DAHUWAR ƘAHO

DAHUWAR ƘAHO

  • WpView
    LECTURAS 1,082
  • WpVote
    Votos 5
  • WpPart
    Partes 15
WpMetadataReadContinúa3h 39m
WpMetadataNoticeÚltima publicación mar, jun 17, 2025
Ni da ku mun san, zamani rikiɗa yake tamkar hawainiya. Kowanne zamani da suffar da yake tafiyar da al'ummar cikinsa. A wannan zamanin na tafiyar biri a yashi, wasu matan sukan kalli ƙarin aure ta munanan fuskoki. Musamman yadda iyayen gida suke ganin wayonsu ne, yasa aka auro su a matsayin iyayen gida. Har wasu suke cin duniyarsu da tsinken tsire, ta hanyar gasawa amare gyaɗa a hannu. Su ɗanɗanawa maza kuɗarsu don hana su rawar gaban hantsi. Saboda suna ganin sun zama kujerun gida, dole a zauna da su.Ba tare da sun hangi me gobensu zata haifar ba. Duk yadda ake ganin iyayen gida suna juyin waina da amare,lamarin bai sauya zani ba. Domin ɓagaren amaren da suke cin alwashin mijin wata ne zaɓinsu, a guntun tunanin wasu. Suna tsammanin gazawar uwargida ne yake sa miji aurensu. Musamman wasu mazan, da suke kwayewa uwargida baya tun a neman aure. Silar haka amare suke hangen kansu a bigiren cusgunawa uwargida, don su nuna mata miji ya daina yayinta. Batare sun hangi yankan kunkurin-Balan da suke wa rayuwarsu ba.
Todos los derechos reservados
#10
zafafabiyar
WpChevronRight
Únete a la comunidad narrativa más grandeObtén recomendaciones personalizadas de historias, guarda tus favoritas en tu biblioteca, y comenta y vota para hacer crecer tu comunidad.
Illustration

Quizás también te guste

  • RAYUWAR BADIYYA ✅
  • BAYA DA ƘURA
  • KWANTAN ƁAUNA
  • Penghulu Bidadariku S2 : Aisyah Humaira
  • MAI ƊAKI...!
  • BAHAGON TUNANI
  • NADIYA!
  • SHAREEF 2023
  • FATU A BIRNI (Complete)
  • KOWA YA GA ZABUWA...

"Tun ina yarinya kike zagin mahaifiyata, tun bansan menene maanar kalmomin wulakanci da muzgunawa ba nakejin kina fadarsu ga mahaifiyata, ina cikin wannan halin wani azzalumi yaje ya kashe min mahaifiya, a gaban idona kika hana a tafi dani inda zanji dadin rayuwata, babu yadda na iya haka na biyoki inda kika doro mani karan tsana, kullum sai kin zage kin dukeni, sunan mahaifiyata kuwa ya zama abun zagi a gareki a koda yaushe, kin hanani abinci, kin sakani wanka da ruwan sanyi lokacinda ake matukar sanyi, kin cuceni iya cutuwa, a haka Allah ya rayani. Sai ke yau dan rana daya kince zakici uwata nace nima zanci taki shine zakiyi kukan munafurci? Ni kin taba laakari da irin kukan danake cikin dare kullun? Dukda mahaifiyata ta rasu hakan bai hanaki zaginta ba. To na fada da babbar murya, wallahi duk kika kara cewa zakici uwata to sai naci taki uwar nima, and that's final!" Zuwa yanzu duk bakin cikin dake zuciyar Badiyya saida ya fito, kuka take kamar ranta zai fita, mahaifiyarta kawai takeda bukata, bakin ciki ya mata yawa, batada wanda zai saka ranta yayi sanyi bayan Momynta, amma tayi mata nisan da yakeda wuyar isa. Ta buda baki zatayi magana kenan Ahmad ya wanke ta da marika kyawawa guda biyu, ta dama da haggu, rike wajen tayi tana kallonshi. Magana ya fara cikin tsananin bacin rai, "Yanzu Badiyya a gabana kike cewa zakici uwarta? Uwata kenan fa Badiyya! To ko Yaya kika zaga bazan kyaleki ba balle wadda ban taba gani ba, dan haka wallahi zakiyi mugun dana sani," ya fada cikeda tsananin fushi, yana kara kai mata mazga saman kai. Kukane ya kara kwace mata "Kai kenan da baka taba ganin taka ba, nifa? Nifa Dady?! Na taba ganinta, nasanta, nasan dadin uwa, amma haka wani azzalumin ya raba ni da ita, sannan kai da nake tunanin zaka share min hawaye kaine kake kara sakani kuka, me na maka? Me Momyna ta maka?" Ta tambaya tana kureshi da idanu. _______ Me zai faru a rayuwar yarinya yar shekara goma data rasa mahaifiyarta? Wace irin rayuwa zatayi a gidan yayar mahaifinta?

Más detalles
WpActionLinkPautas de Contenido