12

345 38 6
                                    

*KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT 08066726866

Ni MMN MUJAHID Ina da kayn gyara kala kala na kasa da sama Ina Saida supplement da kayan mata kala kala cikin sauki Mai kama da kyauta

Hjy ta ki ajiye kunya kifitu kiyi bayani matsala ki abaki ABINDA yaddace Dake

Ina matan da ke FAMA da bushewa gaba

Ina maccen da take a bushe kamas ba niima miji sai yasa yawun sa ku BASILIN 😳

Ina matar da kishiya ta tayi mata zarra ga miji ke rasa Ina matsala take

Ina wadda mijinta kamar kurma baya nuna ya gamsu Dake Dan ku ayi ku abari duk dai suke dashi

Shin ke ku y'ar kuwa ga mijin ki baya Yi da sanbatu in kinji ana Fadi sai kece karya ce

Nazo muku da hadin Zuma wadda duk zata magance way'anga matsalolin cikin ikon Allah wanna Zuma ta samu yabo ga duban mutane Sha yanzu magani yanzu ce Banda haufi akanta wanna Zuma tana ta yadda sha'awa Kai tsaye ruba babba 2500 karama 700👌👌

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT MUNA SAKWATO DA KEBBI INA AIKAWA KU INA 08066726866

IN BAKI SHIRYA BA KIBARI HAR KI TASHI SAYE 😀

      *🅿️12*

Ina shiga Bangaransa na iske sa tsaye a tsakiyar falon yana ta safa da marwa saboda bala'i hatta jakar da ya dawo da ita bai iya sauketa ba kamar yana jira na ina shigowa da sallamata yayi saurin zaburowa Sauran, sallaman tawa ma iya makoshina ta makale jikina ya Dauki karkarwa kamar wacce taga mutuwarta.
Hannunsa manuniya yasa ya na nuna ni cikin Matukar fushi yace"Me na gaya miki..?
Nace me na gaya miki Fa'iza akan wannan mara mutumcin yayar nan taki..?
Yafad'a Lokaci d'aya yana dagamin murya sai na tsaya na kasa gaba ballatana baya jikina na wani gif gif kamar wacce wani abu ke ja kafafuwana suka fara barazanar kayar dani sai nabi Raunin su suka rinjaye ni na koma na Durkushe saman kafafuwa na lokaci daya ina sauke sauke farantin Hannuna ina so nayi mgana na kasa tsoro nake ji kada Yaya mariya ta jimu tunda Jikin Shashen sa na jikin Dakina ne bazan so a ce yau mijina ya Tozartamin yar'uwa ba.
Ina wannan tunanin sai ji nayi ya sakar min gigitaciyar Tsawa Lokaci d'aya yana kara fadin"Nace me na fada miki Fa'iza..?
Hawaye suka gocemin na Tsoron abunda zai biyo baya,na yi baya da jikina ina karkarwa na had'a Hannayena cikin yanayin mgana ta da rawan baki nace"Don..Allah..Kayi hakuri ka yi shuru..Na kasa fad'a mata ne bazan iya ba..wlh bazan iya ba.."
Sai hawaye sharr suka gocemin wasu na korar wasu,Tsayawa ya yi yana min wani irin kallo na raini da kaskanci kafin yace"Au bazaki iya fada mata ba ko..?To ni bari naje na fada mata tunda gida na ne ba gidan wani ba"
Ya karishe fada a fusace yana sauke jakar da ya shigo da ita nan tsakar Dakin nasan zai aikata tunda ya furta Da sauri na mike na isa garesa na Durkusa ina kuka ina fadin"Don Allah..don Allah..!
Mgana ta ta kasa fitowa saboda kukan da yaci karfina Ganin yayi banza dani ya nufi hanyar ficewa yasa na kwashi gudu na isa ga kafarsa na kama na rike gam ina kuka kamar raina zai fita ina fadin"Kada ka tozartamin yar'uwa..Ka bari zata tafi..Zata tafi.."
Sai ya tsaya yana kallona kafin yace"Yaushe zata tafin..?
Cikin kuka nace"Gobe..Gobe zata tafi na rantse da Allah.."
Ko sake kallo na bai yi ba ya Fizge kafarsa sai da nayi baya na fad'i ya Fice da Sauri,ina ganin haka na mike sai da kaina ya sara jiri ya kwasheni ammh ban damu ba na marasa baya ba inda jikina baya rawa har da zuciyata ma gudu take yi da sauri a lokacin.
Sai dai me zuciyata ta tsaya waje d'aya lokacin da na fito na iske Yaya mariya Tsaye a tsakiyar falon daga dukkan alamu ta gama jin duka mganganun mu Saboda Ya Ishaq da karfi ya Dinga Tijaransa,Kasa karisawa nayi kawai sai na Tsaya ina raba ido jikina da zuciyata gabadaya yayi wani Dum kamar ya daina aiki na wani Lokaci.
Ya ishaq kuma yana ganin Yaya mariya bai yi wata wata ba ya gyara Tsayuwa yana fadin"Nasan yar'uwan ki bata gaya miki sako na ba ko..?
Yaya mariya ta kallesa cikin idon da bacin rai yasa s Launin su ya sauya kafin tace"Bata gayamin ba..Ammh Tunda kaga ai waka a bakin mai ita tafi dad'i"
Tafad'a Tana kokarin yaki da zafin zuciyar dake taso mata,Taji duka mganganun Ishaq ta dade tana jin Labarin Rashin mutumcinsa, bata taba katari da shi ba sai yau lalle ko zai sha mamakinta domin in ya yi mata kan kara wlh sai tayi masa na itace.
Cikin gadara yace"Na fad'a mata tun kwanaki da kada na kara ganin ki acikin gidana..Bazai yuyu ki rika shigomin gida bakya daraja ni ba..Kamar ni zaki rika gani kina D'auke kai kamar kin ga kashi..?ai ba gaba da ni kike ba ko Yayarku Asiya ba Sana'ata bace ballatana ke karamar alhaki kin raina uwata da yayata suna fada kina fada sannan ki rika shigomin gida kina raina min wayau bazai sabu ba..Kada na kara ganin kafarki acikin gidana Daga yau sai yau..In yar'uwanki zata yi zumunci dake in kun had'u awani waje ban hanaku zumunci ba ammh ba acikin gidana ba"
Ya karishe fad'a cikin nuna cin mutumci har yana nuna ta da Hannu,Yaya mariya tayi dariyan takaici kafin tace"Shikenan sakon naka..?
Ya daga mata kai Lokaci d'aya yana fadin"eh shikenan"
Yaya mariya ta gyara tsayuwa kafin tace"To ai ba saboda kai ko dangin ka nake zuwa wajen Fa'iza ba..Ku ai baku isa ba wlh Fa'iza yar'uwata ce baka isa ka raba jinin dake Tsakanina da ita ba gida kuma bazan fita ba sai dai kayi abunda zakayi"
Tafad'a cikin Jaddada mganarta cikin mamakinta yace"Haka kika fad'a..?
Ta daga kai kafin tace"Kwarai haka nace in kuma kana da yadda zakayi dani Bismillah.."
Kawai sai ta koma ta zauna kafa d'aya kan d'aya tana latsa wayarta cikin Fushi ya juyo yana kallona cikin Tsawa yace"Wlh ki Fad'ama yar'uwanki ta fice ta barmin gida tun kafin raina ya baci na hadata da jami'an tsaro.."
Na zaro ido cikin rawan murya ina fadin"Yan sanda.."!
Ko kulani bai yi ba ya shige bangaransa da Sauri ni kuma sai kawai na fashe da kuka da Sauri na karisa gaban Yaya mariya zan yi mgana kenan ta Dakatar dani da Sauri kafin tace"Kada ki ce Tak in na isa dake fa'iza in sha Allahu yau zan kawo karshen duk zalunci da yake miki acikin gidan nan"
Cikin kuka nace"Yaya mariya yan Sanda fa yace zai kira miki"
Tayi wani mirmishi kafin tace"in shi takamar shi iskanci na shanyesa na Dokesa ya Dade bai kira yan Sanda ba in yaso ya Dauko gabad'aya police din kasar nan gabadaya yau ko ni ko shi acikin gidan nan"
Tafad'a tana mai kara tabbatar min da mganarta nasan Halinta tana da kafiya da Taurin kai ban kara mgana ba ammh na tsorata sanin Halin Ya Ishaq na kasa zaune na kasa tsaye,Kawai sai gashi ya fito yana waya kalmar da naji ita ta Razani Cikin Fushi yake fadin"Yallabai gida na zasu zo akwai wata matsala ne..Ok sai sun kariso.."
Nasan zai aikata ba ni da Daraja a idanuwansa,ballatana Dangina su yi Daraja a wajensa zai iya aikata duk abunda yaga dama bai damu ba,kuma nasan bazai taba Saurarata ba sai kawai na zube gaban Yaya mariya na Hada Hannayena duka Biyu cikin kuka na fara fadin"Don Allah..Don Allah..Yaya mariya ki tafi bana so ya Tozartaki bana so aci mutuncin ki"
Yaya mariya ta dakamin Tsawa cikin fada tana fadin"Bazan fita ba ina nan inajiran duk abunda zai yi"
Shi kuma yace"Zaki gani sai kin raina kanki yau d'in nan"
Bana so wani abu ya faru shiyasa nake rokonta tatafi cikin wata murya tace min"Ni kike roko na bar miki gidan ki fa'iza saboda wannan azzalumin mijin naki..?
Lokacin da ta fadi haka baya falon ya koma bangaransa ganin bazata Fahimci ba yasa na tashi zan koma Shashen nasa sai gashi mun ci karo da juna,cikin sauri na rikesa ina Fadin"Don Allah kayi hakuri..Kada ka kira mata yan sanda"
Ba laifinta ba ne Goggo ne da suka zo Dubani jiya tace ta zauna na kara jin Sauki shine..Shine ma.."
Sai na kasa karisawa Cikin Tsawa yace"Shine me..?
Cikin In ina nace"Ta tafi da Ahmad tunda..Tunda na ya ye..s.."
Tas..! Kake jin karan marin da ya yarfamin sai d na yi gefe dafe da kuncina cikin Bacin rai ya nuna ni da Hannu yana fadin"Wacece ke da zaki yanke hukunci kan ya'yana ba tare da kin Sanar dani ba..?uban wa yace ki kai min yaro na wani waje? Ban miki kashedi kan hakan ba..?.
Nace ban miki kashedi kan haka ba Fa'iza..?shine kika aikata gaban kanki saboda kin raina ni ko..?
Yana mgana yana nunani da yatsa cikin bacin rai sai kawai na koma na durkushe ina kuka yaya mariya ta mike cikin Takaici da bakin ciki kafin tace"Ba dai Ubanmu kake zagi ba ko..?
Sannan daman ai dabba shi ke dukan matarsa wannan abun da kayi ya tabbatar min da cewa kai Dabba ne acikin mutane"
Ya Ishaq ransa ya baci ya taso mata itama ta taso da Sauri na shiga Tsakaninsu na rike Yaya mariya ina wani irin kuka kamar zan shide cikin Shakewar murya nace"Ki tafi..Ki tafi don Allah yaya mariya ki tafi.."
Yaya mariya ta kalleni kafin tace"Zan tafi..ammh ba ni kadai ba tare da ke Fa'iza yau zaki bar ma wannan azzalumin gidansa in kina da amfani in kuma baki da shi zai sani"
Sai na Rud'e na kasa mgana ta ja Hannuna keey kamar rakumi da alaqa zuwa Dakina ta fara Hadamin kayana tana yi tana fadin"Kin gama zaman aure in da ba'a san Darajan ki ba..da ikon Allah hakkin ki bazai barsa ba sai Allah ya saka miki"
Ni dai na kasa mgana sai uban kuka nake yi,Ta gama had'a min kaya cikin karamar akwatin Amir itama ta Hada nata kayan ta zura hijabi,Nima tace na Dauko Hijabi na saka ganin na kasa tashi yasa ta dauko min ta sakamin tajani,har zuwa Falo yana Tsaye hannayensa goye a bayansa yana Safa da marwa acikin Falon.
Yana ganin mu ya saki mirmishi kafin yace"Better..Ni bazan hanaki tafiya da yar'uwanki ba ni dai ban ce ta tafi ba in kuma tabiki wannan ra'ayinta ne sai dai ta sani in dai ta saka ta bar gidan nan to ta Rubuta ta barsa har abada"
Yaya mariya tace"To sai me..?ai daman ta bar sa har abada kenan wannan bakin gidan da bakomai cikinsa sai zalunci da mugunta da ikon Allah sai Hakkin Fa'iza ya Bibiyeka"
Ya ishaq yace"Sai dai hakkin kashe aure ya Bibiye ki dai..Sakarya wacce bata san inda ke mata ciwo ba..Na dai gama mganata ni dai in dai ta Fita to a bakin auranta sannan har Abada bazata Dawo ba"
Yaya mariya ta fincikeni tana fadin"Zaka gani yau kam zaman Fa'iza da kadaddaran auran ku ya kare"
Bai damu ba ya koma ya zauna ya Dora kafa d'aya kan d'aya ko ajikinsa,Yaya mariya ta rika jana har kofar Falo cikin Dashewar murya nace"Ban saka takalmi ba yaya mariya"
Cikin Fada tace"in mun je tasha na siya miki"
Na kara turjewa ina fadin"Yara na..Yaya mariya su Amir fa..?in na tafi wazai kula da su..?
Ta juyo tana min wani kallo kafin tace"Ko mutuwa zasu yi sai dai su mutu nan d'in ne gidan Ubansu ke kuma ai ba gidan naki uban ba ne wuce muje.."
Ta kara jana naki yarda na Bita na Turje ta juyo ta kara kallona afusace kafim tace"Fa'iza kada ki bari na saka miki Hannu"
Na kasa mgana sai kuka ya'yana nake Tunani in na tafi basu da wani Sauran gata bani da mafita sai zabin Dawowa na cigaba da zama acikin yanayin da nake saboda ya'yana.
Yaya mariya mamaki ya kara kamata lokacin da na kwace hannuna daga gareta na juya baya ina kuka nace"Ki yi hakuri..Kiyi hakuri..Ki tafi don Allah..BAzan iya tafiya na bar ya'ya na ba"
Kiyi hakuri"
Sai kawai na kwashi gudu zuwa Cikin D'akina ina kuka kamar raina zai fita kaina har wani bugawa yake yi Dif dif,Yaya mariya ta kasa motsi saboda abunda nayi Ya Ishaq kuma na zaune yana Dariya kasa kasa kafin ya mike yana kallon Yaya mariya cikin gadara yace"Fita ki bar min gida bakar munafuka..Kin dai ji kunya wlh kin kuma yi asara..Yar'uwan naki da kike Hakilo a kanta ta nuna miki baki da wata Daraja sama dani..Sai ki fice min Daga gida kada na kara ganin siraran kafafunki acikin gidana.."
Yafad'a yana nuna mata hannun alamun ta fice ta bar mai gida Takaici da bakinciki yasa Yaya mariya Zubar kwallah ta kalle shi ta kara kallonsa kafin tace"Naji kayi nasara a kaina zan tafi..kamar yadda ka bukata bazan kara zuwa gidan ka ba..Sannan mganar Fa'iza karyan ka ta sha karya ai jini yafi ruwa kauri sannan wata kusan tafi wata..Zan cigaba da zumumci da yar'uwata domin ba kai ka Had'amu ba..Mgana ta karshe shine akwai Allah kuma yana nan a madakata Duk abunda kake aikata ma Fa'iza na sharri da zalunci kai da Mahaifiyarka da yayarka,Da ikon Allah sai kunga sakkaya tun a duniya sai Allah ya jarabceka da iftila'in da sai ka rasa ina zaka saka kanka in sha Allahu sai Allah ya saukar da aya akan maza ire iren ka da basu darajan matan su sannan basa adalci  ya yin zamantakewar su,Kuma kada ka manta akwai Hakkin zumunci shima sai Allah ya tambaye ka, sannan hakkin Fa'iza bazai  barka kayi rayuwar da kake Buri ba Ishaq Kabir karofi."
Tana gama fad'in haka ta Sauke karamin akwatin na data Dauka,ta juya ta fice tana zubar da hawayen bakinciki da takaici duk da kalamanta sun Dakesa ammh bai damu ba ya Bita har get yana gayamata bakaken mganganu sannan ya Dawo Cikin gida ya Iskoni har dak'i yana gayamin duk mganar da ta fito bakinsa har yana fadim Tunda ya aureni bai Huta ba yake cikin Matsala ni ba matar kirki bace ni matar Tsiya ce.
Nayi kuka,kukan da ban taba yi ba,kukan yadda ya tozarta yar'uwata ni ban damu da kaina ba Daman ni bani da wata Daraja ammh Yaya mariya fa..?yar'uwata ce bata chanchanci cin zarafi da tozarci ba.
In da nagode ma Allah Yaran basu dawo daga makaranta ba,da suna gidan nan ban san wani amsa zan basu ba ina kwance ina kuka suka Shigo,Ganin su yasa nayi saurin share hawayena kaina ciwo yake yi duk yadda yaran suka so su fahimci wani abu ban basu dama ba da Amir ya dameni da Umma baki da lafiya ne..?naga fuskarki ta kumbura ne"
Sai nace masa wani abu ne ya fadamin a ido,Nasan inda Ya Ishaq ya mareni ne ya tasa sannan ga kuma kukan da na sha.
Tuni Ya Ishaq ya fice daga gidan na rarrafa na shiga kitchen na Dafa ma su Amir Jallop din taliya,kunyar kaina nake ji da abunda ya faru ace mijina shi ya tozarta yar'uwata da muka fito ciki d'aya uwa daya uba daya,Abun sai ya tsayamin a cikin raina ya kasa wucewa su kansu yaran su san yanayina ya sauya,suna mgana sai dai na bisu da ido kawai da wuri nayi musu shirin kwanciya Saboda ban jin Dadin jikina,Kamar kazar da kwai ya fashe ma aciki haka jikina ya koma,Kayana da Yaya mariya ta hada ni na kwaso su na maida su muhallinsu araina ina Tunanin Lokaci bai yi ba.lokacin da zan bar Rayuwar Ishaq bai yi ba akwai sauran Lokaci.

KANA NAKA..!حيث تعيش القصص. اكتشف الآن