BAHAGON TUNANI

BAHAGON TUNANI

  • WpView
    Reads 396
  • WpVote
    Votes 7
  • WpPart
    Parts 19
WpMetadataReadOngoing4h 36m
WpMetadataNoticeLast published Wed, Jan 28, 2026
_Ta ya kishiyar da ta shuka sharri ta yi tunanin girbar alkhairi_ _Ta ya kishiyar da ta tarwatsa farincikin abokiyar zamanta ta yi tunanin kwanciyar hankali zai aureta_ _HAFIZA natsattsiyar yarinya, mahaddaciyar Al'qur'ani da ta taso cikin kaɗaicin yayyenta uku da suke hannun kishiyar mahaifiyarsu,tana gana musu azaba sakamakon hatsabibiyar mallakar da ta yi ma Ubansu. Wani gigitaccen al'amari ya tilasta HAFIZA komawa wurin kishiyar mahaifiyarta sakamakon bangon da take kallo a matsayin majigini ya rushe. Kishiyar mahaifiyarta ta ci gaba ta soya musu tsakuwa a hannu yayin da ta keɓe yaranta tana shayar da su ruwan zuma. Sau biyu kishiyar mahaifiyarta na zama silar fasawan auranta ganin za ta fi yaranta jin daɗin gidan miji. Sai dai Ubangiji ya yi ikonsa,domin ta yi dacen miji ɗaya tamkar dubu wanda ya doke na sauran mazajen 'yan'uwanta,ya yi musu fintinkau a komai._ _A tunanin HAFIZA ta yada ƙwallon mangoro ta huta da ƙuda,sai dai bata sani ba tirka-tirkar da ke cin gidan auranta ya linka wanda ta baro a gidansu sau dubu. Bahagon gida ne mai cike da chakwakiya kala-kala masu matuƙar yawa da ban tsoro. Sai dai faɗin hausawa da suka ce WUYA BATA KISA. Silar zuwan HAFIZA gidan ɓoyayyun sirrikan da ke ɓoye sama da shekara ashirin da biyar sun bayyana a idon duniya. Kar na jaku da yawa🥰 ku biyo tsaftataccen alƙalamina don yi muku jagora zuwa duniyoyi biyun da tunaninku bai je ba🥰_
All Rights Reserved
Join the largest storytelling communityGet personalized story recommendations, save your favourites to your library, and comment and vote to grow your community.
Illustration

You may also like

  • BAYA DA ƘURA
  • KAUTHAR!!
  • 🌸RAYUWAR MU A YAU🌸
  • 💤A MAFARKI NASANTA💤( I know her in my dream )
  • NANA AMINATU 2022
  • SAWUN GIWA...!🐘
  • Kaine Rayuwata😭❤❤ Complete
  • KAICO NAH
  • NANATOOU (DIYAR KAKA)
  • FATU A BIRNI (Complete)

Tashi ya yi a sanyaye ya fita ya daga falon, dan zama a ciki zai iya saka sa hauka na wucin gadi. Mota ya shiga ya fita daga gidan a guje. Sai da ya yi nisa ya tsaya a kan hanya, ya kifa kansa a kan steering motar cikin tashin hankali da tsoro mai yawa. Zuciyarsa bugawa take yi sosai, ji yake kamar ya yi hauka, tunaninsa yana ga abinda Abba ya faɗa masa. Da gaske dai matarsa Manal ƙanwarsa ce ta jini ko wasa ake masa? In hakan ya tabbata ya zai yi? In hakan ya tabbata me zai faru, wanne hali zai shiga? In hakan ya faru ya zai yi da ransa?. Allah ya sani yana matuƙar qaunar Manal, yana kallon ta matsayin abokiyar rayuwarsa kuma bugun zuciyarsa, kallon matarsa ma'ajin sirrinsa yake mata, kallon Manal yake a matsayin uwar yaronsa da yake cikin ta. Ta ya rana tsaka ake so a juyata ta koma ƙanwarsa wacce suke uba ɗaya? In hakan ya faru da wanne ido zai iya kallon ta matsayin ƙanwarsa da suke jini ɗaya? Ya matsayin ɗansa da yake cikin ta? Ɗansa ne ko ɗan ƙanwarsa?.

More details
WpActionLinkContent Guidelines