Tashi ya yi a sanyaye ya fita ya daga falon, dan zama a ciki zai iya saka sa hauka na wucin gadi. Mota ya shiga ya fita daga gidan a guje. Sai da ya yi nisa ya tsaya a kan hanya, ya kifa kansa a kan steering motar cikin tashin hankali da tsoro mai yawa. Zuciyarsa bugawa take yi sosai, ji yake kamar ya yi hauka, tunaninsa yana ga abinda Abba ya faɗa masa. Da gaske dai matarsa Manal ƙanwarsa ce ta jini ko wasa ake masa? In hakan ya tabbata ya zai yi? In hakan ya tabbata me zai faru, wanne hali zai shiga? In hakan ya faru ya zai yi da ransa?. Allah ya sani yana matuƙar qaunar Manal, yana kallon ta matsayin abokiyar rayuwarsa kuma bugun zuciyarsa, kallon matarsa ma'ajin sirrinsa yake mata, kallon Manal yake a matsayin uwar yaronsa da yake cikin ta. Ta ya rana tsaka ake so a juyata ta koma ƙanwarsa wacce suke uba ɗaya? In hakan ya faru da wanne ido zai iya kallon ta matsayin ƙanwarsa da suke jini ɗaya? Ya matsayin ɗansa da yake cikin ta? Ɗansa ne ko ɗan ƙanwarsa?.
More details