1💜💚💛💙❤️
Sirrin wasu gayun
💜❤️💙💚💛® zuwairat (ummumaryam)
1️⃣
Alhamdulillah,
Free page
If you know you can't afford to pay than don't start reading, because after free pages comes payed ones. Thanks.
Wani saurayi né zaune cikin wata lungu sai kuka yake while wasu guys guda biyu na rarrashinshi, da wannan ya taba shoulder dinshi sai ya tureshi da wancan ya taba shi sai ya tureshi"Wai haba meye haka?.. Sai kace ba namiji ba?.." Inji daya daga cikin samarin, "Pls ku kyaleni Inyi kukan...ko na fi samun sauki azuciyata...eight years muna tare da khairat amma rana tsaya za'a rabani daita Don an gan ban da kudi..." Saurayin ya fada cikin matsanacin kuka, "Ai sai ka dauki hakuri...komai sai in Allah ya kaddara...kilan ba itace matarka ba..." Dayan saurayin, idanuwa Mai kukan ya daga ya watsawa Wanda yayi magana harara tare dacewa "Haka ma zaka ce?...tou Yanzu bani kudin néman aure in Kai in ba'a bani ba?.. Kawai talauci na yasa na rasa khairat..." Yafada still crying, "Pls safwan kayi hakuri...komai sai in Allah ya yarda ake yinshi...kar ka tada hankalinka..." Inji Dayan, "Pls ku rabu Dani...kawai ku tafi ku barni...you guys won't understand how am feeling...mutuwa ta fi mun komai a Yanzu..." Safwan ya fada cikin kuka, "Nikam nasan yanda nakeji...ba two months ago akayiwa aliya aure ba?.. Kowa yasan Ina kaunar Aliya amma haka na hakura tunda bani da Abunda zan bata in na aureta...ni saida ya kaiga in yan gidan sun ganni sai suce sun rabu da matsiyaci....kawai muyi hakuri..in Allah ya kawo aiki zamu samu wayanda zasu auremu..." Inji daya daga cikin su Mai suna usman, "Yau she zamu samu aiki?... Whole three years da gama degree babu aiki...in mutum baiyi karatu ba ace Don bai da ilimi gashi munyi hustling munyi karatu amma no body is willing to help us and give us a job...Yanzu sai Mai long leg ke samun aiki..." Habib ya fada cikin tsananin bacin rai, "Ai naka is better...tunda uncle Dinka yana da Hali..." Habib ya fadawa safwan da har lokacin bai bar kuka ba, "Kodai muje wurinshi mu rokeshi ko zai taimaka ya Baka kudin da za'a Kai gidansu khairat?.." Usman yafadawa safwan, sufwan daga red eyes dinshi yayi yace"Kawu musan da ko zamu mutu da yunwa bai taimaka mana?.. Shi zai fadawa ya bani kudin néman aure?... Gaskiya ban iya Kai Kaina in sha zagi da yamman nan..." Sufwan yafada cikn bacin rai,"Amma wannan uncle din naku baiyi ba...haba Dan Allah...bai da tausayi ko kadan..." Inji habib, "Ai ni ba tun yau ba nasan bai da mutunci..remember lokacin da ya ganmu mun dawo daga school shi kuma ya dauko yaran shi amma yaki rage mana hanya..hmmmallah dai ya kyauta...kilan yana tunanin mu muka darawa kanmu talauci..." Usman ya fada, shi dai sufwan bai Kara cewa komai ba saboda abinda ya dame shi da ban, kawai he's missing the love of his life, kawai Yanzu yana tunanin saboda bai da kudi ya rasa komai, he loose his two sisters because basu da kudin da zasu biya hospital bills dinsu. Ajiyan zuciya ya saki yana lumshe idanuwa while best friends dinshi suna magana kan habit din uncle dinshi, ahankali ya daga Kai ya kalle friends dinshi yace"Wai yasuhe wannan wahalal zata Kare?... Yasuhe muma zamuyi arziki kaman sauran mutane?... Yaushe zamu samu daraja a idon mutane..." Duk ya jero masu wannan questions din, ahankali Habib yace"Mu dai kam ya zaayi muyi arziki?... Wa zai taimaka mana?... Masu kudi kansu kawai suka sani...kalli makocinmu ko zakka bai fiddawa...last Ramadan da akwai days da bamu samun wani abun kirki muyi buden baki amma su dadinsu suke ji...Kai duniya..Wallahi am tired..." Usman yafada kaman zaiyi kuka, "I wish Ina cikin masu kudi...da na taimakawa talakawa...dana saka mutane da dama farin ciki...amma sai gashi Allah bai yoni Mai arziki ba..." Inji habib, "Ni nayi wata tunani...me zai Hana muje wurin makocinku mu fada mashi ya bamu kudi muyi sanaa in yaso sai mu biyashi with gain..." Sufwan ya fada cikin sanyinmurya, "Anya wannan Mutumin zai yarda?... Da wahala..." Usman ya amsa mashi"Kawai mu gwada mu gani..." Habib yayi adding, sufwan da har lokacin idanuwanshi is still wet ya goge tare da mikewa ya gada bombom din wandon shi fitowa sukayi saga wannan lumgun da suke,unguwar ba unguwar masu kudi bane, irin area din nan né wayanda in kana da machine sai kabi ahankali zaka iya tukata ka shiga gidanka, koina hayaniyar yara né da matasa, duk inda suka ratsa sai an kirasu, suna zuwa wurin wata yarin dake saida awara habib ya duka ya dauki daya"Wallahi yaya hamsin kenan..." Mai awarar ta fada mashi, "In ban biyaba ki kulleni..." Habib ya amsa mata yana dariya, duk matasan babu Wanda ya wuce shekara ashirin da takwas zuwa da tara, kowannensu na sanye da yadi Wanda bai wuce 500 per yard ba, Kayan jikinshi is not expensive but they look neat, "Allah yasa yau an ajiyemin abinci." Sufwan ya fada yana tafiya, "Ni rabon da a ajiye min abinci a gida har na mance....kullum fadar mama na ki samun aikin yi..Tana ganin kaman da akwai aikin nakiyi...h,mm" habib yafada,"Ai Nima haka Inna take fadan banason aiki..wai nafison in dau wanka in dinga yawo agari..." Usman Yafada yana dariya, "Allah dai ya kawo mana iyakan wannan wahalal..." Sufwan ya fada hannunshi biyu cikin aljihu, ahankali suka dinga tafiya har suka Isa wata makeken gida dake bakin titi, duk fadin unguwar babu gidan daya Kai wannan girma da kyau, babu Mai cewa a bayan wannan gidan da akwai gidan talakawa da yawa because the house is all over the place, Nikam I wonder wane Mai kudi né ya Gina wannan katon gida a wannan unguwar, kawai shi yana da access din shiga gidnshi da mota saboda a bakin titi gidan yake amma duk wayanda suke baya basu da hanyar kirki, babu komai sai gutters da sauro da hayaniyar mutane, bakin gate din sukayi knocking after like two minutes maigida ya bude, kallon su yayi from head to toe Sannan yace"Ya dai..." Ya tambayeshi kaman bai taba ganin su ba dukda he knows them, "Wurin alhaji mukazo..." Usman ya fada mashi, kallon banza maigida ya watsa mashi yace"Ka dai San alhaji bayason hayaniyar ku..." Bai karasa ba sufwan yace"Malam ba hayaniya mukazo yi ba...kawai munzo ganinshi né.." Maigida juyawa yayi gareshi yace"To Mara kunya bai nan..." Ya fada mashi, "Haba Dan Allah ka taimaka kayi mashi magana mana..nasan yana ciki.." Usman Yafada mashi cikin girmamawa, "Ikon Allah...wai meye haka?.. Na fada maku bai nan..ku tafi dan Allah ..."Inji angry maigida. Usman zai bude baki yayi magana habib yace"Mu tafi mana...wai dole né?.." Ya fada sounding pissed off, ahankali usman ya rike shoulder dinshi Wanda hakan ya danyi calming nerves dinshi, tsoki Mai gado yaja ya rufe gate din. "I suggest mu koma gefe daya mu jirashi, dole zai fito sallah magrub...lokacin ya kusa..." Sufwan ya fada masu, babu musu suka koma gefe daya suka zauna suna kallon titi then suna hira, bayan kaman minti arbain aka Kira sallah, nan bakin titi sukayi alwallah duk idanuwansu kan gate din alhaji Ibrahim, suna gamawa alhaji Ibrahim ya fito da wasu elderly people guda hudu, "Wannan maigadin bai da mutunci Wallahi..." Inji habib, yana wucewa ta inda suke suma suka bi bayanshi suka isa same masjid sukayi sallah, bayan an idar alhaji ya fito da friends suma su sufwan suka yi saurin bin bayan shi, sallama usman yayi mashi ya juyo ya kalleshi tare da amsa sallaman mashi, da sauri usman yace"Alhaji tun dazun muna bakin gate Dinka muna jira ka...Mai gadinka yacebaka nan..." Alhaji tsayawa yayi ya kalleshi Sannan yace "Tou ya akayi..." Ya tambayeshi Kai tsaye, mutane dake tare dashi tsayawa sukayi suka zuba masu idanu suna kallon su, usman rasa abinda zaice yayi, sufwan yayi saurin cewa"Alhaji so muke ka taimaka mana..." Bai karasa ba alhaji Ibrahim ya daga mashi hannu su kuma manyan mutane dake tare dashi suka saki dariya"Wai meyasa Baku da tunani?... Wai an fada maku Ina growing kudi né?...kowa ya kwaso tsiyarsa wajena yayo... Dan Allah ni ku bar tambayata taimako...Nima ta Allah na dogara...bani da bushiyar kudi...ko roki Allah shima ya baku...daga yau ki bar damuna..." Alhaji Ibrahim ya fada cikn bacin rai, da sauri habib yace"Alhaji ba kyauta mukeso ba...kawai munason ka taimaka mana da wani Abu...mu fara Sanaa sai mu biyaka da riba..." Dariyar da mutanen keyi yasa habib yin shuru"Just listen to what this boy is saying..." Alhaji Ibrahim ya fadawa friends dinshi dake dariya har da rike ciki, "Wai kaman ni zasu damfara..."Inji alhaji Ibrahim"Wallahi sir ba danfararka zamuyi ba...kawai dai ..." Sufwan Bai karasa ba wani daga cikin mutanen dake tare da alhaji Ibrahim yace"Ku kam kuje wajen government...Sannan kullum Ana fada maku kuyi karatu rashin ji bai barin ku...gashi Yanzu tun Baku Kai koina ba kun fara maula..." Habib dake girgiza Kai saboda yanda yake ji cikin ranshi yace"Alhaji munyi karatu...we have good result..." Bai karasa ba wani daga cikin su ya ce "Then good and look for a job...ku bar maula...bai kamace ku..." Mutumin ya fadayana kallon su from head to toe saboda basuyi mashi Kama da wayanda suka da ilimi ba, "Wallahi alhaji kullum muna néman aiki..samu none bamuyi ba..." Sufwan yafada cikin sanyinmurya, "then take your problems to the government...ku bar damuna...kullum unguwar na kun maida ni kaman cbn...kowa yazo ya tatsa..." Alhaji Ibrahim ya fada yana juyawa, manyan mutanen suma juyawa sukayi daya daga cikinsu yace"Ni Wallahi am still wondering yanda akayi bazaka rabu da wannan local area ba...kwata kwata bai dace da Kai ba..." Wani abokinshi ya fada mashi,"Hmmm Ai wannan wajen wuri né na iyaye da kakanni...Sannan wayan nan mutanen da kake gani they're are like securities...nothing bad can happens...so I know why am staying here..." Alhaji Ibrahim ya amsa mashi, "Lallai kam...amma dai kana kokari..." Wani ya fada mashi"Ba kadan ba...kullum cikin bara suke, iyayen su suyi...matansu suyi Sannan matasansu suyi...duk Kaina ni kadai..." Alhaji Ibrahim ya fada sounding so fed up, daya daga cikin su Mai suna alhaji yunusa da tunda su sufwan suke yi magana bai bude baki ba yace"To you should try and help mana...ai mu da Allah ya bamu ba wai Don mun fisu bane...he has a purpose for our lives..." Yafada calmly, "Ai ba wai ban basu ba...kawai suna son in basu duk abinda na mallaka which is not possible...at times Ina siyan buhun shinkafa in Kai nan baya a raba masu...ai Ina iya kokari na...I can't do more than am doing..." Yafada mashi atakaice, gate aka bude masu suka shiga. Har suka shige sufwan, habib da usman suna nan tsaye duk sun rasa abinda ke masu dadi, "Ni Wallahi da na sani da kudin da na yi karatu dasu ajiye su nayi na nemi Sanaa dashi...gashi munyi karatun babu aiki..." Habib ya fada sounding so angry, "Kawai we should be hoping...Allah will surely make way..." Usman ya fada, shi kam sufwan baice komai ba saboda tensions sunyi mashi yawa. Kan wata dakali suka koma suna hirar how to get out of this absolute poverty, duk mate dinsu dayazo wucewa sai yace"Yan uku ya kuke..." Daman sunan da ake kirasu dashi kenan...basu hada komai ba amma amincinsu is too much, komai tare sukeyi, they're birds of the same feather so they flock together, babu Mai taba daya daga cikinsu ya zauna lafiya, kowannensu is cute and handsome but yanayin rayuwa yasa ba'a ganewa suna da kyau, babu Mai jiki cikinsu they're all slim and tall, they understand each other sosai to the extent da wuya suyi fushi da juna, gasu da kishin junansu, they share each other's pain and joy, suna rikewa junansu amana, basu boyewa junansu komai, duk faman hustling da sukayi na néman kudin school tare sukayi, duk semester da daya bai samu kudi ba sauran zasu taimaka suyi buga buga su taimaka mashi ya biya kudin school, at times suna tunanin ko matan da zasu aura bazasu sosu kaman ya da suke kaunar junansu ba, dukkan su unguwar su daya sai dai gidan su usman is closer to the road shiyasa suke kiran alhaji Ibrahim neighbor dinsu because he's closer to him, dukkan su haifaffun garin Kano né, the attended buk and passed out with a flying colors amma basu da aikin yi, duk yanda zasuyi sunyi but no jobs, sun rubuta application wurare daban daban amma ko interview ba'a taba kiransu ba balle su sa ran aiki, yan kudin da suka samu wajen nysc suka hada suka bude shop a unguwar su amma bayan shekara daya yayi liquidating saboda expenses din families atakaice dai dukda ba aiki suke ba their families depends on them tunda iyayen su basu da wani aiki na azo a gani, hamma habib yayi sufwan daya yayi rafka tagumi ya juyo ya kalleshi tare dacewa "Ya dai..." "Wallahi bahbah yunwa nakeji...har na mance rabona da abinci..." Habib yayi fada yana Kare bakinshi, "Ka dai mance...dazun ba mun ci shinkafa a gidan mu ba?.." Usman yafada, dariya habib yayi yana cewa"Da wannan shinkafa da babu ai duk daya né...ko mi kadai zan cinye bai isheniba ..." Dariya sauran sukayi sufwan wace "Mujira Muyi sallah ishai muje gida kilan mun samu Abunda zamuci..." Ya fada looking at habib, "Allah yasa...nidai am so hungry Wallahi..." Yafada yana dafa flat tummy dinshi, "Kullum Baka da aiki sai kukan yunwa...even when muna cikin damuwa...mtwss.." Inji usman, dariya habib ya kasayi yana cewa"Ai abinci dole né...man most eat..." Yafada sounding carefree, shidai sufwan har lokacin babu abinda yake tunani sai khairat, Yanzu he can't believe khairat will be the total property of another man bayan duk plan da sukayi na aure, she loves him and he loves her amma Yanzu yana ji yana gani zai rasa ta"Kai duniya...." Yafada yana girgiza Kai, "Pls a bar wannan maganar mana..." Usman ya fada mashi, juyowa sufwan yayi ya watsa mashi harara yana cewa"Pls ku rabu Dani..." Yafada yana mikewa, barinsu yayi nan wajen su kuma suka Mike suka bi bayanshi, bakin masjid sufwan yaje ya zauna yana sauraron Ana kiran sallah ishai, baki suka kuskura suka shiga cikin masjid. Bayan sun idar da sallah suka fita duk gidansu sufwan suka nufa, wata karamar gida suka tsaya sufwan ya dauko keys daga cikin aljihu ya bude makullin dake bakin wata Kofar sake waje su usman da habib suka shiga ciki shi kuma ya koma hanyar Dayan kofar ya shiga yana sallama, gani duhun dake yar zauren yayi yawa yasa ya Fiddo waya daga cikin aljihunshi ya kunna touch light din wayar, compound din bai da girma sai dakuna biyu né cikin gidan, sai bathroom da wata local kitchen, sallama ya sakeyi yana cewa"Inna.." Ya fada yana ya ye kabulen dakin, wata middle aged woman nagani Tana sallah, bai Kara cewa komai ba ya saki curtains din ya nufi yar kitchen din, pot ya bude yaga miyan kuka sai kuma wata kwano dake dauke da tuwo, wata kwano ya dauko Sannan ya dauki tuwon, yana daf da zuba wa Inna ta fito rike da chasbaha, "Inna inawuni?..." Ya gaisheta "Lafiya...." Ta amsa mashi atakaice Tana kallonabinda yakeyi"Me kakeyi?.." Ta tambayeshi Kai tsaye, "Inna tuwo nake diba.." Yafada tare dacigaba da zuba tuwon"Anya kana da hankali kuwa?... Yanzu wannan uban tuwon zaka dauka kannenka suyi kalaci da me?.." Ta tambayeshi, "Ai Inna ba ni kadai zanci ba..tare nake dasu usman..." Bai karasa ba Inna tace"Lallai ma...ku Wallahi Baku da kunya...manya irin ku Baku Jin kunyar ku shiga kitchen ku debi abinci alhalin ba ko sisi kuke kawowa ba..." Bata karasa ba sufwan ya fara turo baki kaman zaiyi kuka ya kwantar da murya yace"Inna Dan Allah kiyi ahankali karsuji..kinga Nima inaci gidansu...kuma kinsan in Ina dashi ban boye maki..." Yafada kaman Mai rada kar abokanshi su ji saboda yasan duk wata magana Mai karfi yana kunnensu, ,"Kaci ubanka...dallah ka rage wannan Abincin...sauran kannenka dake nemo kudin zasuyi kalaci dashi..." Ta fada mashi atakaice, ahankali ya rage tuwon ya sake cewa"Rage...ci kawai kuka iya sai kuma gantali cikin unguwa...sa anninku suna chan da iyalensu..." Tafada afusace, ahankali ya sake ragewa, tuwon da ya rage sauran Dan kadan Inna ya zuba mashi Miya dan kadan kuma tayi tsaye Don kar ta bar wajen ya Kara, ahankali ya fita da kwanon abincin su usman da suka gaji da zama cikn duhu kalleshi, ajiyewa yayi nan wajen ya kallesu yace"Bisimillah..." Yafada masu atakaice yana komawa kan kwallabati ya zauna, "Kai fa..." Usman ya tambayeshi yana gyara zama, "Ni abinda ya dameni daban.. Bata abinci nake ba..." Yafada yana tagumi, "Ta khairat kake kenan..bari yunwa ta hanaka bacci ..." Habib ya fada mashi yana Kai hannu cikin kwanon tuwon, sufwan dai bai fada masu komai ba Illah ya kurawa waje daya Ido yana tunanin what a horrible world is this,. Within three minutes habib da usman suka cinye Abincin wata budurwa tazo shigewa gidan habib ya kalleta yace"Asiya ki kawo mana ruwa..." "Tou " Ta amsa mashi ta shige few minutes later ta kawo masu ruwa. Yau dai sufwan bai rakasu zuwa inda suke hira har goman dare ba, he feels so bad, bai San yanda rayuwa zata kasance mashi ba, he's become one fed up, "Wai ahaka zamu kare?.." Yafada cikn sanyinmurya "At 29 bamu da komai na kanmu?.." Ya fada yana juyawa kan yar katifar dayake Kai, "Ya Allah ka iyakance mana wannan wahalal..." Yafada kaman zaiyi kuka, yana juye2 ya dingayi har lokacin sallah asuba yayi, mikewa yayi ya shiga cikin gida ya Kama ruwa yayi alwallah yayi sallah, yana dawowa ya dauki jarkoki yaje near by borehole ya bugo ruwa jarka 6 kaman yanda ya Saba duk safiya kafin gari ya waye, daki shi ya koma ya kwanta sai lokacin bacci yayi gaba dashi. Karfe goma ya farka ya shiga cikin gida yayi wanka, fitowa yayi ya shiga dakin Inna yace"Dan Allah Inna zan samu wani Abu na kalaci?.."ya tambayeta cikin sanyinmurya, kallon shi tayi from head to toe Sannan tace"Baka da ko sisi amma kana kwance kana bacci har Karfe goma kaman wani shugaban kasa...ya zaayi ka samu aiki?.. Lokacin da masu néman aiki suna chan suna nema Kai kana nan nannade cikin bargo...to jeka bani da wani abun kalaci..." Tafada mashi cikn bacin rai, kura mata Ido yayi for a moment hawaye na taruwa idonshi, "Inna kaman Yanzu ganina yana bata maki rai....kiyi hakuri...Wallahi babu yanda naiya né...wata rana sai labari..." Yafada cikin sanyinmurya, tsoki Inna taja tace"Wata rana sai labari..kilan in na mutu zaka samu labarin...nidai ka fice min da gani...mata da yawa suna alfahari da yaransu na farko..amma Banda Kai..." "haba inna...ya kikeso Inyi da Kaina né?... Kina ganin a son Raina nake yawo cikin unguwa?..farin cikina né Ina yawo cikin gidan nan?.. Wallahi Inna bani da farin cikin daya wuce in faranta maku...kullum gurina in samu in Baku amma Allah baisa hakan ya faruba...nidai Inna kawai adua nake bukata daga gareki...Dan Allah kar ki karamin sama da abinda nakeji...pls Inna..." Yafada hawaye na taruwa idonshi, tsokin takaici Inna taja ta juya ta shiga dakinta Tana cewa"Allah yasa ba kashin tsiyar ubanka ka dauko ba..." Tafada kaman she's not talking to her own son, ahankali sufwan ya fita daga gida ya shiga dakinshi dake Kofar gida ya zauna, kawai sai ya fara hawaye, "In wacce ta haifeni ta tsananeni because of my poverty Ai kowa ma zai tsaneni..." Yafada cikin hawaye, bude Kofar akayi habib ya shigo, da sauri safwan ya goge face dinshi, zama habib yayi gefenshi yace"You and Inna?.." Ya tambayeshi Kai tsaye saboda sun San yanda Inna takeyi mashi, suma nasu iyayen suna masu haka but na Inna is worst, kullum fadanta sufwan ya kawo kudi kaman zaiyi sata,"Wai saboda wannan kake kuka kaman you're not a man?... Ai inda sabo ka saba...pls stop crying..ka shirya muje néman abunyi...ko Dan garuwane muje wata unguwar muyi..." Habib ya fada mashi, ahankali sufwan ya kalleshi yace"Dan garuwa fa Kace?...." Sufwan ya fada cikn sanyinmurya, "To do we have a choice?... Ya zamuyi?.. Yau gidan mu babu komai kuma ni mama taje jira...Yanzu dai dole yau mu nemi wani Abu da zamuyi tunda shagon dinki babu kasuwa..." Habib ya fada mashi, "Ni ko tafiya ban iyayi sosai...rabona da abinci tun shinkafa da mukaci gidansu usman..." "Yanzu dai ka shirya muje gidan shinkafa da wake ka siya kaci mu fita""Wallahi sisi bani dashi..." Sufwan ya fada mashi "Muje Ina da Dari...ka saya kaci sai mu tafi..." "Ina usman..." Sufwan ya tambayi habib,"Nasan yana daf da shigowa...Yanzu na ganshi yace babanshi ya aikeshi layin jankai...amma daga chan zai zo nan..." Habib ya fada yana kwantawa kan katifar, ahankali sufwan ya Mike ya dauko Vaseline ya shafa Sannan yadauko wata neat blue yard ya saka, takalmin shi ya goge da old labulen bakin kofa ya saka, fita sukayi tare da habib sai suka hango usman karshen layin ya taho, jawo kofar sufwan yayi ya kulle, usman na zuwa suka gaisa Sannan suka nufi gidan shinkafa da wake, habib ya sayawa sufwan na 70 yaci Sannan suka bar wajen,"Nifa Allah na gani bazai yu Insha inuwar ceiling in dawo Ina saida garuwa ba...kawai mu nemi wani abunyi..." Usman ya fada not in support of abinda habib yace, "Me zamu nema Yanzu?... Ai munyi kokarin nema amma hakan baiyuba...kawai muyi garuwa in da rabon mu hole a gaba mun hole..." Habib ya fada, shidai sufwan baice komai ba, "Gaskiya aa...kawai I suggest mu cikin gari muna bin shaguna ko suna butatan maaika...kilan muci saa..." Shuru habib yayi ya kalli sufwan dake tafiya kaman Ana ingiza shi yace "Wai Kai won't you say anything?.." Habib ya fada cikin bacin rai, ajiyan zuciya sufwan yayi yace"Hmmm me Zance...kawai let's Allah's will be done..." Yafada cikn sanyinmurya, tafiya sukayi har cikin gari which takes them about one hour, wani katon shigo suka shiga sukayi tsaye suna kallon masu shopping, wajen Wanda ke zaune counter sukaje, habib yace"Dan Allah Ana samun aiki?.." Ya tambayeshi, Mutumin kallon su yayi from head to toe Sannan yace"Aa ba vacancy..." Aka amsa masu atakaice.Cikin wani gida wata yarinya ce zaune gaban wani maguji Tana wanke wanke kwanoni, sai gunguni kawai take alaman she don't want to wash the plates, wata yarinya ce ta ta fito da wasu plate kuma yarinya ta juyo afusace ta kalleta Tana cewa" ke Dan ubanki daukesu ki maida..." Ta dakawa yarinyar tsawa, da sauri yarinyar ta juya kaman zatayi kuka tace"Mommy..tace batayi" naji yar yarinyar ta fadawa mahaifiyar su, wata fara matar Mai kyau ce ta fito daga daki tace"Maza ki maida mata..." Ta umarci wannan yar yarinyar, juyowa yarinyar tayi ta taho da plates din, irin kallon da Mai wanke wanke take mata yasa tayi saurin ajiyesu ta bar wajen da alaman she's so afraid of her, Mai wanke wanken sake juyowa tayi looking so furious, yarinyar na ajiyewa ta Mike Tana cewa"wai ni baiwace a gidan nan?... Duk aiki ni kadai keyi..Sannan abun takaici inayi kuna turomin wasu kaman jakka..." Tafada kaman zata tashi sama, "Lallai ma nana...wato Yanzu kin girma ban isa in saki aiki ba..." Matar ta fada, baki yarinyar ta turo Tana cewa"Na gaji Ai...aiki kullum kaman jakka?... " Bata karasa ba matar ta nufota "Maza ki farayi kafin ranki ya mugun bace..." Da sauri yarinyar ta dawo kujera wanke wanken ta tacigaba dayi Tana cewa"Wallahi ko za'a kasheni a campus zan zauna..ban zaman gidan nan..." Tafada kasan makoshinta. Share...

YOU ARE READING
Sirrin wasu gayun
Mystery / ThrillerIt's story about greedy rich people, greedy ladies and guy with no jobs