*silah*
*na khairat up*
*30*Washe gari kam sun sha kayan break fast da suka gama tayi cikin gidan su da murna abbu ya tarbeta shi da taufeeq ya kasa nutsuwa harda JB
Ya na makale da hannun ta ya ki barin ta sai kallon ta yake yana jindadi ta ce ya akai yi ne ya ya JB ?
Kawai kin min kama da irin hajiyoyin nan masu daula kin yi kyau noufal na kula da amanar sa naji dadi da kika saki jikin ki kuma kika yi moving on am so happy for you ki cigaba da addua all will be ok insha Allah!.
Murmushi kawai ta masa kowa yana ganin kaman ita da noufal suna rayuwa irin ta ma'aurata ne bayan su abota kawai suke yi.
Yan biyu ma sun shigo ana shiri dasu na biki taji dadin ganin su ita ta manta ma da wani fada da aka yi a da can kan wani noufal sai saddiqa wanda ta maida abin wasa.
Kowa DEAR kowa ita abub haushi yake bata sossai amma ta dake
Yanzu ma kasuwa take son zuwa ita da saddiqa yin siyayya dan anjima za ayi kamu .Ta gama shirin ta tsaf ta fito ta dau wayarta
Se ina in ji mommy?
Kasuwa zamu yanzu zamu dawo nan nasarawq zamu karasa kusa da gida kawai saboda goslowTo ayi dai sauri a dawo da wuri dan kun san bama san wani african tima ko
Insha Allah mommy yanzu zamu dawo ba a wancan filin na abbun za ayi ba tunda shi de ya muby second hand ne kuma second marriage
Dariya tayi tace kin zama gulmammiya DEAR second hand ko zaki sani kaman a kunnen shi
Muje sayyada kar ma yaya ya shigo ya gan ni nasan ze iya hanawa dan be son zuwa kasuwa
Muje to
Sun shiga mota suka yi waje da sauri
Aiko basu yi minti biyar da fita ba ya shiga gidan shi da su taufeeq harda angon se smiling yake yi
Oh su mubarak anji kunya kayi a hankali mana se blushing kake yi bsyan wata tace kai second ne
Dariya yayi yace mommy in kina bin ta DEAR zaki yi hawan blood wata ran ki kyale ni da ita zata san second !
Aka sa dariya
Naji shiru sun fita ne
Wani irin shiru duk mutanen da suke cikin gidan ka taba ganin gidan biki shiru?Uhm'uhm ai wai ita talkative din nake nema
Taje kasuwa yanzun nan suka tafi ita da sayyada amma nan kusa .
Noufal na jin wai sun tafi kasuwa yaji wani iri fita ma tayi bata tambaye shi ba??
Wayarsa ya zaro ya kira layin ta
Tana gani taki dauka tasan fada ze mata yayi ta kira ta masa biris
Haushi ya cika shi dake dan duniya ne se be nuna ma kowa ba aka shiga komai da shi.
🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡🍡
An yi decorating komai yayi kyau an na ta shagalin biki
Fadar yadda kannan ango suks yi kyau second time ma bata baki ne
Anyi komai an gama an sha rawa musamman ma DEAR kamar zata balle dan rawa.
Haisam yace wannan yarinyar ko ina ga ana sa mata battry ne in dai tana rawa wata ran zata balle kwankwaso su mata burin su aje biki suyi rawa shi kawai suke so
Tashi yayi ya fita waje amsa wata waya
Ya gama kennan ya juyo yaga mutum a bayan shi juyowa yayi ya ce lafiya dai ko?
Uhm
To ban hanyaYi hakuri bawan Allah ka taimaka ka saurare ni kaji
Ina jinki na baki minti 5 ki fadi menene?
Wallahi tunda kuka shigo naji ka burge ni ina son in bazaka damu ba ka bani number wayan ka
Kallon ta ya kuma yi up n down sannsn yace kiyi hkr baiwar Allah ina da aure
Dariya ma ya bata
Na sani ai noufal kana da aure kuma wadda ka aura na san ta ba wai ina son muyi soyayya....Juyo da ita aka yi cikin azama da sauri ta kalleta hannun ta cikin nata dan zafi tace wace haka cika ni
Waya ce ki tsaya da miji na mufeeda?
Saboda zan amsa number shi
Mari ta zuba mata wallahi karya kike munafuka shegiya mara aji shi ne kika biyo shi waje mayya kawai bar nan kamin na karasa zubda kafaffuwan ki
Ni kika mara
Eh ko xaki rama neBazan rama ba amma zaki san baki yi daidai ba
Ta juya ta yi waje ko gun bikin bata koma ba
Shi kuma mamaki ya cika shi *kishi* shi ne abunda ya fada ya na kada kai lallai ma wannan
Ya hade rai ya ina hira zaki kora min budurwa
Hararshi tayi sannan tace wallahi ka cuce ni karasa wadda zaka tsaya da se wannan abar?
Ni ta min kyau wallahi zan bita na amsa numberta
Ai kuwa ta saki kuka ta zauna a kasa da sauri ya dagota me haka ke wai har yanzu yarinya ce kin girma fa komai kuka yanyanyan kaman wata baby gurl!
Hararshi ta kuma yi
To ke ina ruwan ki naga ba sona kike ba ko ?
Kinga ki barni na yi rayuwata wallahiKeda zan baki takardar ki zaki sake aure ni kuma fa ?
Au da gaske se ka sake ni
Eh mana ai ni abokin ki ne kuma yayyan ki sannan kuma baki maida ni miji ba
In ji wa?
In ji ni mana saboda me dazu kika fita baki fada min ba kuma kika ki amsa waya na nasan kuma kin gani wallahi!.
Shi kennan kaje kayi ta zancen nima zan yi saurayi ai
Zata shiga ya fizgo ta ya na mata wani irin kallo ya hadata da jikin mota
Ahhh cika ni dan Allah yaya zafi fa wayyo!
Ni zaki ce ma xaki yi saurayi kema ?
Wasa nake yi maka fa
Karya kike yi
WallahiKe ni kin ga bara ma na fada miki gaskiya ni ba sakin ki zan ba ina son ki ina son ki ina sonki ki ma daina sawa a ranki cewa ni xan sauwaka miki ko daya dan nida ke mutu ka raba wallahi koda wasa na gan kida wani katon Allah zan mata matsayin ki
Ya doki jikin motar da karfi
Ban san mesa mace in kace kana son ta ba se ta raina ka i cant take this any more kowanne second na bugun zuciyata da ke yake bugawa ya zaki dinga min haka ni ina kaunar ki ina kishin ki ni kuma kin kasa ganewa ban san me kike so ba a rayuwa
Ki fada min yau ni nine ba kya so ko kuma wani kike so?
In kuma dan hilal ne ai ya bar duniyar kuma ya bani amanar ki ya ce na kula dake kema ya baki tawa mesa baxaki yi abinda yake so ba!.Kuka take yi kawai
Ok kuka to naji kije khairi na daina takura miki amma ki sani ban rabuwa dake kuma wallahi kika yarda wani ya kula ki ya miki magana hann zaki yi remembaring wannan ranan na fada miki.Ya shiga motar sa yayi reverse sekuma ya tsaya
Fitowa yayi ya ja hannun ta ya shige da ita cikin motar ya kulle ya mata key se gida kuka kawai take yi.
YOU ARE READING
Sila
RandomAmma kin san akwai karatu ko ko kyalkyalen banza kike so Ni de aa wallahi bazan iya ba Ta mike Ya biyo ta *DEAR* ta juyo yaya na gaji tafiya xan yi. Ki xauna anjima kadan zan yi lec in nayi sallah se mu tafi tare Yaya da mota nazo Ni yau da nap...