10

3.3K 204 1
                                    

            💖ABDUL-MALEEK!!💖
                             (BOBO)

             Bilyn Abdull ce

Pg 11

A 6angaren bobo kam bayan sun dawo daga masallaci aharabar gidan suka sake zama, hira aketayi da barkwanci, saida aka k'ara kiran sallar isha'i sannan suka mik'e, masu sake alwala suka sake, wadda tasu bata karyeba sukayi gaba.
   Ana idar da sallah suka shigo gidan, shiri suka fara, kowa yana k'ok'ari kada time ya k'ure.
   Bobo kam wanka shima yashiga, yafito d'aure da tawul fari a k'ugunsa, k'arami kuma yana goge kansa zuwa fuska da wuya har k'irjinsa zuwa k'asa.
   Wurga tawul d'in yayi saman kujera, yaja kujerar madubi ya zauna, mai yafara shafawa, hardasu farar fauda afuska, yashafe kansa da mai mai k'amshi har zuwa sajensa dad'an gemunsa na gayu, yasa kum yak'ara taje kansa da gemunsa, sannan yay amfani da burosh wajen kwantar da sajensa, yako kwanta luf sai walk'iya yake da tashin k'amshi.
    Turarurruka yad'auka kala kala yafeshe jikinsa, sannan yanemi guri abikin gado ya zauna batareda niyyar saka kayaba.

Atsakar gida kam mutane harsun fara fita, Dan kowa bayaso atafi abarsa, dandanan motoci suka fara d'aukar mutane, kowa ya cakire da kalar kayan dayakeso, manyan iyayene kawai suka saka wani Dan datsetsen less fari tas, suka nad'a Orange d'in gwagwgwaro, masha ALLAHU abin sai Wanda yagani.
     Su khairiyyama ba'a barsu abayaba, sunci ado da dogayen riguna na lemon green d'in material sunyi k'yau masha ALLAHU, suda matansu ya sulaiman duk iri d'aya suka saka.
   Nawal ma anshiryata cikin farin less irinnasu Ammi, doguwar riga aka mata, aka nad'amata Orange d'an kwali, yarinyar tafito d'as kamanninta da bobo ya k'ara fitowa.
   Tare suka shiga Mota da Ammi.

Ya Hamza yafara waige waige, cikin Jan tsaki ya ce, "wai mi Bobo yakeyine tun d'azu yafasan saiyaje sun taho da amarya, gasu ammi harsun wuce.
   Ya is'haq shima yay tsaki ALLAH yaron nan d'an wulak'ancine, Hamza kaje d'akinsa kaga miyakeyi?.
   Ya Hamza yanufi d'akin Bobo, ya Sulaiman dai baice k'alaba.
   La'ilah Abdulmalik minene haka?.
  Bobo dake zaune yana latsa waya yad'ago yana kallon ya Hamza daya had'e cikin Farin Suit sai k'amshi yake.
    Minayine yaya?.
Bansaniba, dallah malam kana 6atamana lokaci katashi kasaka kaya, su Ammi harsun wuce.
   Baki yaturo kamar wani k'aramin yaro, nikam wlhy ya Hamza barcima nakeji.
   A'a kakan barci kakeji ya Hamza yafad'a ahasale, wlhy zankira ya Is'haq.
   Da Sauri bobo yamik'e, yafara saka gajeren wando da bes, ya warware had'ad'd'un Suit lemon green sai d'aukar ido sukeyi.
   Wandon yafara sakawa da Orange d'in Riga mai dogon hannu, ya tsuke k'ugunsa da belt, ya Hamza yad'auki nektayit d'in green yafara saka masa, shi abumma dariya yabasa, amma baiyi dariyarba gudun kar ya Hamza yasake k'uluwa.
   Da taimakon ya Hamza yasaka rigar Suit d'in, yafara saka botiran ya hamza na gyara ma kwala d'in. Takalmima saida ya taimaka MASA yasaka, sannan yak'ara feshe jikinsa da turare, yad'auki wayarsa d'aya yazura a aljihun Suit d'in, suna tafiya yana d'aura agogo.
  Na ce o'o me bobon Ammi sai a slowly.

Saida ya Hamza yaga yashiga mota a baya, sannan shima yashiga mazaunin direba Nasiba d'iyar k'anwar Ammi na gefensa.
    Suma su ya is'haq suka tada mota, suna gaba su bobo na bayansu har anguwar su Rahma.

Ak'ofar gida suka faka, ya Hamza yafita shida Nasiba har cikin gidan suka Shiga sukace afito da amrya ango yazo.
   Gaban Rahmane yafad'i Ra's, jitake tamkar tafasa ihu, kowacce irin tarba angon zai mata ta tanbayi zuciyarta?.
  Batada mai bata amsa, tana cikin zancem zuci aunty Ruk'ayya ta ce, taso Rahma angonki yazo.
  Jitake tamkar ta ce, bazataba amma yazatayi.
  Haka aunty Rukayya takamo hannunta sukayo waje, dama dayawan mutanen sun tafi sai k'alilan suka rage.
  Kowa yashiga mota amarya kawai akejira.
  Ya Hamza yabud'e d'ayan gefen da Bobo yake zaune Dan ganin amarya tafito. Azuciyarsa ya ce, ''masha ALLAHU, gsky amaryar auta ta had'u.......
  Isowarsu ta k'atse masa tunani, yayinda gaban Rahma keta fad'uwa azatonta Ya Hamzane angon, kanta na k'asa aunty Ruk'ayya tasakata amotar.
    Wani k'amshine da sanyi suka bigi hancinta, tashak'a talumshe ido azuciyarta ta ce, ''oh ALLAH, wannan wane irin k'amshine?.
   K'ok'arin gyara zama tayi saitaji ta dunguri mutum, dasauri tajuyo ta kallesa, yana zaune ak'ame kamar wani jinin sarauta, saidaifa k'amshin amaryar tasa ta narkar da zuciyarsa, saiwani lumshe idanu yakeyi, ahankali yajingina bayansa da kujerar ya lumshe ido.
   K'irjin Rahma sai dukan uku uku yake, jitayi wani sabon zazza6i yana neman rufeta, dukda kallon fisha tayima angon nata ta tabatar ya had'u masha ALLAHU.
    YA Hamza dake tada mota ya ce, amaryarmu ykk?.
    Muryar Rahma na rawa ta ce, "ina yini.
  " lfy lau, ya fara hidima?."
   Alhmdllh tayi maganar ahankali.
  Tad'an kalli gefen Bobo ta ce, ina yini.
    Dukda yagane dashi take amma yay shiru.
   Takuma cewa ina yini, sai asannan ya amsa da lfy, ykk?.
   Kasa amsashi tayi, sai kawai tayi k'asa da kanta tana wasa da zoben hannunta.
   Sunkusa isa wajen faty d'in Bobo yatashi zaune sosai, wata leda yad'akko agefensa yazaro rafar 'yan 200 guda hud'u yad'ora saman cinyarsa.
    Rahma data k'urama zonen hannunta ido saikawai taga mutum ya d'oro hannunsa saman cinyarta, gabanta ya ce, "wani Rasss!, fos d'inta yazare data d'ora saman cinyarta ta d'ora hannunta akai.
  Tabud'e idonta ahankali daga rintsewar datayi, Fos d'in yabud'e yaga 'yan 50 rafa biyu sai wayarta, wayar yaciro yasaka kud'in daya ciro aleda yasa a fos d'in maida wayar yayi zai rufe fos d'in amma tak'i shiga dan tacika dayawa.
   Ciro wayar yakumayi yarufe fos d'in yad'ora mata saman cinyarta, wayarta kuma yasaka cikin aljihun suit nasa, nufinsa idan sunje angama taron talik'a kud'in saiya bata.
   Itadai Rahma batace masa k'alaba Dan batasan miyayi da fos d'inba.
   Har gaf da d'akin taron ya Hamza ya faka, yafito yabud'e musu k'ofa, asanyaye Rahma tafito, duk kunya ta isheta tasaba duk inda zataje saida k'aton hijjab, amma yau gata kod'an gyale babu, sauk'intama Rigar bubuce kuma tabud'e bata matsetaba.
   Su yaya Ishaq suma fitowa sukayi daga motarsu, suma kayansu iri d'aya dana ya Hamza.
  Suma sun yaba da amaryar k'anin Nasu sai masha ALLAHU suke jerowa.
  Ya Hamza yashiga d'akin taron yasanar da MC amarya da ango sun iso.
  Aiko nanfa yafara kayayato, falon taron yay tsit anzuba ido aga amaryar Bobo d'an gayunnan maiji da kansa.

Ahankali Bobo yatako har zuwa gaban Rahma data duk'ar dakai k'asa kamar ace ar ta gudu.
   Ahankali ya ce, "bismillah muje.
     Jerawa sukai suna tafiya ahankali har cikin wajen, bayansu kuma su ya Sulaiman ne suka take musu baya.
    Tunda suka shiga wajen taron jikin Rahma yay sanyi, Dan ita irin mutanan ne masu tsoron shiga mutane, dandanan tafiyarta ta sauya, sai wani sassarfa takeyi.
   Raf raf raf raf!! d'akin taron yad'auki tafi lokacinda Rahma ta hard'e taigaba kamar zata fad'i, da sauri Bobo yaruk'o hannunta yana fad'in ezeee madam.
    Ajiyar zuciya tasauke danjin bata fad'iba, a u okey?, yafad'a yana kallonta. Kai tad'aga da sauri.
   Tom kiyi ahankali plzz karki ji ciwo.
  Ngd tafad'a tana kallon k'asa, to muk'arasa ya nuna mata hanya.
    Ahankali suka taka zuwa inda aka tanar musu, sunbirge mutane gsky saidai mak'iyi, kowa fad'i yake sun dace da juna, Ammi saijin dad'i takeyi Dan harga ALLAH Rahma tashiga ranta.
   Suna zama DJ yasaki wak'ar because, i luv u. Wannan wak'ar Bobo ce dayake bala'in so sosai, ya Hamza yabada wak'ar asaka Dan Bobo.
   Aikuwa sai sakin lallausan murmushi yakeyi danjin dad'in wak'ar.
   Masu hotuna kam sai aikinsu suke, itadai Rahma kanta yana k'asa tana shak'ar daddad'an k'amshin turaren Bobo.
  Bayan wak'ar tak'are aka fara gudanar da abinda ya tara mutane.
       Ammi tayi bayani da godiya ga d'unbin mutane dasuka halarci mother's Night d'in, sannan taima amarya da ango fatan alkairi.
    Rahma taji dad'in bayanin ammi itada danginta, wannan kad'ai ya isa yanuna mata dangin mijin nata suna sonta.
   Ankira  amarya da ango filin rawa, shuru sukayi kamar bazasu tashiba, kowa da abinda yake kitsawa a zuciyarsa, saida mc yasakeyin magana sannan suka mik'e ahankali.
    Afilin rawar suka tsaya k'ik'am babu mai motsi balle rawa, itakam Rahma dama bata rawa da dadai safan ce kam wannan gwanace.
     Bobo yafiddo rafar kud'i yafara lik'ama Rahma idonsa k'yam akanta, itakam kanta na k'asa, Dan danan guri yad'au ihu da tafi, jiki a sanyaye Rahma itama tabud'e fos d'inta danufin d'akko 'yan wazo d'inta saitaga kud'i dayawa.
   d'agowa tayi ta kalli bobo, shikuma yad'aga mata gira kuwa, da sauri tamaida kanta k'asa, yamatso da bakinsa wajen kunnenta cikin muryarsa mai taushi da laushinnan ya ce, "ko bakisone?.
  Ajiyar zuciya ta sauke itama ahankali ta ce, " ngd sosai".
   Hak'k'ine akaina aii yafad'a idomsa agefe kamar bashi yayi maganarba.
   Batace komaiba itama tazaro kud'in tafara lik'a masa gashi yamata tsawo, amma ahaka taringa masa lik'i ihun mutane da tafi yak'aru, masu hotuna da video sai haskasu sukeyi.
   Ammi ta taso itama ta rungume Rahma tana saka mata albarka, tafara lik'ama Rahma 'yan dubu dubu, (abin na manyane masu karatu), Bobo ma yakoma lik'ama Ammi sai murmushi yake saki itama Ammi haka, Rahma kam kanta ak'asa itama tana lik'ama ammi.
  Su yaya sulaiman ma suka taso, dandanan gurin ya kaure da lik'i kamar ba'asan ciwon kud'iba, k'awayen ammi da danginta duk suntaka rawar gani, hakama dangin Rahma ba'a barsu abayaba, kai wannan taro ya k'yatar masha ALLAHU.
  *_(can na hango Aunty bilyn Abdul tana lik'a 'yan naira 5🤣😜🤐, ba ruwana kartajini)._*
  _karfa kuce nina fad'a🤸🏻‍♀_

Sai k'arfe 11:30pm taro yatashi lfy, kowa yafara k'ok'arin tafiya, Rahma duk barci yacika mata ido, cikin mota take zaune tana jiransu bobo sugama sallamar bak'i shida yayunsa, saida kuwa suka gama sannan suka shigo, yanzu kam wani d'an uwansu bobone zai maidasu ba ya Hamza ba, su ya Hamza matansu suka d'auka da yaransu sukayi gida.
   Rahma ta kifa kanta kan cinya harta fara barci, kallonta kawai yayi baice komaiba, shifa koma sunanta bai saniba, bai tada itaba har sukaje gidan.
    Yay shiru yana tunanin yanda zai tasheta.
  Lukman ya kallesa Bobo kona baku gurine?, a'a malam wane kabamu guri gida zata shiga, ita barcima takeyi.
  To ka tada ita dare na k'arayi shabiyu saura fa.
   Daurewa yayi yad'an ta6a bayanta, ko motsi batayiba, yakuma d'an bubbugawa, firgigit ta tashi da addu'a abakinta, tad'an kallesa, shima idonsa na kanta, munzo yafad'a akasalane.
   d'auke kanta tayi tabud'e motar, saida safe tafad'a cikin muryar barci, harta rufe motar Lukman ya ce, "haba malam aii ka rakatadai kasani kotanada magagin barci.
   d'an tsaki bobo yayi shima yafito, harta fara tafiya yad'an hanzarta ya cimmata, dama ita kad'ai mai gadi yake jira Dan haka k'ofar abud'e take.
  Dariya Lukman yashek'e da ita, sai Bobon Ammi yafad'a harda dukan sitiyari.
   Har k'ofar falonsu yarakata, saida takama k'ofar zata bud'e sannan ta ce, " saida safe.
   ALLAH yakaimu yafad'a yana juyawa.
   Amota yasamu Lukman yashiga gaba suka wuce gida suma..........


ABDUL-MALEEK (BOBO)Where stories live. Discover now