GUMBAR DUTSE

GUMBAR DUTSE

  • WpView
    Reads 2,175
  • WpVote
    Votes 79
  • WpPart
    Parts 8
WpMetadataReadOngoing1h 37m
WpMetadataNoticeLast published Tue, Dec 30, 2025
"Haka nake yawo, bana saka talkami." Ahankali, Jawad ya durkusa, guiyoyinsa suka baje kasa. Ya kai hannunsa ya rike kafar Batula, sannan ya dago idanunsa cikin natsuwa kamar mai rokon afuwa ya kalleta. Ganin za ta zame yasa ta rike kofar. Ya sunkuyar da kansa ya sumbaci tafin kafarta a gaban kowa. Batula ta bude idanunta da suka cika da razana, zuciyarta na dukan kirjinta tamkar gangar yaki. Tsoro da kunya suka hadu. Jawad ya sauke kafar, ya kama hannunta tamkar wanda ya yi nasara a yaki, ya ja ta cikin falon ba tare da jin kunya ba, daman fargaba da tsoro ba halinsa ba ne. Sai falon ya dauki shiru. Ko amo na numfashi babu, kowa ya kasa motsi. Idanuwa suka manne kansu tsabar mamaki, duniyarsu ta tsaya cak tana jiran abin da zai biyo baya. *** *** *** Mafi yawanci saba ji da ganin mace sai ta yi hawaye kafin ta samu farin ciki. Amma "Gumbar Dutse" Zai nuna muku wata hanya dabam inda soyayya ta zama ruwan sanyi, aure ya zama gata, kuma mace ta sami damar rayuwa cikin aminci da kauna har sau biyu a rayuwarta. Duniya ta yi ma Nasreen dadi. Ko kun san akwai mazan da basa juyawa mace baya, akwai masu rikon Amana gina rayuwar iyalinsu? Soyayya ba wai mafarki ba ce gaskiya ce idan aka hadu da nagari. Labarin Batula, Nasreen, Jawad, da kuma Zayyan.
All Rights Reserved
#979
marriage
WpChevronRight
Join the largest storytelling communityGet personalized story recommendations, save your favourites to your library, and comment and vote to grow your community.
Illustration

You may also like

  • NANATOOU (DIYAR KAKA)
  • KWARKWARAR SARKI MATAR YARIMA CE
  • ISMUHA ZAINAB Completed
  • Dr Azeema
  • Saat Takdir Memilih [C]
  • Chaar Saaye Mohabbat Ke 💫
  • KUSKURE
  • THE NEMESIS OF SAKINAH...KADDARAR SAKINAH✅
  • Kaine Rayuwata😭❤❤ Complete
  • BAKAR WASIKA

Labari ne akan wata Yar kauye da aka sangarta ta, Duk kauyen su ta addabi kowa ba mai iya tsawata mata, tun daga yara, matasa, yan mata, tsoffi, hatta da sarkin garin duk ta addabe su........................ wani matshin saurayi da baze wuce shekara sha takwas ba ya ce"ya ana miki magana kin miyar da mutane yan iska". kallan Shi tayi Sama da kasa tana gyara dan kwalin ta sai wani murgude murgude take ta ce"ba yan iska ba karuwai da kwartaye na mai da ku ko kuma ka ce yan goguwa ta fada tana murgude baki tare da hararar shi". Keh ni za kiwa rashin kunya, ganin yanda ya harzuka yasa ta ja da baya tana shirin ko ta kwana, dan ubanki ni zaki zaga, ja da baya ta yi ta tattare zanin ta ta ce" ba dai ubana ba sai dai ubanka mln salisu mai wankin hula". Toh wallahi ubanki zan ci idan na kama ki, sai na karya kasusuwan ki dan duk dangin ku ba sa'a na. Wani wawan birki ta ja har tana kokarin faduwa ta ce"kaiiiiiiii! Amman kai mugun makaryaci ne, tsabar raini da rashin ta ido ni zaka kalla kace min duk dangin mu ba sa'an ka, toh ina ka aje aboki balle kuma yaya mugu ehhhhhh!, ko dai abinda ka ke sha ne ya fara dagula maka lissafi, kun san ku samarin zamanin nan ba a raba ku da aaaa, ta fada tana gwada mishi yanda ake shan taba". Iya kuluwa ya kulu ya dade yana jin irin rashin mutunci da takewa mutane, abin yau yazo kan shi, dutsen dake kusa da shi ya raruma zai Jefe ta da shi tsohon dake tsaye yana kallon su ya ce"kul dan nan kar ka kuskura", bata ko san suna yi ba dan tuni ta yi gaba............................ Mu haɗu da ku a cikin labarin..... Started Fri sep/12/2025 Finish................

More details
WpActionLinkContent Guidelines