Chapter 21

81 1 0
                                    


💫💫💫💫
          _*MEE'AD*_
                   💫💫💫💫
            
               

    

           ***CONTINUE***


*PERFECT WRITERS' ASSOCIATION*🌞

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

*THE BOOK IS WRITTEN*

*BY*

*_HAUWA IBRAHIM MISAU_*

Follow me on wattpad
👇👇👇
@hauwancyy44.

 

        JINJINA & SADAUKARWA

Na jinjina na kuma sadaukar da wannan littafin na gareki babbar aunty SAFNA ALIYU JAWABI Allah ya kara daukaka, basira da kuma fasaha ya kuma kareki da sharrin dukkan mai sharri. Ameeen .
 

√√√√√ MEE'AD fan's kuyi hakuri da rashin post akan time, sbd wasu dalilai. √√√√√√

         
     
**** Pls don't forget to vote, share & comments 👌 love u fan's 💯%.
          

37 ~ 38

Safiyar lahadi! baki d'aya illahirin mutanen gidan zaune suke a falo cikinsu harda Hajiya Hindu da jikanunta twins, ba 'abinda suke sai fira da tsokanan juna musanman Majeed da Mee'ad yayinda Amal take can gefe d'aya zaune kusa da Hajiyarta sai ya tsine fuska suke.

Hajiya Hindu da twins suna zaune kusa da Majeed ita kuma Mee'ad tana kusa da Mommyn ta.

Bayan wadansu lokuta Daddy da Abba suka fito suna fira zama sukai kusa da Hajiyarsu suna tsokanar ta. daria suke sosai sai da suka sha hira kafin Daddy ya gyara zama yace Hajiya nasan kinsan abinda ya taramu anan dan haka muna neman addu'arki.

Murmushi Hajiya Hindu tayi kafin tace idan baku manta ba tin lokacin da Allah yayima Alhaji rasuwa na baku umurnin hade kai tare da shawara da junanku kuma naji dadin wannan hadin kan naku Allah yayi muku albarka.Ameeen sukace baki d'ayan su.

Daddy ya gyara zama sannan ya dubi Majeed dake gefen Abba kafin yace Abdulmajeed kai yarone na gari mai cikakken ilimi da tarbiyya. kuma kai dane a gare mu meyi mana biyayya wannan halayyar taka ce ta janyo hankulan mu har mukaga ya dace mu hadaka 'aure da babbar d'iya 'a garemu wato Amal. mun baka aurenta munsa rana nan da 3month bayan kaje gida kafin ka wuce America sai a daura 'auren ku wuce tare.

Murmushin jin dadi Majeed yayi kafin ya furta kalmar Alhamdulillahi a cikin zuciyarsa. dukar dakai kasa yayi kafin yace Daddy na gode sosai kuma na karbi hadin da kuka yimin ina rokon Allah ya sanya 'alkairi ya kuma za'ba abinda yafi alkairi naji dadin hakan sosai Allah ya kara rufa 'asiri.

"Baki dayansu suka 'amsa da Ameeen.

Abba ya ce Allah yayi maka 'albarka ya kuma sanya 'alkairi da 'albarka cikin wannan hadin.

"Ameeen Majeed ya ce.

Gyaran murya Hajiya Hindu tayi kafin tace to kunji ta bakin Ango amma banga kunbi takan Amaryar ba.

Daria sukayi kafin Daddy ya ce aitin a jiya mun gama da fannin Amarya kam yanzu lokaci kawai muke jira.

Mee'ad dake gefen Mommynta sai a lokacin ta mike ta nufi wajen da Amal take zaune kama hannunta tayi fiskarta cike da murmushi tace na tayaki murna yar uwata Allah ya sanya 'alkairi. tana gama fadin haka ta nufi sama zuciyarta cike da damuwa. Majeed yabi bayanta da kallo zuciyarsa cike da sake ~ sake.

MEE'ADWhere stories live. Discover now