SalmaAhmadIsah
Aure! A 'yan kananan shekarun a take da su duniya, wanda basu wuce goma sha tara (19) ba, idan aka tambayeta menene aure? Za ta ce wata tarraya ce ta mutane guda biyu, bautar Allah shi ne kasudin wannan tarayya, zama ne da an an lokacin da a fara shi, amma sanin ranar da zai kare babu wanda ya sani, ta sani da cewa zaman aure ya gaji kalubale iri-iri. Za ta iya cewa gidan aure tamkar jami'a ce, kowa a fannin da yake karanta, dan haja jarrabawar ko wani fanninta banbanta da ta wani fannin. Ta kuma tabbatar da cewar duk yadda wasu suka kai ga fuskantar kalubale a rayuwar aurensu, wasu suna cikin farin ciki a nasu auren. Sannan akwai wani abu da ta yi imani da shi kan aure, cewar Aure kan sauya mutum!
A ɗan ƙaramin hankalin da take da shi, wannan ce ma'anar da ta bawa aure, shin da gaske haka auren yake? Ko ko kallon biri takewa rogo? Shin ita ma nata auren zai kasance cikin masu sa'a? Koko akasin haka ce za ta faru da ita? Duk da waɗannan tarin tambayoyin da suka cika kanta, irin wanda 'yan mata da yawa kan yi gabbanin aurensu, hankali kwance, sannan cike da zumuɗi Rahama take shirin aurenta.