FITILAR KWAI

FITILAR KWAI

  • WpView
    Reads 1,180
  • WpVote
    Votes 25
  • WpPart
    Parts 23
WpMetadataReadOngoing3h 42m
WpMetadataNoticeLast published Tue, Jul 1, 2025
A wani zamani daya shuɗe, Da zarar magriba ta gabato kusan ko wani gida zaka riske su ɗauke da *FITILAR ƘWAI* Tun ba a fara min halitta ba na ke wahala, har tsahon watanni biyu a cikin ciki ina gwabzawa tare da mahaifata, ni ne ƙwan halittar dake cikin ta,ƙwan halittar da ake son a zubar. Kaifin kwakwalwar da Allah yayi ma jarirai ya sanya na ke fahimtar cikin labaran ta akwai rina a kaba. Mahaifiya ta ta shiga halin tsaka mai wuya, ta sha gwagwarmaya a rayuwar ta don kare ni daga magungunan da Abba na ya ke kawo mata don zubar da ciki na, Abba ya manta cewa mugun nufi, baya kashe ɗan barewa kuma da ikon Allah haƙan sa ba zai taɓa cimma ruwa ba akan gurbatacciyar buƙatar sa. A lokacin da sinadarin allurar ya feso zuwa mahaifar wato cikin in da na ke babu irin jijjigar da ban sha ba, maganin ya so ya tarwatsa sassan jiki na wanda bai da ɗe da zama tsoka ba, da ikon Allah na koma bayan mahaifarta na yi wa kai na ɓuya duk da tsananin wahalar da na sha tsakanin rayuwa ko mutuwa, Allah ya zaɓa min rayuwa, tsahon watanni shidda ina bayan mahaifarta sannan na dawo na zauna daram a cikin mahaifarta na kuma ɗaura daga kwanakin da na tsaya,lokacin na san da cewa kainuwa dashen Allah ne, haka zalika zakaran da Allah ya nufa da cara ana muzuru ana shaho sai yayi abin sa.
All Rights Reserved
#111
hausalovestory
WpChevronRight
Join the largest storytelling communityGet personalized story recommendations, save your favourites to your library, and comment and vote to grow your community.
Illustration

You may also like

  • A JINI NA TAKE
  • MIJIN TSOHUWA
  • KAICO NAH
  • Title: "Dua: Ek Roohani Mohabbat Ki Kahani " By( Sana Ijaz )
  • BAKAR WASIKA
  • FATU A BIRNI (Complete)
  • MATAR SADAM
  • NANA AMINATU 2022
  • Asmaraloka Saptakāla
  • SAFEENATU

Labari ne daya kunshi masarautu biyu; Masarautar Katsina, wacce take cikin Nigeria da kuma Masarautar Damagaran, wacce take cikin Kasar Niger. Labarin yayi duba ne da rayuwar Yarima Bilal, wanda rashin magana da miskilanci ya kanja ya shiga tarun matsaloli, wanda hakan yake haifar mashi da auren Zeenah Kabir Muhammad. Diyar Bafade da kuma baiwa. Me zai faru a rayuwar auren da aka hada miskili da kuma masifaffiya? Wanda dama tun farkon haduwarsu da masifa aka fara har yakai ga ya kure hakurinta ta sharara mashi maruka biyu? Shin ko zasu samu zaman lafiya kuwa? Bilal wanda ya kasance zuciyarshi a kulle take tun bayan rasuwar mahaifiyarshi zai bude ma Zeenah ita? Ya rayuwa zata basu bayan Zeenah ta fada soyayyarshi sai kwatsam Juwairiyya ta kunno kai? Wane hali Bilal zai shiga a lokacin da Fulani ta bankado wani tsohon sirri dake tsakaninsu? Fulani fah? Wacce take uwar gida kuma mai kula da hidimomin Masarautar Katsina gaba daya? Zata rufe sirrin data gano tsakanin Zeenah da Bilal dan gujewa tarwatsewar farin cikinsu? Abu daya ne zai kai ga na biyu, wanda har Bilal zai tsinci kanshi an mashi shamaki da Masarautar Katsina, hakan zai dangantashi da Masarautar Damagaran! Ku biyo Yar Malumfashi domin jin yadda labarin zai kasance.

More details
WpActionLinkContent Guidelines