NADIYA!

NADIYA!

  • WpView
    Reads 5,565
  • WpVote
    Votes 77
  • WpPart
    Parts 8
WpMetadataReadComplete Sun, Oct 20, 20241h 24m
'Ta dan juya kanta cike da mamaki, tace, "Daddynka kuma? wanene shi?" Yace, "Habib Abdullahi Makama?!" cikin sigar tambaya. Jin sunanshi kadai ma sai daya sanya taji bugun zuciyarta ya canza. A duka kwanakin da suka wuce tun bayan daya ajiyeta a kofar gidansu ya wuce, karya take yi tace babu wata rana da zata fito ta koma ga mahaliccinta bata tunano wannan mutumin ba. Abin har ya kusa zame mata jiki, yin tunaninshi a lokacin da taje yin kwanciya barci. Wasu dararen kuwa har da mafarkinshi da tunanin wannan daddadan kamshi nashi, wanda ta lalubo turaren da yake amfani dashi cikin wadanda ya bata, itama ta mayar dashi nata turaren. Yaudarar kanta take, da take cewa wai tuni ta manta da sha'aninshi da kurar data kwasoshi. Ita tasan karya take yiwa kanta. Duk kuma yadda taso abinda ke tukarta a zuciya kada ya bayyana, sai daya bayyana din. Ta rasa fara'ar kirkirowa tayi koda ta yake ce kuwa, haka bugun zuciyarta ya ki saisaituwa duk yadda taso ta saisaita shi kuwa. Ta daure dai da kyar tace, "ok, na ganeshi. Yana ina yanzu?" Ya dan daga kafada, "ban sani ba nima. Kawai dai yace in zauna a wajenki zai dawo ya daukeni." Ita abin ma sai ya girmame mata, mamaki ya hanata motsi. To ita kuma a su wa? Kuma da wane dalili? Da zai dauko danshi ya kai mata?..." To domin sanin dalilin, don me, kuma me yasa? Sai ku biyoni Ni Jeeddah Lawals tare da Nadiya a wannan tafiyar tamu.
All Rights Reserved
#23
hausaromance
WpChevronRight
Join the largest storytelling communityGet personalized story recommendations, save your favourites to your library, and comment and vote to grow your community.
Illustration

You may also like

  • NI DA KANNENA (Hausa Novel)
  • Penghulu Bidadariku S2 : Aisyah Humaira
  • Title: "Dua: Ek Roohani Mohabbat Ki Kahani " By( Sana Ijaz )
  • NI DA ABOKIN BABA NA
  • 💤A MAFARKI NASANTA💤( I know her in my dream )
  • KOWA YA GA ZABUWA...
  • SAWUN GIWA...!🐘
  • MATAR SADAM
  • GADAR ZARE
  • RUHI BIYI (a gangar jiki daya)

SHARHI AKAN LITTAFIN "NIDA KANNENA' "BISMILLAHIRRAHMANIRRAHEEM!" "WASSALATU WASSALAMU ALA RASULULLAHI (SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM)" "A'UTHUBIKHALIMATULLAHI TAMMAT MIN SHARRI MÁKHALAQ" "RABBISHRAHLIY SADRIY WAHLIL UQDATUN MIN LITHANIY YAFQAHU QAULIY" "ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH WABARAKATUHU" ƳAN UWANA WANNAN SHINE RUBUTU NA NA FARKO DA NA FARA WALLAFAWA A WATA KAFA TA SADA ZUMUNTA INA NEMAN ADDU'AR KU DA GOYON BAYAN KU SANNAN KOFAR MU A BUƊE TAKE WAJEN BAMU KUSKURE DON MU GYARA TA HANYAR LISILAMA BA TARE DA ZAGI KO CIN MUTUNCI BA. WANNAN RUBUTU ƘIRƘIRARREN LABARI NE KUMA FASAHA TA CE TAWA TA KAI NA BABU HADAKA KO HAFIN GWIWA DA WANI KOKUMA KWAIKWAYON RAYUWAR WANI KO AIKIN WANI IDAN KAJI WANI BANGAREN YAYI KAMA DA RAYUWAR KA KO AIKIN KA TO KAYI MANA AFUWA BAMUYI DON TOZARCI BA. SANNAN YANA DAUKE DA HATIMIN RASHIN SAHALEWAR KWAFAYYA (copy right) BAN YARDW WANI KO WATA SUYI AMFANI DASHI BA SAHALEWA TA BA YIN HAKAN ZAI KAIMU GA MATAKIN SHARI'A. SABODA HAKA A KIYAYE. NI DA KANNENA" LABARI NE SARKAKIYA, MAI CIKE DA DARASUSSUKA NA RAYUWA, DA SUKA SHAFI JARUMTA, SADAUKARWA, JAJIRCEWA AKAN SHA'ANIN RAYUWA, HAKURI, JURIYA, DA NAGARTA. ZAI DINGA ZUWAR MUKU DUK RANAR LARABA DA DADDARE INSHAALLAHU A KAFOFI KAMAR HAKA: WATTPAD: @khadijaaliyuibrahim FACEBOOK: Hausa novels by k_d_j WhatsApp: 08129464832(kayi message da inaso a sani a novel group). Written and edited by: Khadija Aliyu Ibrahim 08129464832

More details
WpActionLinkContent Guidelines