Story cover for KUSKURE by Shatuuu095
KUSKURE
  • WpView
    LECTURES 907
  • WpVote
    Votes 20
  • WpPart
    Chapitres 15
  • WpHistory
    Durée 1h 54m
  • WpView
    LECTURES 907
  • WpVote
    Votes 20
  • WpPart
    Chapitres 15
  • WpHistory
    Durée 1h 54m
Terminé, Publié initialement août 05, 2025
Hannu na karkarwa yake, jiki na har bari yake, saboda tun da nake Rai na Bai taba baci ba kamar yau, ban taba tunanin Baba zai iya abin da yayi yau ba, na saka hannu na na toshe kunne na saboda na daina Jin muryar shi, Amma tamkar a gaba na yake ihun, tamkar ni din yake yiwa masifa


"...Saboda ke Baki da mutunci, ke ba yar mutunci bace ba, har ni zance kiyi Abu ki kiyi, to se de ki bar min gida na yau dinnan, ki fito ki hada kayan ki ki bar min gida na, ni ba shashan namiji bane ba..."

He kept on saying, ya cigaba da fada Yana yarfa zagi, na zata zagi na Yan kauye ne, na zata ana yin zagi ne ga mutanen da ba su da ilimi, se gashi Baba ne yake zagin Mama a tsakar gida, a gaban mu, gaban kishiyar ta, gaban almajirai, masu aiki yake mata wannan cin mutuncin, nasan ya taba, ba sau daya ba, ba sau biyu ba Amma Bai taba cin mata mutunci irin na yau ba, a gani na ko Babu komai ya kamata taci albarkacin mu, ya kamata ya daga mata kafa saboda mu, se naji zuciya ta tana zafi, tana zugi na kasa hakuri na fito daga dakin, Kai a lokacin ma it's as though I'm possessed saboda wallahi kwakwalwa ta bata tare da ni, zuciya ta ce kawai ke fada min kada na bari, kada nayi shiru cin mutuncin yayi yawa, na kuwa fito tsakar gidan, gidan yayi tsit saboda Baba ya gama ya wuce dakin shi, se almajiran mu biyu suna yiwa Amarya shanyar labule da suka wanke mata, na wuce su na nufi dakin shi fuska ta tayi Wani irin ja, hatta wata vein da nake da ita a goshi na ta fito, tabbacin Rai na ya baci, Yana zaune na same shi a parlon shi, na kalle shi saboda ko sallama banyi ba shi ma ya kalle ni nace

"Baba! Me yasa zaka dinga cin zarafin Maman mu a gaban mu, a gaban kowa a gidannan, me tayi maka?"

Se ya dago ya kalle ni, I can see the amazement in his eyes, saboda yayi mamaki, baiyi tunanin bakar zuciya ta har ta Kai haka ba...




Inaaya
Tous Droits Réservés
Inscrivez-vous pour ajouter KUSKURE à votre bibliothèque et recevoir les mises à jour
ou
#5marriagecrisis
Directives de Contenu
Vous aimerez aussi
NANA AMINATU 2022, écrit par UmmuDahirah
56 chapitres Terminé Contenu pour adultes
Maganganun ta tamkar saukar kibiya take jin su a zuciyarta duk idan ta tuna, suna sukan ta su hana ta sukuni, suna tarwatsa ta su saka ta taji ita ƙasƙantanciya ce wacce bata kai ɗin ba kamar yadda take cewa, tana ganin baƙin kanta a koda yaushe a wacce bata kai ba, ko kaɗan bata taɓa saurara mata ba, ya za'a yi ta dena kallon kanta ta daban a cikin mutane yayinda take tuna duk wata kalma ta ɓatanci da take bin ta dasu a kullum ranan duniya? tun sanda ta buɗe idanuwanta da wayon ta take jin waɗannan munanan kalaman da ke tarwatsa mata duk wani farin ciki da jin daɗin ta. Sai dai kuma a duk sanda take jiyo kalaman sa sai ta ji ƙwarin gwiwa har ta kalli kanta a wacce ta kai kuma ta isa, ashe akwai ranan da zata yi farin ciki haka? Akwai ranan da wani zai iya yabon ta har ya nuna mata tana da matsayi fiye da sauran Mata? She can't believe that... Shi ne Mutum na farko da yake faɗa mata kalaman da idan ta ji su take ganin ta kai Mace, ta kai Mace cikakkiya ba wacce ta rako Mata ba, a kullum ganin kanta take yi a bata kai matsayin ba, ita bata kai Macen da zata iya fitowa ayi gwagwarmaya da ita a matsayin ta na ɗiya Mace ba. Shin wane ne shi wannan ɗin? Tabbas Ƙaddara kowa da irin tasa, wasu tana zuwar musu da sauƙi wasu kuwa akasin hakan, ba wai don wani ya fi wani bane a wurin Allah hakan ke faruwa, a'a, sai dai don Allah na gwada ko wanne bawa ta hanyar ɗaura masa tashi ƙaddaran, walau me sauƙi ko akasin sa, ko wanne bawa da tashi ƙaddaran kuma kowa yana fatan ace ya tsallake ƙaddaran da Allah ya ɗaura masa. Haka itama NAANA AMINATU tayi fafutuka a cikin rayuwar ta domin ta ga ta cinye nata ƙaddaran da ta kasance babba a gare ta. Na san Kuna so ku bibiyi labarin ta domin ku ji mene ne ya faru a rayuwar ta, to ku bi Ni sannu a hankali Zan warware muku komi a cikin sauƙi, ina fata labarin zai zame muku darasi a cikin rayuwa.
 AFRA , écrit par Smiling_Bay
57 chapitres Terminé
Murmushi tayi mishi wanda ya tafi da imanin sa yayin da ta juya kallonta ga duɓɓin mutanen wajen. Dogayen yatsunta biyu wanda suka sha jan lalle ta buga akan speakern dan ta ga ko yana aiki. Illai kuwa sai ta ji ƙaran bugun da tayi. Murmushi ta ƙara sakar wa mutanen da duk ita suke kallo, da mamaki a idanuwansu, kafin ta buɗe baki tafara magana kamar haka. " Assalamu alaikum " sai ta ɗan dakata kaɗan don su amsa mata, ba laifi wasu sun amsa mata wasu kuma sunyi ƙum da bakin su. " dama na zo ne don na nuna farinciki na game da taya abokin mu, kaninmu da yayen mu Salim murna " tace yayin da take kallon angon wanda tun tahowarta stage yake warwara ido kamar baƙin munafuki, gashi yanda zufa yake ta keto masa, zaka zata ba ac a wajen. Kau da idanunshi yayi kafin su hadu da nata. " amma kuma abin da ya sosa min rai game da wannan abin shine ni nafi chanchanta da a kira in zo in bada tarihin wanan bawan Allah. " ta ƙara dan dakatawa yayin da ta runsunar da kanta kamar mai wani tunani, sai kuma ta k'ara daga kanta ta kalle mutanen da duk suke yi mata kallon mahaukaciya wadda batasan abin da take ba. Budar bakin ta ne sai tace. " duk da dai an kira abokin ango yayi nasa bayanin barin in ɗan baku tak'aitaccen nawa ". " amarya Salima " tace tana kallon amaryar da tace kwalliya a cikin doguwar riga kalar ja itama, sai dai na amaryar bai kai na wannan budurwar kyau da tsaruwa ba, dan inbaka san wacce amaryar ba sai kazata itace. Salima wacce tun da yarinyar tafara magana ta ke ta faman bankamata harara, taja wani ɗan tsaki game da sake sakarmata wani hararan. Afra , yarinyar da ta ke kan stage in ta murmusa kafin tace ." ina taya ki murnar auran munafukin namiji, azzalume wanda bai san darajar mutane ba, ina kuma ƙara tayaki murnar samun daƙiƙin na namiji wanda ban da wata shakka ƙarshen sa bazai yi kyau ba, kuma ki kasa kunan ki kiji mijinko mayaudari ne, me bin mata ne kuma zan iya rantse miki fasiƙi ne " Read and find out
HAIRAN🔥💥♥️, écrit par Shatuuu095
23 chapitres Terminé
Tunda Anty ta fara magana, Prof yake kallon ta, idan ka kalle shi ba zaka taba fahimtar a yanayin da yake ciki ba, ba zaka fahimci emotions din shi ba, Amma yadda yake kallon Anty, da yadda ya bata dukkan hankalin shi, Abu ne da zai tabbatar maka cewar maganar babba ce. Anty ta gama bayanin ta tsaf sannan tayi shiru tana jiran ganin hukuncin da Prof zai yanke. Cikin nutsuwa yace " A Ina ta samu?" Shi ne tambayar da yayi ma Anty, maimakon tayi masa bayani se cewa tayi " Ai na Gama nawa professor, abin da ya rage kaji ta bakin HAIRAN kawai!" "Me yasa Anty?" Cike da nutsuwa tace " Saboda zaka ga kamar kare ta nake, Amma idan tayi maka bayani Ina Jin zaka fi gamsuwa da kyau!" Daga haka Prof yayi shiru Yana son ya auna nauyin Abubuwan da Anty ta fada Masa, se kawai ya Mike yayi ma Anty sallama ya fita. Kunsan yadda tsumma yake idan aka tsoma shi cikin ruwa ko? To haka Prof yayi, gaba daya jikin shi ya saki, yayi shiru tamkar wani kurma, ya bude mota ya shiga ya kifa Kan shi akan steerer wheel, shi yasa take fada Masa lallai lallai se sun rabu kenan? To Ina ta samu shi ne tambayar da take zuwa Masa... *** Shigowa ta kenan daga lecture, na gaji, gajiya kuwa matuka saboda shirin exams da muke, har lokacin bana cikin dadin rai, Abu ya kusa wata daya Amma still nukurkusa ta yake Yi. Ina Zama Saman gado Ina kallon Nuriyya da ta dakko wani gari tana kokarin kwaba shi da ruwa nace " Me zakiyi?" Tace "Kunun aya Mana!" Se nace " Kunun Aya Kuma, gaskiya Kin iya bawa Kai wahalar, ana shirin exams din!" Tayi dariya tare da daga min wata transparent ziplock tace " Waye zai Baki wani wahala, wannan ai is outdated, halan Baki San Islah foods ba ko? To ita take siyarda wannan garin na kunun Aya, yours is just to make little effort se ki Sha!" Nayi murmushi Amma kafin nayi magana se Naga Kiran Anty na shigowa cikin waya ta, da sauri nayi excusing Kai na sannan na mike Dan fita
NANATOOU (DIYAR KAKA), écrit par AishaMaaruf1
20 chapitres En cours d'écriture
Labari ne akan wata Yar kauye da aka sangarta ta, Duk kauyen su ta addabi kowa ba mai iya tsawata mata, tun daga yara, matasa, yan mata, tsoffi, hatta da sarkin garin duk ta addabe su........................ wani matshin saurayi da baze wuce shekara sha takwas ba ya ce"ya ana miki magana kin miyar da mutane yan iska". kallan Shi tayi Sama da kasa tana gyara dan kwalin ta sai wani murgude murgude take ta ce"ba yan iska ba karuwai da kwartaye na mai da ku ko kuma ka ce yan goguwa ta fada tana murgude baki tare da hararar shi". Keh ni za kiwa rashin kunya, ganin yanda ya harzuka yasa ta ja da baya tana shirin ko ta kwana, dan ubanki ni zaki zaga, ja da baya ta yi ta tattare zanin ta ta ce" ba dai ubana ba sai dai ubanka mln salisu mai wankin hula". Toh wallahi ubanki zan ci idan na kama ki, sai na karya kasusuwan ki dan duk dangin ku ba sa'a na. Wani wawan birki ta ja har tana kokarin faduwa ta ce"kaiiiiiiii! Amman kai mugun makaryaci ne, tsabar raini da rashin ta ido ni zaka kalla kace min duk dangin mu ba sa'an ka, toh ina ka aje aboki balle kuma yaya mugu ehhhhhh!, ko dai abinda ka ke sha ne ya fara dagula maka lissafi, kun san ku samarin zamanin nan ba a raba ku da aaaa, ta fada tana gwada mishi yanda ake shan taba". Iya kuluwa ya kulu ya dade yana jin irin rashin mutunci da takewa mutane, abin yau yazo kan shi, dutsen dake kusa da shi ya raruma zai Jefe ta da shi tsohon dake tsaye yana kallon su ya ce"kul dan nan kar ka kuskura", bata ko san suna yi ba dan tuni ta yi gaba............................ Mu haɗu da ku a cikin labarin..... Started Fri sep/12/2025 Finish................
SAWUN GIWA...!🐘, écrit par Hafnancy01
18 chapitres Terminé
"Dallah gafara can malama, har ke kin isa ki mana abunda Allah bai mana shi ba? Akanki ne aka Fara irin hakan? Ko kuwa akanki ne za'a daina? Sai wani ciccika bak'in banza kike awurin kamar zaki iya tabuka abun kirki idan har mukayo gaba da gabanta, Ke kin sani sarai ba yabon kai ba ammh wallahi tsab zan tumurmusheki anan wurin kuma in zauna lfy lau agidan Mijina, Kuma ki saurareni dak'yau, halinki ne ya jaza miki wannan cin amanar, Ke kowacce mace tana mafarkin samun miji kamar naki ammh ke Allah ya baki salihin mutum mai tsoron Allah, Sai ke kuma kikai amfani da hakan kina muzguna masa? Bashi da iko da gidansa sai yadda kikai? Babu wata muryar da yake tsoro da shakka face naki? To wallahi ki sani da'ace ayau bani da aure ne to Kinji nace Allah mijinki zan aura, zan shawo kansa kuma dole ya saurareni don kowacce mace da salon nata kissar, balle ma idan yaga ina masa abunda ke baki masa shi, kin san Zuciya nason mai faranta mata, ke mahaukaci kankat kenan yana kaunar mai faranta masa balle mai hankali, Hajiya Sa'a kiyi kuka da kanki ba dani ba don iya allonki ne yaja miki Faruwar hakan." Kuka sosai Hajiya Sa'a ke rerawa don ta kasa Furta komai kuma, Hajiya Aisha ta gama kashe mata jiki, Kama baki Hajiya Aishar tayi tana Fadin"Ai baki ma soma kukan ba, nan gaba kadan zakiyi wanda yafi wannan, kuma ki saurareni dak'yau, ga 'yata nan amana, Ku Zauna lfy ke da ita don wallahi kika sake naji ance ko ciwon kai kin sakata Allah saina lahira ya fiki jindadi, don kwarai zan cire kunyar Surukuta da amintar dake tsakaninmu musa wando kafa daya dani dake, Sabida haka ki kiyaye sannan Kuma akyalesu su sha amarcinsu Cikin kwanciyar hankali, don wallahi Hajiya Sa'a tashin hankalinsu kema tashin hankalinki, Tun wuri ki iya takunki don karki ce ban fada miki ba, Suhaila ita kadai ce 'yar da Allah ya bani sabida haka zan iya yin komai akanta, Ki huta lfy."
Vous aimerez aussi
Slide 1 of 10
NADIYA! cover
NANA AMINATU 2022 cover
MATAR SADAM  cover
 AFRA  cover
HAIRAN🔥💥♥️ cover
NANATOOU (DIYAR KAKA) cover
KAISI TERI KHUDGARZI 💔💔 cover
SAWUN GIWA...!🐘 cover
SIRRIN MU cover
KAUTHAR!!  cover

NADIYA!

8 chapitres Terminé

'Ta dan juya kanta cike da mamaki, tace, "Daddynka kuma? wanene shi?" Yace, "Habib Abdullahi Makama?!" cikin sigar tambaya. Jin sunanshi kadai ma sai daya sanya taji bugun zuciyarta ya canza. A duka kwanakin da suka wuce tun bayan daya ajiyeta a kofar gidansu ya wuce, karya take yi tace babu wata rana da zata fito ta koma ga mahaliccinta bata tunano wannan mutumin ba. Abin har ya kusa zame mata jiki, yin tunaninshi a lokacin da taje yin kwanciya barci. Wasu dararen kuwa har da mafarkinshi da tunanin wannan daddadan kamshi nashi, wanda ta lalubo turaren da yake amfani dashi cikin wadanda ya bata, itama ta mayar dashi nata turaren. Yaudarar kanta take, da take cewa wai tuni ta manta da sha'aninshi da kurar data kwasoshi. Ita tasan karya take yiwa kanta. Duk kuma yadda taso abinda ke tukarta a zuciya kada ya bayyana, sai daya bayyana din. Ta rasa fara'ar kirkirowa tayi koda ta yake ce kuwa, haka bugun zuciyarta ya ki saisaituwa duk yadda taso ta saisaita shi kuwa. Ta daure dai da kyar tace, "ok, na ganeshi. Yana ina yanzu?" Ya dan daga kafada, "ban sani ba nima. Kawai dai yace in zauna a wajenki zai dawo ya daukeni." Ita abin ma sai ya girmame mata, mamaki ya hanata motsi. To ita kuma a su wa? Kuma da wane dalili? Da zai dauko danshi ya kai mata?..." To domin sanin dalilin, don me, kuma me yasa? Sai ku biyoni Ni Jeeddah Lawals tare da Nadiya a wannan tafiyar tamu.