🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽
👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽
👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽
SUN GUJE NI (SANADIN CUTAR LAKKA)👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽
👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽
👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽
👨🏻‍🦽👨🏻‍🦽
👨🏻‍🦽
(IT BASED ON TRUE LIFE STORY).

LABARI DA RUBUTAWA:FARIDAT HUSAIN MSHELIA(UMMU-JIDDAH).

GODIYA.
Ina mai farawa da sunan Allah mai rahama mai jinƙai ,ubangiji buwayi gagara misali sarkin da baya bacci kuma gyangyaɗi bai taɓa kama shi ba,miliyoyin salati su ƙara ninkuwa ga masoyin raina Muhammadur-Rasulullahi(SAW)da iyalan sa tsarkaka da sahabban sa zaɓaɓɓun Allah.
Ina godiya ga Allah da ya bani ikon fara rubutun wannan littafin mai albarka,ina kuma roƙon sa da ya bani ikon rubuta daidai ya sa rubutun nan da zan yi ya zamto silar janyo hankalin wannan al'umma ta mu dangane da masu fama da irin wannan lalurar ta CUTAR LAKKA(SPINAL CORD INJURY)musamman manyan ma su kuɗi,gawurtattun ƴan siyasa,masu faɗa aji tare da kai musu ɗauki na gaggawa domin jinya ce mai buƙatar kulawa ta musamman dan haka ya na ga yakamata in farkar da ma su da shi domin su din ga biyar jaridu,talabejin,kafafen sada zumunta domin bada ta su gudummawar, yanda na fara lafiya ina roƙon Allah ya bani ikon kammalashi cikin ƙoshin lafiya alfarman Annabin rahma.

SADAUKARWA.
Na sadaukar da wannan littafin ga ma su CUTAR LAKKA(SPINAL CORD INJURY)na duniya gabakiɗaya.

SHAFI NA ƊAYA.

SHIMFIƊA.

Ina kuɗi na da na ajiye cikin dirowar nan?ya tambaye ta cike da zargi da tsana dan har ga Allah shi kam ya fara gajiya da halin Amaryan nan ta sa wacce ke ƙwamushe ma sa ƴan kuɗaɗe a duk lokacin da ya je ya yi sana'ar sa ya dawo gida,

ganin sai wani soshe-soshen munafurci ta ke yi ya sa ya ƙara jeho ma ta wata tambayar"Ba tambayar ki na ke ba?",

ta yi wuri-wuri da ido dan har ga Allah ba ta san ya san ta na ƙwamushe masa ƴan kuɗaɗe ba a duk lokacin da ya ajiye tun da kuɗaɗen da ya ke ajiye wa suna da yawa kuma satar na masu wayau da dabara ta ke yi in da ta ke ɗiɓan wani bangare daga cikin kuɗin ta bar mi shi wani sashen da ya fi ya wa dan haka ta tattaro sauran ɗan ƙarfin gwiywar da ta ke da shi ta ce"Haba Yusuf,haba Assidiƙ kawai dan na kasance matar cushe a gareka shiyasa ka ke ƙala min duk abin da ka yi niyya?",

"Menene laifi na dan na zaɓe ka a matsayin mijin aure bayan nagarta da tarbiyar ka nagani ya sa na zaɓe ka acikin duk manema na?"

"menene laifi na dan Allah anan da ka tsane ni, zagin safe daban na rana daban na dare daban?ga shi yanzu har ka fara ɗaura min sata"

"Ni Yusuf za ka ce ƙira ɓarauniya?,ta nuna kan ta da yatsa tana mai fashe wa da wani irin kuka da ya taɓa zuciyar shi,

kasancewar shi mutum mai tausayi sam baya son ganin kukan mace macen ma kuma matar sa ta sunna amman fa zuciyar sa ya naƙalto masa" a gidan nan daga ita sai shi kuma da daddare ya ke dawowa ya ajiye kuɗin ba da rana ba balle ya ce ko masu zuwa gidan na su ganin amarya ne su ke ɗauka,da zaran ya dawo daga kasuwa ya ke ajiye kuɗin ya wayi gari ba bu wani sashi daga cikin su,to wani barawo ne zai shigo da daddare ya ɗau kuɗi kaɗan ya bar masu yawa in dai ba mafi kusanci da shi ba?,nan ta ke ya ce,

"zato zunubi an ce ko da ya zamto gaskiya dan ha ka cikin sanyin murya ya ce

"Shikenan ubangijin da ba ya bacci ya fi ni sanin wanda ya ke min wannan aika -aikar dan haka na bar mi shi hukunci a hannun sa",

Wata ɓoyayyar ajiyar zuciya Amarya Ra'isat ta yi tun da ta ji yace haka ta ta shi ta kakkaɓe zanin ta da datti ya canza mi shi kala daga shuɗi zuwa baƙi ta ce cike da tsiwa tamkar ba ita ce ta gama ihu da kururuwa yanzu-yanzun nan ba akan an ɗaura mata sata,

"oho dai ai Allah ba azzalumi ba ne yana kallon abinda ka ke aikata wa saboda ba ni ce zaɓin ran ka ba shiyasa ka ke mi ni haka"ganin yanda ya ke kallon ta sheƙeƙe ya sa ta ƙara ma rigar ta iska ta fice tana dariyar shaƙiyanci a zuciyar ta.
Madafa ta shige ta na mai cewa"wawan banza da wofi yo kai a tunanin ka daman ummana ta dage da a haɗa auren mu dan menene?,

"dan kawai ace ina auren mai kuɗi ko mai rufin asiri ma zance,shikenan in zauna kallon ruwa kwaɗo ya yi min ƙafa,in yi ta kallon sulalla ba tare da mun yagi rabon mu ba?"

"To kuwa gaskiya ka yi babban kuskure dan wallahi ban aure ka dan yin biyayya ba,na aure ka ne saboda abin hannun ka kuma dole in dinga adana wa saboda gudun ɓacin rana,ya zam ddole mu fantama tunda kai na lura irin maxan nan ne masu shegiyar baƙar rowa daga ka ajiye kayan abinci shikenan ba bu kai ba ba da kuɗi alhalin kuɗin a kwaisu to kuwa dole in ɗiba in adana mu yi bushashar mu ni da uwata"ta furta hakan ta na mai juya dafadukar shinkafa da waken da ta ke yi da ludayi tamkar mai tuƙa tuwo dan tuni shinkafar da ruwa ya mata yawa ga rashin wadataccen haɗi ga uban juyawar da ta ke samu ya chaɓe dan haka ya fara ƙauri yana ƙonewa ta ƙasa tun ruwan bai ida sa shanye wa ba,

hannu ta sa ta ɗebo shinkafar ta kai baka cikin jin zafi da ɗanɗanon kafi zabuwan da ya ratsa harshen ta ta ce "chakwai ne aradu" dan haka tuni ta kashe rishon wanda ke fesar da wani irin hayaƙi wanda ya ɓata ilahirin madafar ko'ina ya yi baƙi tamkar wacce ke amfani da itace,wata farar kula ta ɗakko ta manna ta da jikin tukunyar da ta yi baƙiƙƙirin ta fara ɗibo dafadukar tana sanya wa can ta ga wata curarriyar albasar da aka rabata gida 3 aka watsa a dahuwar ta dulmiya hannun ta da ya yi kaca-kaca da baƙi ta ciro ta tare da wurgawa bakin ta tana wani irin tsalle tana yarfe hannu saboda zafin da ta ji ya baƙunce ta lokaci guda cikin wani irin dariya ta ce"Aradun Allah ka shammace ni ai na ɗauka ɗan dunkule ne ma har ina ɓari ashe ma albasa ce"

Yuzarsib wanda takaici da damuwa ya sa ya ji ya gaji da zama ya biyota bakin madafar tsaye ya yi a kan ta ba tare da ta ma sani ba ya yi mata mugun kallo ya harare ta(ni kuwa na ce wannan ai shi ake kira da harara a duhu dan ba ta ma san kana yi ba)cikin wani mugun takaici ya ce, "ke fa na ke jira ina abincin?" ta nu na mishi kular da ke daɓe a cikin caɓalɓalin da ke ƙasan ta ce"ga shi nan ina zubo ma ka?

"Waaah ni ɗin nan?ya nu na kan shi da hannu "ai in kin ganni a lahira kai ni a ka yi wannan abincin na ki da bai da maraba da kumallo(Amai)ba da ni ba"dan haka ya hura ma rigar sa iska tare da ficewa daga gidan gabaɗaya zuciyar shi na mi shi wani irin ƙuna mara misaltuwa na da nan zuciyar shi ta bijiro ma sa da tambayar da ke ƙunshe a cikin ta"da man haka ake auren?"eh tabbas haka ake yi tunda ga shi na gani ganin idona"shagalalliyar zuciya ta ba shi amsa cike da zugar maƙiyin mu shaiɗan dan haka ya zauna ya yi ɗare-ɗare akan hakan amman sai wani amsa ya bijiro ma sa nan ta ke n"sam ba haka ake aure ba ha ka dai na ka ƙaddarar ta zo ma ka, ƙaddarar da ka rubuta da hannun ka tun kana cikin cikin mahaifiyar ka",

"shin haka ka ta so ka ga ana yi a gidan ku da har shaiɗaniyar zuciyar ka za ta kai ka ta baro?,

"Shin haka ka ga nagartacciyar mahaifiyar ka na aikace-aikacen gidan ta komai a ƙazance ,ashe ba kyakykyawar tarbiyan da ka samo daga gare ta ba ne na horo da nagartacciyar tsafta ya sa har ka ke banbance wa tsakamin fari da baƙi a rayuwar ka ba?",

"tabbas ka yi ma sunnar ma'aiki karan tsaye idan har ka ce haka auren ya ke, bayan mai tsira da aminci ya umurce mu da yin aure ne dan ƙara samun nutsuwa da kwanciyar hankali ta yanda zamu bauta ma ubangijin mu a tsanake cikin ƙanƙan da kai da nutsuwa amman meyasa ni na wa ya kasance haka?,

shaiɗaniyar zuciyar sa ta jeho ma sa tambaya akan amsoshin da nagartacciyar zuciyar da ta ke ƙoƙarin sai ta shi a hanyar ƙwarai,

"saboda ba ka yi da ce da macen ƙwarai ba,saboda ba ka bi matakan da Annabi ya yi umurni da abi ba dan samun mace ta gari,shiyasa ka ga kana fuskantar waɗannan matsalolin"

"to wacece mace tagari kuma wani mataki ake bi domin a samo ta?.

Amsoshin duka tambayoyin suna cikin alƙalamin Ummu-Jiddah wacce ta zage dantse dan zaƙulo ma ku hanyoyin da zamu ɓulle akan matsalolin mu na rayuwar yau da kullum amman fa sai kun agazo ta hanyar bi na da sharhi mai nagarta in ba haka ba in maida novel ɗin na kuɗi,

UMMU-JIDDA.

SUN GUJE NIOnde histórias criam vida. Descubra agora