Story cover for AN YI SAKE by JannatQurratulayn
AN YI SAKE
  • WpView
    Membaca 704
  • WpVote
    Vote 41
  • WpPart
    Bab 19
  • WpHistory
    Durasi 3h 9m
  • WpView
    Membaca 704
  • WpVote
    Vote 41
  • WpPart
    Bab 19
  • WpHistory
    Durasi 3h 9m
Bersambung, Awal publikasi Mei 17, 2022
Yar mace shi ne sunan da mutanen unguwarmu suke ba da kwatance na ga kowa, sai dai ban taɓa ɗauka sunan wani giɓi na rayuwata ba, domin a iya wayo da tunanina ina ganin kowanne ɗa ko 'ya   dukkan mu 'Yayan mace ne, domin mace ce ta durƙusa akan guiyoyinta tsayin awanni ko kwanaki kwatankwacin tsayin wahalar da Ubangiji ya yanka mata kwatankwacin azabar ciwon da ta shanye kafin zuwanmu duniya, bayan tazarar shuɗewar watanni tara mun rayuwa a cikinta cikin wahala da juriyar ciwo kala-kala, kafin girma da mallakar hankalin kanmu ta jure faɗi tashi na wahala damu tsayin shekaru ba tare da gajiya wa ba, a ganina idan har ba a kiramu da 'Yayan mace mun amsa ba da wane suna za a kiramu mu amsa? Saɓanin nawa sunan da ya dinga amsa kuwwa kafin ɓulluwar wannan, wato Shegiya ko 'Yar shege ba laifi don mutane sun rasa sunan da ya da ce su kira ni da shi duk da cewar ina da sunan yankan da aka ba ni kamar kowanne ɗa a duniya mene laifina don na rasa adon sunan Uba a gaban sunana kamar kowanne cikakken mutum na duniya? Mahaifiyata wacce ta durƙusa ta kawo ni duniya ba ta taɓa ba ni damar sanin ko ni wacece ba, a karan kaina ina tambayar wacece ni? Amsa ni baiwa ce.
Seluruh Hak Cipta Dilindungi Undang-Undang
Daftar untuk menambahkan AN YI SAKE ke perpustakaan kamu dan menerima pembaruan
atau
Panduan Muatan
anda mungkin juga menyukai
FATU A BIRNI (Complete) oleh suwaibamuhammad36
18 bab Lengkap
"I promise you Mami, zan nemo miki ƴar'uwarki a duk inda take a faɗin ƙasar nan. SULTAN promises you that." Sultan ya shiga ya fita, har ya aikata abunda ba'a tsammani domin ya cika wannan alƙawari da ya ɗaukawar mahaifiyarshi, aka yi dace ya gano inda take. Wani abun takaici shine a maimakon ya samu ƴar'uwar Maminshi kamar yanda ya ci buri, sai ya haɗu da ƴarta kwalli ɗaya tak da ta haifa a duniya ta bari cikin ƙauyanci da kuma rashin wayewa. Baƙin cikinshi bai tsaya a nan ba, domin dattijon da yake riƙe da ita a take ya aura masa yarinyar ba tare da ya iya kaucewa wannan mummunan ƙaddaran ba. Ya tafi ya barta ba tare da ya sake waiwayarta ba, ya kuma tafi da wani kaso na zuciyarta ba tare da ya sani ba. Fatu (Fatima) ta ji haushi, sannan tana cikin baƙin cikin tafiyar da mijinta yayi ya barta. Tun tana tsumayinshi tana fatan ya dawo ya ɗauketa, har zuciyarta ta daskare da tsantsar tsanarshi na wofintar da ita da yayi, da kuma banzatar da igiyar aurensa dake kanta. Tayi alƙawarin ɗaukan fansa, ta kuma yi alƙawarin raba tsakaninsu ko da duniya zasu taru su hanata. Sai ta nemo shi a duk inda yake. Ta shiga cikin Birni nemansa, a nan kuma ƙaddara ya gifta tsakaninsu suka haɗu a lokaci da kuma yanayin da basu yi tsammani ba. Shi kuma ganin kyakkyawar baƙuwar fuska mai ɗauke da kamala, ya sashi faɗawa cikin sonta dumu-dumu ba tare da ya shiryawa hakan ba, kuma ba tare da ya gane cewa Matarsa ce ta Sunnah ba, Halal ɗinsa. Me zai faru idan Fatu ta haɗu da mutumin da ta ƙullata tsawon shekaru a yayin da shi kuma yake jinta a zuciyarsa tamkar ruhinsa? Me kuma zai faru Idan wasu sirrikan suka bayyana a lokacin da ba'a shirya musu ba? Fatu mace ce ɗaya mai hali mabanbanta; Fatu- Matar Sultan. Fatima- Budurwar Sultan.
RAYUWAR BADIYYA ✅  oleh Aishatuh_M
61 bab Lengkap
"Tun ina yarinya kike zagin mahaifiyata, tun bansan menene maanar kalmomin wulakanci da muzgunawa ba nakejin kina fadarsu ga mahaifiyata, ina cikin wannan halin wani azzalumi yaje ya kashe min mahaifiya, a gaban idona kika hana a tafi dani inda zanji dadin rayuwata, babu yadda na iya haka na biyoki inda kika doro mani karan tsana, kullum sai kin zage kin dukeni, sunan mahaifiyata kuwa ya zama abun zagi a gareki a koda yaushe, kin hanani abinci, kin sakani wanka da ruwan sanyi lokacinda ake matukar sanyi, kin cuceni iya cutuwa, a haka Allah ya rayani. Sai ke yau dan rana daya kince zakici uwata nace nima zanci taki shine zakiyi kukan munafurci? Ni kin taba laakari da irin kukan danake cikin dare kullun? Dukda mahaifiyata ta rasu hakan bai hanaki zaginta ba. To na fada da babbar murya, wallahi duk kika kara cewa zakici uwata to sai naci taki uwar nima, and that's final!" Zuwa yanzu duk bakin cikin dake zuciyar Badiyya saida ya fito, kuka take kamar ranta zai fita, mahaifiyarta kawai takeda bukata, bakin ciki ya mata yawa, batada wanda zai saka ranta yayi sanyi bayan Momynta, amma tayi mata nisan da yakeda wuyar isa. Ta buda baki zatayi magana kenan Ahmad ya wanke ta da marika kyawawa guda biyu, ta dama da haggu, rike wajen tayi tana kallonshi. Magana ya fara cikin tsananin bacin rai, "Yanzu Badiyya a gabana kike cewa zakici uwarta? Uwata kenan fa Badiyya! To ko Yaya kika zaga bazan kyaleki ba balle wadda ban taba gani ba, dan haka wallahi zakiyi mugun dana sani," ya fada cikeda tsananin fushi, yana kara kai mata mazga saman kai. Kukane ya kara kwace mata "Kai kenan da baka taba ganin taka ba, nifa? Nifa Dady?! Na taba ganinta, nasanta, nasan dadin uwa, amma haka wani azzalumin ya raba ni da ita, sannan kai da nake tunanin zaka share min hawaye kaine kake kara sakani kuka, me na maka? Me Momyna ta maka?" Ta tambaya tana kureshi da idanu. _______ Me zai faru a rayuwar yarinya yar shekara goma data rasa mahaifiyarta? Wace irin rayuwa zatayi a gidan yayar mahaifinta?
SAWUN GIWA...!🐘 oleh Hafnancy01
18 bab Lengkap
"Dallah gafara can malama, har ke kin isa ki mana abunda Allah bai mana shi ba? Akanki ne aka Fara irin hakan? Ko kuwa akanki ne za'a daina? Sai wani ciccika bak'in banza kike awurin kamar zaki iya tabuka abun kirki idan har mukayo gaba da gabanta, Ke kin sani sarai ba yabon kai ba ammh wallahi tsab zan tumurmusheki anan wurin kuma in zauna lfy lau agidan Mijina, Kuma ki saurareni dak'yau, halinki ne ya jaza miki wannan cin amanar, Ke kowacce mace tana mafarkin samun miji kamar naki ammh ke Allah ya baki salihin mutum mai tsoron Allah, Sai ke kuma kikai amfani da hakan kina muzguna masa? Bashi da iko da gidansa sai yadda kikai? Babu wata muryar da yake tsoro da shakka face naki? To wallahi ki sani da'ace ayau bani da aure ne to Kinji nace Allah mijinki zan aura, zan shawo kansa kuma dole ya saurareni don kowacce mace da salon nata kissar, balle ma idan yaga ina masa abunda ke baki masa shi, kin san Zuciya nason mai faranta mata, ke mahaukaci kankat kenan yana kaunar mai faranta masa balle mai hankali, Hajiya Sa'a kiyi kuka da kanki ba dani ba don iya allonki ne yaja miki Faruwar hakan." Kuka sosai Hajiya Sa'a ke rerawa don ta kasa Furta komai kuma, Hajiya Aisha ta gama kashe mata jiki, Kama baki Hajiya Aishar tayi tana Fadin"Ai baki ma soma kukan ba, nan gaba kadan zakiyi wanda yafi wannan, kuma ki saurareni dak'yau, ga 'yata nan amana, Ku Zauna lfy ke da ita don wallahi kika sake naji ance ko ciwon kai kin sakata Allah saina lahira ya fiki jindadi, don kwarai zan cire kunyar Surukuta da amintar dake tsakaninmu musa wando kafa daya dani dake, Sabida haka ki kiyaye sannan Kuma akyalesu su sha amarcinsu Cikin kwanciyar hankali, don wallahi Hajiya Sa'a tashin hankalinsu kema tashin hankalinki, Tun wuri ki iya takunki don karki ce ban fada miki ba, Suhaila ita kadai ce 'yar da Allah ya bani sabida haka zan iya yin komai akanta, Ki huta lfy."
NANATOOU (DIYAR KAKA) oleh AishaMaaruf1
20 bab Bersambung
Labari ne akan wata Yar kauye da aka sangarta ta, Duk kauyen su ta addabi kowa ba mai iya tsawata mata, tun daga yara, matasa, yan mata, tsoffi, hatta da sarkin garin duk ta addabe su........................ wani matshin saurayi da baze wuce shekara sha takwas ba ya ce"ya ana miki magana kin miyar da mutane yan iska". kallan Shi tayi Sama da kasa tana gyara dan kwalin ta sai wani murgude murgude take ta ce"ba yan iska ba karuwai da kwartaye na mai da ku ko kuma ka ce yan goguwa ta fada tana murgude baki tare da hararar shi". Keh ni za kiwa rashin kunya, ganin yanda ya harzuka yasa ta ja da baya tana shirin ko ta kwana, dan ubanki ni zaki zaga, ja da baya ta yi ta tattare zanin ta ta ce" ba dai ubana ba sai dai ubanka mln salisu mai wankin hula". Toh wallahi ubanki zan ci idan na kama ki, sai na karya kasusuwan ki dan duk dangin ku ba sa'a na. Wani wawan birki ta ja har tana kokarin faduwa ta ce"kaiiiiiiii! Amman kai mugun makaryaci ne, tsabar raini da rashin ta ido ni zaka kalla kace min duk dangin mu ba sa'an ka, toh ina ka aje aboki balle kuma yaya mugu ehhhhhh!, ko dai abinda ka ke sha ne ya fara dagula maka lissafi, kun san ku samarin zamanin nan ba a raba ku da aaaa, ta fada tana gwada mishi yanda ake shan taba". Iya kuluwa ya kulu ya dade yana jin irin rashin mutunci da takewa mutane, abin yau yazo kan shi, dutsen dake kusa da shi ya raruma zai Jefe ta da shi tsohon dake tsaye yana kallon su ya ce"kul dan nan kar ka kuskura", bata ko san suna yi ba dan tuni ta yi gaba............................ Mu haɗu da ku a cikin labarin..... Started Fri sep/12/2025 Finish................
anda mungkin juga menyukai
Slide 1 of 10
KAICO NAH cover
FATU A BIRNI (Complete) cover
MAI ƊAKI...! cover
BAHAGON TUNANI  cover
RAYUWAR BADIYYA ✅  cover
SAWUN GIWA...!🐘 cover
DARE DUBU cover
KOWA YA GA ZABUWA... cover
Milik Tuan Megat [𝒞 ] cover
NANATOOU (DIYAR KAKA) cover

KAICO NAH

56 bab Lengkap

Shin abinda nayi zan samu sassaucin allah kuwa bare na iyayena,wanda sun yi alkwarin duk wanda yayi mua'amala dani bashi basu. Taya zan tunkaresu bare na fada musu cewa duniya tayimin zafi..........?😓😓😓 Ina ganin na fita a wannan chakwakiyar ashe wata na kuma tsunduma kaina,wacce na mayar tamkar mujiya a cikin kawaye ita ce tayimin zarrar da bazan iya kama ko da tafin kafarta ba............. Taya zan iya zaman gidan auren da koda akwai bora a gidan to tafinin daraja da matsayi....... Wai tukunna ma mai ya rufemin ido nabi rudin zamanine haka,meyasa na kasa gane shi lokaci dama ce wacce bazata taba maiamaituwa ba a rayuwa......... Kaico nah..,.....😥😥😥😥!!!h Hakika ina cikin tsaka mai wuyah ni sumayyah.......