2

1.6K 14 1
                                    

*DANDANON WASU DAGA ZAFAFA BIYAR*

*CIKIN LITTAFIN*

🧣🧣 *DAURIN BOYE* 🧣🧣

         *NA*

*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*

HASKE WRITERS ASSO

(home of expert and perfect writers)✍




        0⃣1⃣

      Sake gyara tsaiwarshi yayi jikin machine din nasa samfurin lifan kirar MOTO B,agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa ya kalla yana sake qiyasta mintocin daya kashe tsaye a qofar gidan,tabbas banda wani babban dalili babu abinda zaya sanyashi zaman jira har kamar haka,babu abinda ya tsana a rayuwarshi kaman jira,mutum ne shi mai kiyaye qa'ida wanda bai yarda da samfurin wannan maganar da hausawa ke bawa lokaci ba na african time.

      Sauke hannun nashi yayi ya maida dubansa ga madaidaicin get din dake maqale da katangar gaban gidan wanda ya kasance shine kofar da zai sadaka da ainihin cikin gidan,kaman jiran hakan kuwa ake qofar ta soma yunkurin budewa,cikin sakannin kadan matashiyar dake yunqurin bude qofar ta bayyana.

     A hankali take takowa zuwa inda yake,sanye cikin dinkin atamfa riga fitted da skert wanda ya zaunawa jikinta das,ta lullube jikinta da mayafi wanda baikai matsayin medium ba,a hankali yayi kokarin mamaye fuskarshi da murmushi duk da yadda fuskarta take kadaran kadaham hakan bai dameshi ba duk da yana ankare,ba fara'a sannan ba kuma a daure take can ba,kallo take kare masa tun daga nesa kaman yadda ta saba masa duk sa'ilin da ya ziyarceta,shirt ce jikinsa ruwan makuba da bakin wando jeans mai matsakaicin kudi,kafafunsa saye da takalmi budadde dinkin hannu na kasuwar kofar wambai,fes yake hakanan kayan sun masa kyau babu laifi,sumarshi kanshi zuwa sajensa a gyare a taje wanda hakan ya sake bayyana sirrin kyan da Allah ya bashi,ba shakka banda wani abu guda tak muhammad ya cika mijin aure wanda za'a iya nuna shi a ko ina,saidai wannan abun daya rasa din ya sanya ta cireshi daga tsarin mutumin daya cancanci aurenta.

"Barka da fitowa gimbiya zulaiha" ya fada cikin sassanyar muryarsa wadda na daya daga cikin abinda ke burge zulaihan tare da shi,duk da bata jin zata iya bashi damar kasancewa cikin rayuwarta,yana ci gaba da nazarin yanayin fuskarta a fakaice sanda ta amsa masa
"Barkan ka" ta fada cikin wani salon shan qamshi da basarwa
"Har na fidda rai ai,na tsammaci yau bazan samu ganinki ba"
"Kusan da hakan ce ta kusa faruwa,saboda zamu fita ne da maama,sannan ma kuma bansan zaka zo din ba,yanzun ma zuwa nayi na gaya maka.....don Allah ya kamata ace duk sanda zaka zo ka fara sanarmin tukunna kafin kazo din"ta fada kanta tsaye tana yamutsa fuska murmushi ya saki gami da dan duqar da kanshi qasa yana wasa da duwatsun dake shimfide a qofar gidan,baice komai ba sai murmushin da yaci gaba da fitarwa yana tattaunawa shi da zuciyarsa,tabbas yasan wannan rana na nan tafe,fiye da haka kuma na nan zuwa nan gaba kadan,wannan ba baqon lamari bane a gareshi,zulaiha ba itace mace ta farko da makamancin hakan ta faru tsakaninsu ba,saidai bazai yanke mata hanzari ba,zai jirata har zuwa ranar da zai zata furta kota yanke alaqar dake tsakaninsu da bakinta,sai bayan daya kammala wannan tunanin sannan ya dago ya dubeta
"Shikenan....babu damuwa...kiyi hakuri" ba tare data tanka ba ta juya tana niyyar komawa cikin gidan nasu
"Ki gaida maaman idan kin shiga"
"Zata ji" ta fada gami da jan qaramin tsaki can qasa ta shige gidan gami da rufe qofar gidan garam.

      Kai ya girgiza bayan shigewarta cikin gidan yana sakin murmushi tare da cije lebansa na qasa,cikin qwarewa ya haye saman babur din bayan ya tadashi ya figeshi cikin gudu ya fice daga layin,zuciyarsa cike fal da tunani da mamaki,mamakin da har yau yaqi barinsa,tsahon shekaru kenan wannan abu na daure masa kai,da gaske haka rayuwa ta koma?,ya gode Allah da baiyi gaggawar yiwa hukunci wa rayuwarsa ba.

ZAFAFA BIYAR (DANDANO)Where stories live. Discover now