NI CE SANADI

532 19 27
                                    

NOT EDITED

NI CE SANADI ......NA YBK

باسم الله الرحمن الرحيم .
Allah ya bani ikon rubutun da zamu amfana, Ameen.
Kyautace ga duk masoyana.

1

A hankali take tafiyarta hankalinta kwance, ta tura ƙofar ajinsu ta shiga ta samu wajen zamanta da ta saba zama a gaban aji, ta zauna.
Littafinta na ƙurani ta ɗauko ta buɗe inda taji ana karantawa cikin suratul Nisa'i.
Bata ankaraba taji saukar bulala a bayanta. A tsorace ta miƙe ta
damƙe bullarar, ta kalli mutumin da ya tsala mata bulalar, ta ƙara da "lafiya malan?"
"Ke baki da idanu ne har sai kin tambaya, ko bakiga sauran yaran ba, kowace a tsaye ta ke?" Ya fizge bulalar daga hannunta.
"Na gani amma ai ban san laifin da sukayi ba malan kawai sai in miƙe tsaye nima ba tare da nayi laifi ba" Lallai wanna malamin babu ko shakka sabon malamine, dan babu malamin da ya taɓa aza koda tsinke a jikin Hannan da sunan hukunci, ba a islamiya ba har ma boko. Sam bata son a taɓa lafiyar jikinta, hakan ya sa ta ke kiyaye duk wata doka da aka gitta mata.
"Mi sunan ki? Ya tambayeta tare da komawa wajen zamansa a gaban allo.
"Sunana Hannan AK" Ta amsa a taƙaice.
"Minene kuma AK? A dai-dai lokacin idanuwansu suka harƙe.
Ta ɗauke nata ta na tura baki ta na hura anci, idanuwanta suka ƙanƙance. Babu wanda bai san sunanta ba duk inda ta shiga. Bugu da ƙari bata son faɗin sunan mahaifinta kai tsaye. Amma da alama wannan sabon malamin ya fita tsaurin ido "Hannan Abdulkarim" Ta faɗa cikin ɗaure fuska.
"Laifinki na farko Hannan, shine zuwa makaranta ba a kan lokaci ba, na biyu na san irinku kan ku ba komai ciki sai daƙiƙanci da takkwalanci, dan haka kema sai ki miƙe tsaye kamar yadda sauran yaran su ka miƙe dan basu iya karatu ba" Ya ƙarasa maganarsa yana murmushin mugunta.
"Indai kace na makara zuwa, to na yarda, amma karatu kam har gaba da inda aka tsaya ma zan niya karantowa a hardace" Take ta kawo ayoyi goma da aka basu harda, sannan ta kawo tafsirinsu a taƙaice.
"Da ka yi rantsuwa malan da kayi kaffara, dan ban ji ka cini gyara ko ɗaya ba".
Malamin, bayyi zaton hakan daga Hannan ba, ba shiri ya ce kowaccensu ta zauna. Ya kalli Hannan yace "Hukuncin makarar da ki ka yi zai biyo baya" Ya kira ɗaya daga cikin malaman makarantar ya cigaba da koya ma su karatu, shikuwa ya bar ajin, a ransa ya na sake-sake. Wannan yarinyar ta raina ma shi hankali, har tana gaya ma shi magana. Amma dole ne ya samu hanyar da zai hukunta ta, dan dalilin makara kawai bai isa ya hukuntata ba yadda ya ke so. Sannan dan dai karatunta na yau bai isa ya sa ta cikin jerin wa'anda ya ke d'auka masu maida hankali ba na makarantar.
Fitar malamin dake tsare dasu keda wuya, Hannan ta tsinci sunan malamin daga ƴan ajinsu. Watau malan Lukman. Ƙawayenta Marwa da Halima (Sa'adiya), wanda kuma maƙotansu ne, suka lallaɓo zuwa gefenta.
Sa'adiya ta ce "Wallahi ƙawas kin taimaka mana yau, wataƙila da har a tashi muna tsaye".
"Indai ƙeta ce ba na biyunshi" Faɗar Marwa, yayar Sadiya.
Haka sauran ƴan ajin kowace ta rinƙa tofa albarkacin bakinta suna zagaye da ita, suna ƙara zuga ta.
"To wai yaushe ya fara koyarwa a wannan makarantar ne? Ni kam ban taɓa ganinshi ba ma" Hannan ta faɗa, ta na ƙanƙance idanuwa ta tsuke baki tana ƙara tuno yadda ya kirata daƙiƙiya, da yadda yasa ta faɗi sunan babanta, sam sai taji bata son shi a take.
"Ai da yake kina zuwa makarantar kwana, kuma yawancin lokuta kina Bakori, shima ba koda yaushe yake nan ba, shiyasa baku taɓa haɗuwa ba, da alama wannan ne karon farko da kuka taɓa haɗuwa" Sadiya ta faɗa tana dariya ta kai ma Hannan duka a baya cikin wasa.
Hannan ta tsala Ihu tana murza wajen, da malan ya duke ta.
"Kai Hannan wallahi kin cika raki, wannan ɗan dukan" Faɗar Marwa.
"Hmmm, Allah Ya sa ya ma ki irin bulalar da ya mani gobe" Ta faɗa.
"Mu kam ai mun saba" Marwa ta bata amsa cikin dariya.
Sauran ɗaliban makarantar ma dai malan Lukman ne hirarsu a ranar, kamar kowane lokaci in ya zo.
Ba ƙarya, ya kai cikakken matashin saurayi.
Kyakykyawan saurayi ne mai ɗan tsayi. Gashin kanshi kwance ya ke, wannan baya rasa nasaba da alaƙarshi da larabawa. Sajen fuskarshi yana ƙara ma fuskar yalwa. Hakanan bai cika yin dariya ba, amma baya ɗaure fuska, hakan ya yasa duk wanda ya kalleshi ba kasafai zai tunkareshi ba farat ɗaya. Mutunne mai kwarjini.

Kamu telah mencapai bab terakhir yang dipublikasikan.

⏰ Terakhir diperbarui: Nov 01, 2020 ⏰

Tambahkan cerita ini ke Perpustakaan untuk mendapatkan notifikasi saat ada bab baru!

NI CE SANADITempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang