Fitar min daga gida, karuwar banza karuwar wofi, saida kika gama yawon gantalin da tambaɗar taki zaki dawo mana gida? Babanta ne ya fito "barni da ita na kashe ta kowa ma ya huta tunda abin kunya take son janyo mana, tabaryar dake hannunshi ya wurga mata, ai da gudu tafita daga gidan inda mota tayi gaba da ita, take ta watse a titi. Bata jira komaiba ta mike duk ta gurje gwuiwa da hannunta ga shi ta fama ƙunar kafarta sai jini takeyi. "Wai meyasa duk wanda ya taimakeni koya nuna min kauna saiya mutu, duk kuma wanda bai kaunata yafi dadewa "Hafsat ke zancen zuci...