAR BADIYYA ✅  cover
IGIYAR ZATO....💕 || PAID NOVEL (COMPLETED✅) cover
Namiji Kanin Ajali cover
DA AURENA cover
RAYUWA TA THE NOVEL cover

DOCTOR'S FAMILY

67 parts Complete Mature

Family ne me cike da abun mamaki, gaba ɗayan su sun kasance DOCTORS ne, Rayuwar Ɗahira da Usman waɗanda suka kasance cikin Familyn, sun kasance maƙiyan juna, inda ƙaddara ta zo ta haɗa su aure, suna zama ne tamkar za su kashe juna don ƙiyayya, ya tsane ta tun tana tsumman goyo, kuma shi ya koya mata tsanar sa tun bata san meye tsana ba. Inda gefe ɗaya Ɗahira take zagaye da maƙiyan ta, mutanen da suke son ganin bayan ta, inda kuma ta faɗa soyayyar Yayan ta batare da tasan shi ne suke soyayya ba, sai ƙadddaran auren maƙiyin ta ya zo ya raba su, tare da gudummawar mahaifiyar sa, wacce babu wanda tafi tsana sama da ita. shin ya labarin nasu zai kaya? Bi Ni a sannu don jin labarin waɗannan maƙiyan junan.