AN YI SAKE
  • WpView
    OKUNANLAR 735
  • WpVote
    Oylar 41
  • WpPart
    Bölümler 19
WpMetadataReadDevam ediyor3h 9m
WpMetadataNoticeSon yayınlanan Paz, Şub 19, 2023
Yar mace shi ne sunan da mutanen unguwarmu suke ba da kwatance na ga kowa, sai dai ban taɓa ɗauka sunan wani giɓi na rayuwata ba, domin a iya wayo da tunanina ina ganin kowanne ɗa ko 'ya dukkan mu 'Yayan mace ne, domin mace ce ta durƙusa akan guiyoyinta tsayin awanni ko kwanaki kwatankwacin tsayin wahalar da Ubangiji ya yanka mata kwatankwacin azabar ciwon da ta shanye kafin zuwanmu duniya, bayan tazarar shuɗewar watanni tara mun rayuwa a cikinta cikin wahala da juriyar ciwo kala-kala, kafin girma da mallakar hankalin kanmu ta jure faɗi tashi na wahala damu tsayin shekaru ba tare da gajiya wa ba, a ganina idan har ba a kiramu da 'Yayan mace mun amsa ba da wane suna za a kiramu mu amsa? Saɓanin nawa sunan da ya dinga amsa kuwwa kafin ɓulluwar wannan, wato Shegiya ko 'Yar shege ba laifi don mutane sun rasa sunan da ya da ce su kira ni da shi duk da cewar ina da sunan yankan da aka ba ni kamar kowanne ɗa a duniya mene laifina don na rasa adon sunan Uba a gaban sunana kamar kowanne cikakken mutum na duniya? Mahaifiyata wacce ta durƙusa ta kawo ni duniya ba ta taɓa ba ni damar sanin ko ni wacece ba, a karan kaina ina tambayar wacece ni? Amsa ni baiwa ce.
Tüm hakları saklıdır
En büyük hikaye anlatıcılığı topluluğuna katılınKişiselleştirilmiş hikaye önerileri alın, favorilerinizi kütüphanenize kaydedin ve topluluğunuzu büyütmek için yorum yapın ve oy verin.
Illustration

Ayrıca sevebilecekleriniz

  • ABUL KHAIRI 2021
  • Milik Tuan Megat [𝒞 ]
  • NANA AMINATU 2022
  • 🌸RAYUWAR MU A YAU🌸
  • ZATOH
  • FATU A BIRNI (Complete)
  • KOWA YA GA ZABUWA...
  • BAHAGON TUNANI
  • RAYUWAR BADIYYA ✅
  • SHAREEF 2023

Daskare wa yayi a wajen tamkar an zare masa rai, sai da yaji wani dumm kamar ba ya duniyar, kafin ya dawo hayyacin sa, wani irin zaro idanu waje yayi ya nufe ta da sauri yana salati Duƙawa yayi gaban ta, ya saka hannyen sa da kamar za su tsinke tsaban rawan da suke yi, wuƙan ya ɗauka yana me kiran sunan ta "Ke.. ke ZIYADA.. ke.. tashi mana meye.. haka?" Yayi maganar kamar zuciyar sa zata faso ƙirjin sa tsaban tsoro Girgiza ta ya hau yi, amma dai kamar ba ta motsi, kamar dai ranta ya daɗe da fice wa a jikin ta. Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.. haƙiƙa wannan abun da ya faru ƙaddaran sa ne, mafarin shi ne shigowar ta rayuwan sa, domin ita ɗin ƙaddaran sa ce, kuma Bawa ba ya tsallake wa ƙaddaran sa me kyau ko mara kyau, ABUL KHAIRI ya shiga tsaka me wuya, kuma ya yi dana-sanin bijirewa iyayen sa zaɓin da suka yi masa, ya bi son zuciyar sa.

Daha fazla bilgi
WpActionLinkİçerik Rehberi