1-5

8.5K 224 28
                                    

[7/7, 1:54 PM] Aishat Muhammad: ♦♦♦
              *SANGARTATTCE*♦♦♦

Maman Abd Shakur

1...
Free page

Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai.

"wayyo Allah na Baba mutuwa zanyi, wayyo Mama huramin cikin" mata biyune suka zagayeta akan tabarman dawasu yara mata guda biyu dake tsakar gidan dayasha simenti kal kal dashi duk sunyi zuru zuru, kana ganinsu kaga tashin hankali kwance akan fuskarsu, chan ta gefen tabarman  kuma wajajen inda kafanta yake wani dan tsohone haka dake sanye da babbar riga dakuma yar hula daya zagayeta da rawani irin na malamai dinan ya rike kofin silver yakara abaki yanata addu'o'i aciki anatse, ihu takara yi ta dage rigarta sama tabude daidai cikinta dake nan kaman bata tabacin abinci ba, ta gefen haggun cikin ya dan kumbura idan kaga wajen saika rantse wani irin babban kurjine yafito ya kumbura haka yay ruwa zai fashe, ihu tasake yi tariko hannayen matan dake kanta tace "wayyo Allah Mamammu na shiga uku, azaba Mama wayyo, azaba yakemin" tasaki hanunsu tana ihu "Baba Baba baba kiranka nakefa, wayyyo Allah na ba banu ni" wani irin ihu take ta rirrike hannayansu gam tana nishi, wajen ciwon cikin kuwa sai balbal yake yanda kasan halita mai rai ne acikin wurin, duk ihun ta yacika gidan, tsabagen takaici ma daya daga cikin matayen wacce itace mahaifiyarta taja tsaki, hakan yasa dayar ta goge zufan datake yi agoshi, takamo fuskarta da hanunta tarike tace "haba Balkisu, iye mai gadon zinare, ki daure mana baga baban kinan namiki addu'a aruwaba, kefa mai dauriya ce, jaruma, kinga Layla da Raiyana zasuce ke raguwa cefa gashima sai kallonki suke" girgiza kai tayi tawani irin kece da kuka da ihu harda shesheka tace "ni kukiramin Baaba wlh, Baaba tazo, Baaba kizo ki taimakeni" tafara shure kafa idanun nan sunyi jajir tace "Baba, Baba, Muji, wayyo Allah na Mujittapa kuzo kutaimake ni, Shato kuzu dan Allah na shiga uku, wayyo Mama dubamin kiga kodai barkewa cikin yakeyi ne?" tawani irin buga ihu hakan yasa mahaifiyarta dake kanta ta buge bakinta da karfi tace "kewai baki iya kiran sunan Allah bane banziya kawai" daidai lokacin Baba ya cire cup daga bakinshi ya kalli Uwargidan yace "dagomin ita Zainaba" dagota tayi ahankali sai wani uban nishi take tana cije baki tace "tsaya tsaya uhmm" tsayawa tayi tana kallonta cike da tausayi, hannu budurwan tasa akan kafadar matar tareda runtse ido da karfi tana nishi tace "tona shirya" har Mama saida tasa hannu suka dagota zaune ahankali wani irin ihu tayi kaman zata mutu "ya isa, ya isa, yayi" suka jinginar da ita ajikin bango, kafamata kofin Baba yay abaki ta kurbi ruwan sosai tasha tana kara dage rigar atampan jikin ta sama, ragowan ruwan Baba ya debo yay addu'a zai shafamata akan kullutun da sauri tarike hanunshi tana ihu tana kuka tace "Baba wlh azaba yakemin, in kanama Allah karka tabamin, kaji dan yarasulullahi" hanunta Mama dake kanta ta buge tana wurga mata wani mugun kallo, hakan yasa Baba ya girgiza kai ya shafamata ruwan awajen tana wani irin shegen ihu da duk yacika musu kunne, tashi Baba yay ya kalli mahaifiyarta ya mika mata cup din yace "bayan awa daya kikara bata Amina, bari nakoma zaure wajen dalibai" jiki asanyaye ta karba tace "to malam" juyawa yayi yay hanyar zaure bude kofa yayi sanan ya daga asabari dazai sadashi da zauren yafita, almajirai ne cike a zauren sunata karatu da alo, ga wasu manya akansu dake rike da bulala suna lura dasu, bangon zauren duk jakunkunan almajiran ne dakuma taburmai dasuke kwana akai dan zauren nada girma sosai, daliban na ganinshi suka kara karfin karatun dasuke, fita yayi daga zauren zuwa kofar gida nan ma wasu almajiran ne akan simentin kofar gidan dayawa sunata karatu da alo, anyi babbar runfa daya kare kofar gidan sabida koda ana ruwan sama dan wasu almajiran anan waje suke kwana, ga robobin almajiran cike akan dankali dan dazaran karfe biyu tayi zasu tsaya sai ayi salla kowa yatafi bara, daga chan gefen kofar gidan kuma lungu ne dayasa suka gineshi dajar kasa aka zagaye suka maida bayi, anan almajiran suke wanka suke dai komi nasu sanan a kofar gidan akwai rijiya da guga dasuke diban ruwa, zama yayi akan tabarma da aka wareshi musamman tashi ce dan akwai yar dadduma mai taushi akai ya zauna tareda yin bismilla yanajan chasbaha, yana bin kowani dalibin dake wurin yana karatu da kallo, wani dalibi babba dan yana daga cikin wayanda ke kula da sauran almajiran ne yazo kusa da malam ya zauna tareda tankawshe kafa yadan dukar dakai yace "Allah taimaki Malam, Allah gafarta ma Malam, Allah kare mana Malam" ahankali Baba ya ijiye charbin ya kalli yaron yace "sun biya karatun da kyau Isyaka?" "i sunbiya  Malam, na muhammadu ne kawai bai kawo da kyau ba amma nakara maimaita mai" murmushi Malam yayi tareda kishingida da bango yace "masha Allah to, daukomin Al Qur'ani na nabarshi a zaure saika biyamin naka inji" dan kallonshi matashin yayi saikuma ya sunkuyar da kai yace "Malam ya jikin Balkisun?" ajiyar zuciya Malam ya sauke yace "da sauki namata addu'a zata sami lpy nan bada jimawaba" cike da damuwa Isyaka yatashi yabar wajen zuwa zauren dan dauko abinda Malam ya aikeshi.

SANGARTATTCE Where stories live. Discover now