Story cover for SOFIA ✔ by DielaIbrahim
SOFIA ✔
  • WpView
    LECTURAS 569
  • WpVote
    Votos 43
  • WpPart
    Partes 24
  • WpHistory
    Hora 4h 16m
  • WpView
    LECTURAS 569
  • WpVote
    Votos 43
  • WpPart
    Partes 24
  • WpHistory
    Hora 4h 16m
Continúa, Has publicado sep 24, 2023
Nakasar rashin ƙwarin ƙafar da Sofia za tayi tafiya ita ce KALUBALE  da kuma JARABAWAR da ta shafe kowacce jarabawa zafi da ciwo.Binchiken likitoci sun gane cewa Kafafuwan Sofia tun a cikin cikin mahaifiyar ta suka samu rauni wanda hakan ya samu sila ne ta dalilin Depression a turance kenan, to amma likitoci sun faɗa cewa da ace mahaifiyar bata da ciki da ita zata samu rauni (na rashin ji, ko kuma rashin gani, ko ciwon hauka) sai akayi rashin sa'a uwar na ɗauke da juna biyu sai abin ya sauka akan abin da ke cikin ta,Maimakon yayi ma uwar illah sai yayi ma SOFIA illah aka haife ta nakasasshiya kuma likitoci sun tabbatar ba lallai ta iya tafiya ba saboda jijiyoyin da zasu taimake ta wajan tafiya sun mutu basu da karfin da zasu iya zama lafiyayyun jijiyoyi.

Shin da gaske ita ɗin MABARACIYA ce?,  Yaya zata kalli AL'UMMA ko yaya AL'UMMA zasu kalle ta?, SADAUKARWA mai cike da rugujewar Mafarkai da Burika, SARƘAƘIYA, KADDARA, RAYUWA mai cike da ZAGON ƘASA.
Todos los derechos reservados
Regístrate para añadir SOFIA ✔ a tu biblioteca y recibir actualizaciones
O
#91partner
Pautas de Contenido
Quizás también te guste
NAUYIN BAKI  de UwarBatoorl96
25 partes Continúa
Me Nauyin baki ke janyowa? Me Nauyin baki ke haifarwa? Me ke afkuwa da mutum sanadin nauyin baki? ABUBAKAR SADEEQ ya tsinci kanshi tsumdum cikin matsananciyar soyayyar HALIMATU SADIYA tun bata san kanta ba har ta kai ga ta mallaki hankalin kanta, amma NAUYIN BAKI ya hana shi furta mata har ya kai matakin ƙarshe na rasata, wanda a wannan lokacin bayyana mata soyayyarsa ba lallai ta amfanar da shi da komai ba, domin a nata ɓangaren kallon Yaya na cikin umma guda take masa, dan soyayyarta take sha da masoyin ranta kuma muradin zuciyarta ALIYU HAIDAR, wanda tsabar ƙauna da soyayya har ta kai ga sun haɗa sunansu ya koma guda, ire-iren yanda masoya ke yi AL-SAD(Aliyu+Sadiya), a haka har ta kai ga sun haura matakalar da za ta kai su ga cin ribar soyayya, ta hanyan mallakan junansu, ɗauki da shirin aurensu suke cikin matuƙar yunwar mallakan juna, sai dai wani hargitsi ya gifta suna gaf da cimma burin nasu. SHIN BURINSU NA MALLAKAN JUNA ZAI CIKA? SHIN WANDA SANADIN NAUYIN BAKI HAR YA KAI MATAKIN ƘARSHE NA RASATA YA MAKOMARSA TAKE? A MATAKIN ƘARSHEN NAN ZAI IYA SAMUN WATA ƳAR ƘOFA TA MAFITA? (ONE CHANCE)? KOKO DAI DOLE ZAI YI HAƘURI? IDAN YA SAMU ƳAR ƘOFA SHI WANDA TAKE SO YAKE SONTA YA ZAI YI? ANYA ZA TA BI WANDA KE SONTA TA BAR WANDA TAKE SO? WA KUKE TUNANIN ZA TA ZAƁA KO KO WA YA KAMATA TA ZAƁA? SADEEQ KO HAIDAR? KO DAI DUK RASATA ZA SUYI? AUREN WANDA TAKE SO KO AUREN WANDA KE SONTA? Akwai wani hanzari ba gudu ba habibties, rayuwa gaba ɗaya tana tattarene kuma tana tafiya bisa doron ƙaddaran da Rabbi ya ƙaddara mana tun fil'azal, ko ya bawa ya kai ga shirinsa to ba ya taɓa iya gujewa ƙaddararsa. MENENE ƘADDARAR SADIYA? WAYE ƘADDARAN SADIYA? WAI YAYA NE KAM HABIBTIES?
RAYUWAR BADIYYA ✅  de Aishatuh_M
61 partes Concluida
"Tun ina yarinya kike zagin mahaifiyata, tun bansan menene maanar kalmomin wulakanci da muzgunawa ba nakejin kina fadarsu ga mahaifiyata, ina cikin wannan halin wani azzalumi yaje ya kashe min mahaifiya, a gaban idona kika hana a tafi dani inda zanji dadin rayuwata, babu yadda na iya haka na biyoki inda kika doro mani karan tsana, kullum sai kin zage kin dukeni, sunan mahaifiyata kuwa ya zama abun zagi a gareki a koda yaushe, kin hanani abinci, kin sakani wanka da ruwan sanyi lokacinda ake matukar sanyi, kin cuceni iya cutuwa, a haka Allah ya rayani. Sai ke yau dan rana daya kince zakici uwata nace nima zanci taki shine zakiyi kukan munafurci? Ni kin taba laakari da irin kukan danake cikin dare kullun? Dukda mahaifiyata ta rasu hakan bai hanaki zaginta ba. To na fada da babbar murya, wallahi duk kika kara cewa zakici uwata to sai naci taki uwar nima, and that's final!" Zuwa yanzu duk bakin cikin dake zuciyar Badiyya saida ya fito, kuka take kamar ranta zai fita, mahaifiyarta kawai takeda bukata, bakin ciki ya mata yawa, batada wanda zai saka ranta yayi sanyi bayan Momynta, amma tayi mata nisan da yakeda wuyar isa. Ta buda baki zatayi magana kenan Ahmad ya wanke ta da marika kyawawa guda biyu, ta dama da haggu, rike wajen tayi tana kallonshi. Magana ya fara cikin tsananin bacin rai, "Yanzu Badiyya a gabana kike cewa zakici uwarta? Uwata kenan fa Badiyya! To ko Yaya kika zaga bazan kyaleki ba balle wadda ban taba gani ba, dan haka wallahi zakiyi mugun dana sani," ya fada cikeda tsananin fushi, yana kara kai mata mazga saman kai. Kukane ya kara kwace mata "Kai kenan da baka taba ganin taka ba, nifa? Nifa Dady?! Na taba ganinta, nasanta, nasan dadin uwa, amma haka wani azzalumin ya raba ni da ita, sannan kai da nake tunanin zaka share min hawaye kaine kake kara sakani kuka, me na maka? Me Momyna ta maka?" Ta tambaya tana kureshi da idanu. _______ Me zai faru a rayuwar yarinya yar shekara goma data rasa mahaifiyarta? Wace irin rayuwa zatayi a gidan yayar mahaifinta?
Quizás también te guste
Slide 1 of 10
NAUYIN BAKI  cover
IVAN QIDRAN cover
THE NEMESIS OF SAKINAH...KADDARAR SAKINAH✅ cover
I Got Love cover
AL'AJABIN SO cover
Penghulu Bidadariku S2 : Aisyah Humaira cover
WAYE MACUCI cover
MEEMA FARUKH cover
Saat Takdir Memilih [C] cover
RAYUWAR BADIYYA ✅  cover

NAUYIN BAKI

25 partes Continúa

Me Nauyin baki ke janyowa? Me Nauyin baki ke haifarwa? Me ke afkuwa da mutum sanadin nauyin baki? ABUBAKAR SADEEQ ya tsinci kanshi tsumdum cikin matsananciyar soyayyar HALIMATU SADIYA tun bata san kanta ba har ta kai ga ta mallaki hankalin kanta, amma NAUYIN BAKI ya hana shi furta mata har ya kai matakin ƙarshe na rasata, wanda a wannan lokacin bayyana mata soyayyarsa ba lallai ta amfanar da shi da komai ba, domin a nata ɓangaren kallon Yaya na cikin umma guda take masa, dan soyayyarta take sha da masoyin ranta kuma muradin zuciyarta ALIYU HAIDAR, wanda tsabar ƙauna da soyayya har ta kai ga sun haɗa sunansu ya koma guda, ire-iren yanda masoya ke yi AL-SAD(Aliyu+Sadiya), a haka har ta kai ga sun haura matakalar da za ta kai su ga cin ribar soyayya, ta hanyan mallakan junansu, ɗauki da shirin aurensu suke cikin matuƙar yunwar mallakan juna, sai dai wani hargitsi ya gifta suna gaf da cimma burin nasu. SHIN BURINSU NA MALLAKAN JUNA ZAI CIKA? SHIN WANDA SANADIN NAUYIN BAKI HAR YA KAI MATAKIN ƘARSHE NA RASATA YA MAKOMARSA TAKE? A MATAKIN ƘARSHEN NAN ZAI IYA SAMUN WATA ƳAR ƘOFA TA MAFITA? (ONE CHANCE)? KOKO DAI DOLE ZAI YI HAƘURI? IDAN YA SAMU ƳAR ƘOFA SHI WANDA TAKE SO YAKE SONTA YA ZAI YI? ANYA ZA TA BI WANDA KE SONTA TA BAR WANDA TAKE SO? WA KUKE TUNANIN ZA TA ZAƁA KO KO WA YA KAMATA TA ZAƁA? SADEEQ KO HAIDAR? KO DAI DUK RASATA ZA SUYI? AUREN WANDA TAKE SO KO AUREN WANDA KE SONTA? Akwai wani hanzari ba gudu ba habibties, rayuwa gaba ɗaya tana tattarene kuma tana tafiya bisa doron ƙaddaran da Rabbi ya ƙaddara mana tun fil'azal, ko ya bawa ya kai ga shirinsa to ba ya taɓa iya gujewa ƙaddararsa. MENENE ƘADDARAR SADIYA? WAYE ƘADDARAN SADIYA? WAI YAYA NE KAM HABIBTIES?