6 - 7

2.2K 134 2
                                    

*JARABTA*

Maman Abd Shakur

6&7...

Dawani irin mugun gudu ya tsallako titin bai damu da babban trailer dayama fadi ba, tsayawa yayi a akan dakalin tsakiyan titin ganin motoci kusan uku su bubbuge juna, waigawa yayi sanan yasake waigawa again dan baiga Eesha ba, ahankali yace "kodai taji tsoro ne ta koma gida?" hanunshi yaji anrike da sauri ya daga kai Yusuf yagani ya rikemai hannu gam, gasu Ibrahim tela da abokanayen shi yan wajen aiki da suka daura hannu aka suna kallon titin ganin yanda mutane harsun cika wajen suna ku matsa aciro ta tana numfashi, wani irin fuzge hanunshi yayi daga Yusuf ya shiga titin, mutane kawai yake turewa kaman zararre yana kutsawa cikin crowd din, Yusuf da abokanansu ne suka bishi da sauri ture mutanen yayi duka harsaida yakai dadai saitin wata bakar jeep, kasa yabi da kallo kaman zararre ganin jini nabin wajen, da sauri ya tsugunna ya leka kasan motar, hango Eesha yayi hakan yasa ya tashi da sauri kaman zararre yace "ku matsar da motar da sauri masu motocin suka shiga, ahankali aka mammatsar da motocin, tsugunna nawa yayi ya jawota ya daura kanta akan kirjinshi yana kallon fuskarta yama kasa magana, murmushi tamai jini nafito wa daga bakinta, kokarin yimai magana take amma takasa da sauri Yusuf ya tsugunna ya dafa kafadar Khaleel ahankali yace "Aisha kice La'ilaha illallah Muhammadur rasulullah" bakinta ne ke rawa haka Yusuf ya dinga maimaita mata harta karba, da kyar ta daga dayan hannunta da ledan agogon ta ke ciki ta daura akan hanun Khaleel, sanan hanunta yay lagwal.

"Abba Abba" kanin Eesha ne Ibrahim yazo da gudu da farin shaddan anko dinshi ajiki, Abba dake tare da abokanan aikin shi yace "lafiya Ibrahim" yana haki yace "Abba anyi hatsari sosai akan titi wlh" subhanallah Abba yafadi shida abokanan shine suka tashi dan zuwa dubawa, Karo sukaci da Babban Khaleel da wanshi suma zasu dubawa hakan yasa dukan su suka dunguma zuwa titin.

Salati gabaki dayan crowd din wajen suka dauka, kowa ya kasa motsi barinma mutumin daya bigeta wanda yake arne yaci suit jikin shi yay mugun sanyi, ahankali Yusuf yakai hannu ya rufemata idanu, Khaleel ya kalla dayaga kallonta yake kaman zai cinyeta yace "Khaleel Khaleel" ko kallon shi Khaleel baiyiba har lokacin yana tsugunne da ita akirjinshi. Tashi tsaye yayi idanunshi sun xhanza launi, hango su Abba yayi kana ganinsu kaga tashin hankali karara akan fuskokin su, ahankali suka tako zuwa wajen tsugunnawa baban Eesha yayi ya kalleta shiru yayi yana addu'a sanan ya kalli Khaleel yace "Khaleel" ko dago kai Khaleel baiyi ba har lokacin fuskar ta yake kallo yay shiru da sauri Ibrahim tela ya koma shago ya dauko wata katuwar tabarman shi dayake yanka dinki akai, karaso wa yayi yamika ma Baban Khaleel ya karba, zuwa wajen yayi ya warware, ahankali baban Eesha ya mika hannu zai karbe ta wani irin ihu yayi yasake riketa yace "karku tabamin matata, bacci take" dariya yayi ya kalli fuskar ta yace "My Eesha sleep kinji idan kin tashi saimutafi, kitashi kafin karfe daya fa dan lokacin zaa daura mana aure" Ahankali baban Khaleel yake furta "innillahi wa innailaihi raji'un" ahankali yace "Son saketa zamu kaita gida amata sutura" ko kallon mahaifin nashi baiyi ba, hakama Baffan shi Abba babu wanda ya kalla cikin su, Yusuf ne da abokanansu su kusan takwas suka rirrike shi da kyar aka dauketa akai gida da ita, Khaleel kam ahaka abokan shi da Yusuf suka rirrike shi yana maganganu dako gane meyake fadi basayi suka taho kofar gidan su Eeshan dashi.

Ance kowani rai mamaci ne, mutuwa bata baka notice, once lokaci yayi you just have to go, mu kusanci Allah mu nisanci zunubai, muyawaita istigifari bamusan kozamuga gobe ba.

Babu wanda ya yarda Eesha bata, Mama gani take ya'ta da yanzun nan tazo tacemin zata fita dama ajali ke kiranta?? Khadija kam kasa magana tayi kuka kawai take, su Ihsan dasu Faiza da kanin Eesha bansan wama ke lallasan wani ba, Maman Khaleel da Umma da Mujiba ma duk zuwa gidan su Eesha sukayi.
Ko alwala ma yima Khaleel akayi sosai yafita hayyacin shi hanunshi damke da ledan da Eesha tabashi yana wasu irin surutai, haka aka mata Salla aka kaita, aka dawo shikenan fa duniyan.
Yauce Rana uku da rasuwan Eesha, babu wanda zaiga Khaleel dabazai yi kuka ba, koka zo gaisuwa bakai niyyar kuka ba shiza kagani kai kuka, ko abinci yakici, ruwama saidai abashi wanda ya shiga ya shiga sauran su zube akasa dan baya zukan ruwan da kanshi, ko wanka yakiyi balle ma wani abun, bayama kowa magana saidai yay ta maganganu shi kadai, addu'a ake mai bana wasaba amma har lokacin ba chanji, Maman Eesha duk idan ta kallai saitai mai kuka, Ammin shi kam baa cewa komai.
Misalin 1:25 na dare kowa na dakin shi, karan fashe fashen abubuwa ne yasa kowa ya mike daga kan gado dan dama bawani baccin kirki kowa keyiba, afrigice Yusuf ya farka gefen shi ya duba ganin babu Khaleel dake kusa dashi yasa yay jumping daga kan gado yafito daga dakin, cin Karo yayi da Abban shi da Umma, Abban shi zaiyi magana saiga Daddy da Ammi sun fito, su Ihsan ma haka atare suka dunguma suka sauka kasa kitchen sukayi dan nan sukejin karan. Shiga sukayi da sauri Khaleel suka gani dauke da tabarya a hannu yana faffasa koma me hanunshi yakai yana ihu yana magana "ba Kaine bakin jeep dinba Kaine my Eesha ke karkashin ka, ku ku 5 ne" tawarwatsa kwanuka kawai yakeyi, ko kallon su Abba dake kiranshi baiyiba, Yusuf ne ya fizge tabaryan ya ijiye hakan yasa ya ture Yusuf, da sauri Ammi ta juya ta koma falo danji tayi wani mugun kuka yazo mata, Ihsan ma fita tayi da sauri jikin Ammi tafada sai kuka da kyar Umma ta lallashe su, wani irin murmushi Mujiba tayi mai wuyar fassara kafin ta dawo falon ta zauna. Baban Eesha Abba yakira dan babban likita ne shi, within 2min ya iso, da kyar su hudun suka iya kama Khaleel dubashi baban Eesha yayi kafin yamai alluran bacci, nan bacci yay gaba dashi akan dogon kujera.
Ajiyar zuciya Abban Eesha yayi kafin ya kalli Abba yace "I think Khaleel yay developing mental issues".

JARABTA Where stories live. Discover now