👠👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝
👠👠👠👠
👝👝👝👝
👠👠👠🦚🦚🦚🦚🦚🦚
🦚🦚🦚🦚🦚
🦚🦚🦚🦚
🦚🦚🦚💄💄💄💄
💅💅💅
💄💄💄💄💅 *HALEEMATUS* *SADEEYA* 💅💄
Written by *HUSBA'AHFAMA*
IG **officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real* *husba'ahfama*Follow me on Wattpad @ *Real* *husba'ahfama*
*Bismillahir* *Rahamanir* *Rahim*
44-45
Bayan tafiyar malika da kwana uku sadiya takoma gidanta tare da ya'yanta ummice ta rakata tare da shatara ta arziki gyara kuwa sadiya ta,shashi ko amarya se dai haka Sadiya tayi mamakin gyaran da aliyu yayiwa gidan nasu yadada kyau aliyu besan sadiya ranar zata dawoba Amma Yana gari yaje kaffaninsane Dan daga ummi har abbah Basu Gaya Masa sadiya zata dawo ranar Dan haka yai ficewarshi danshi fishi yake da su ummi sunki bashi matarsa sadiya ma fishi yake da ita gani yake itama tanasan Zama wajan ummi Dan haka batacewa ummi tanaso takoma gidaba har ummi tatafi gida aliyu be dawoba
Ranar ummi taga gidanta yadada Mata girma su sadiya sun koma
Se dare aliyu yadawo lokacin sadiya Tasha gayu ta gyara yan biyunta da su Amira gawani kamshi dake tashi agidan da jikinta girki lfyaiye ta shirya Masa agajiye yashigo falan da sallama bakinsa bakowa se kamshi dake tashi gani yayi falan yadada kyau gidanma tsaf dashi mamakine yakamashi to waye yai wannan gyaran kalle kalle yafara bega kowaba Kan kujera yazauna yajingina yadafe Kai da hannu biyu yai shuru kamar me tinani du kansu suna labe abayan labule du suna kallansa lokacin da yashigo tausayi yabawa sadiya Tai musu alama da hannu da sufito gaba dayansu ahankali suka fito suka hada Baki atare sukace oyoyo daddy azabure yabude Ido Yana kallansu kamar amafarki gani yayi gaba daya sun canza Masa musamman sadiya da Yan biyunta da sauri suka karasa gabanshi suka rungumeshi suna dariya shima dariyar yake yarungumesu yayi Daya bayan Daya yasumbacesu sannan yakarbi su Areef Ido yakurawa sadiya Yana murmushi itama murmushin take
yace yaushe kuka dawo Babu sanarwa abinma Yar shammataceko
Tace eh Mana bafashi kake da muba yazamuyu mu gaya maka taturo Baki
Murmushi yayi yace ai tinda kundawo nahuce Kuma kun min bazata sannunku da zuwa yau Ina cikin farinciki iyalina sun dawo yau zanji dadin gidan wlh har fargabar dawowa nake saboda kadaici ngdwa ummi da tabani iyalina kallan su Areef yayi me mommy da ummi suke baku haka kuka girma
Dariya tayi tace muje na hadama ruwan wanka ko
Yace to Allah sarki Ni aliyu bawan Allah yau nine nasamu gata za ahadamin ruwan wanka wlh nayi kewarku haskena
Tace Nima haka masoyina mijina
Gaba tayi yabita abaya su Amira zamansu sukayi afalo suna kallo suna shiga yakwantar da su Areef Akan gadansu da yasa musu mekyau adakinsa yahau cire Kaya lokacin da sadiya tafito daga bandaki Yana tsaye yakurawa yanbiyu Ido Yana murmushi yanawa Allah godiya
Rungumeshi sadiya tayi tabaya Tace abban Walid nagama hada maka kaje Kai wanka
langabar da Kai yayi kamar Karamin yaro yace Ni kece zakiyi min nagaji yakarasa wajanta yarungumeta atare suka sauke numfashi
Dakyar ta lanlabashi tasamu yashiga wanka tafito Masa da Kayan da zesa marasa nauyi Yana fitowa ta temaka Masa yashirya suna tahira cikin nishadi atare suka fito daga dakin aliyu har inda tajera Masa abinci tazuba Masa yanaci yana Santi dariya sadiya take ta masa yanasa Mata Albarka tanajin dadi jinshi yake cikin farinciki du kansu suna falo suna tahira se kallan sadiya yake ko Yaya ta motsa idansa na kanta da sun hada Ido zasu sakarwa junansu murmushi har zuwa magariba yaja Walid sukatafi masallaci Basu dawoba se da akayi sallar Isha bayan sunci abincin dare suka dantaba Hira kadan su walid sukace bacci zasu kwanta sadiya takai ko wanne dakin bacinsa tai musu addua tatofa musu sannan tafito tasamu aliyu na waya bayan yagama yakalli sadiya
YOU ARE READING
Haleematus sadeeya
Randomlabari ne akan abin da yake faruwa a yanzu ko nace a wannan lokacin da muke ciki ku biyoni danjin me nake dauke dashi