GUMBAR DUTSE

GUMBAR DUTSE

  • WpView
    Reads 2,237
  • WpVote
    Votes 79
  • WpPart
    Parts 8
WpMetadataReadOngoing1h 37m
WpMetadataNoticeLast published Tue, Dec 30, 2025
"Haka nake yawo, bana saka talkami." Ahankali, Jawad ya durkusa, guiyoyinsa suka baje kasa. Ya kai hannunsa ya rike kafar Batula, sannan ya dago idanunsa cikin natsuwa kamar mai rokon afuwa ya kalleta. Ganin za ta zame yasa ta rike kofar. Ya sunkuyar da kansa ya sumbaci tafin kafarta a gaban kowa. Batula ta bude idanunta da suka cika da razana, zuciyarta na dukan kirjinta tamkar gangar yaki. Tsoro da kunya suka hadu. Jawad ya sauke kafar, ya kama hannunta tamkar wanda ya yi nasara a yaki, ya ja ta cikin falon ba tare da jin kunya ba, daman fargaba da tsoro ba halinsa ba ne. Sai falon ya dauki shiru. Ko amo na numfashi babu, kowa ya kasa motsi. Idanuwa suka manne kansu tsabar mamaki, duniyarsu ta tsaya cak tana jiran abin da zai biyo baya. *** *** *** Mafi yawanci saba ji da ganin mace sai ta yi hawaye kafin ta samu farin ciki. Amma "Gumbar Dutse" Zai nuna muku wata hanya dabam inda soyayya ta zama ruwan sanyi, aure ya zama gata, kuma mace ta sami damar rayuwa cikin aminci da kauna har sau biyu a rayuwarta. Duniya ta yi ma Nasreen dadi. Ko kun san akwai mazan da basa juyawa mace baya, akwai masu rikon Amana gina rayuwar iyalinsu? Soyayya ba wai mafarki ba ce gaskiya ce idan aka hadu da nagari. Labarin Batula, Nasreen, Jawad, da kuma Zayyan.
All Rights Reserved
Join the largest storytelling communityGet personalized story recommendations, save your favourites to your library, and comment and vote to grow your community.
Illustration

You may also like

  • GADAR ZARE
  • KUSKURE
  • Dr Azeema
  • MIJIN TSOHUWA
  • RAYUWAR BADIYYA ✅
  • THE NEMESIS OF SAKINAH...KADDARAR SAKINAH✅
  • Kaine Rayuwata😭��❤❤ Complete
  • MATAR SADAM
  • Tu woh chaand
  • ISMUHA ZAINAB Completed

A firgice ya mik'e daga inda yake zaune, yana kallon sauran abokanan nasa fuska cike da hawaye idonsa yayi ja sosai Buga kansa ya fara yi ajikin bango yana ihu yana cewa " sun kashe min kowa bani da kowa yanzu, zaman dirshan yayi a k'asa, yana ihu yana yarfa hannunsa, zumbur ya mik'e ya nufi fridge ya d'auko robar ruwa ya bulbulawa kansa "Akan ido na suka k'one gidan mu, mahaifiya ta, mahaifi na, k'anne na duk suka mutu akan kunne na ina jiyo ihun su *************** "Cikin waye wannan a jikin ki? uban waye yayi miki ciki? bazaki fad'a ba saina kashe ki, wayyo na shiga uku duk irin tarbiyyar dana baki abinda zaki saka man dashi kenan, cikin kuka tace " wallahi Aunty ban sani ba, idan za'a kashe ni ban san wanda yayi min cikin nan ba, nima ganin shi kawai nayi ajiki na, tafiya tayi ta bud'e durowa ta d'auko Qur'an ta d'ora akan ta tace " na rantse da wanda raina ke hannunsa bansan wanda yayi min ciki nan ba. Kanta tayo gadan-gadan tana nizaki rainawa hankali, ta shak'e ta idonta suka kakkafe ************** A cikin gidan yarin yake ihu yana kuka yace " sunci Amana ta, sunyi min butulci, na yarda dasu amma sun ci min amana sun had'a min GADAR ZARE Amintattu nane suka yi silar zuwa na gidan yarin, sun raba ni da kowa nawa sun raba ni farin cikina,cikin matsanancin kuka yace " wallahi koda zan rasa komai na rayuwata bazan kyale su ba. Sun mun sharri, sun had'a man makirci da GADAR ZARE ************* "Koken a cikin kayana kuma, kafin ya k'ara sa maganar dubbun police sun kewaye shi da bindugogi, Ana cikin haka wayarsa ta fara ringing, dakyar ya samu ikon d'agawa, ji yayi muryarsa ta tintsere da dariya yace " nine, d'an uwanka, kaga yadda nayi wasa da hankalinka ko, na nuna maka halin 'yan Adam Cikin rawar murya yace " mai yasa kaci amanata? " saboda ina santa, ita rayuwa tace kuma mallakina , Wani irin mahaucin ihu ya saki tare da buga wayar da k'asa .

More details
WpActionLinkContent Guidelines