part 5

2.3K 159 10
                                    

[6/20, 10:52 AM] 😘Um Nass🏇🏻: *HADIN GWARMAI* 🎊

©by *😘UM NASS 🏇🏻*

*Follow mee on Whatppad @UmNass*

® *NAGARTA WRI.ASSOCIATION.

_"Alhmdlh Alhmdlh in sha Allah na dawo xan ci gaba.,ina mana barka da sallah da ftn Allah ya kar6i ibadinmu da mukayi acikin watan da ya gabata Ameeen."_

Page 8

Kai tsaye suka nufi kwandostan motar dake faman ambatar Kano.
"Zamuje kano malam INA motar da xamu shiga?"
Maganar da Abdallah yayima kwandostan Wanda yasashi washe bakinsa "a a Bismillanku to ga motar can."
Nuni ya musu da hannunsa kana yayi gaba zuwa ga motar cikin hanzari suma suka bishi.
Cikin sa'a suka tadda saura mutum uku motar ta CIKA Wanda suna shiga wani yazo shima ya shiga.
Kudin motar Kwandosta ya shiga kar6a har sai da ya kar6i na kowa sanan ya miqama Direban ya wari abin da xai basu.
Tuni Direban yazo ya shiga ya kunnata bakinsa dauke da bismillah,.
Abin da ya qarama su Abdallah nutsuwar xuciya jin Addu'a abakin wanan Direban wanda abune mai wahla jinta abakin Direban tasha.

Tafiya suke cikin kwanciyar hankali, baka jin komi sai surutun mutunen motar Wanda har baxaka iya tantance nawa xaka jiba.
Domin kowa buqatarsa nasa ya xama mafi rinjaye ga mutane.

Tafiya tayi tafiya Wanda mafiya yawan mutanen sunyi barci saboda Nisan dake tsakanin yobe da kano ba kada bane.
Idan ka dauke Direba da yake tuqi sai kuma Abdallah Wanda ya shiga kogin tunanin yanda rayuwarsu xata kasance akano ko da dadi ko kuma akasin hkan.

Yini guda suka cinye ahanya kafin su fara hango gine ginen garin kanon Wanda mafiya yawansu dauke suke da tambarin kwankwasiya akansu.

Tuni mutanen da sukayi barci sun tashi zaune suna bama idanuwansu abincin.

Baki Abdallah ya saka yana qara bude idanuwansa ganin mutane birjik ta ko INA da dai duniya sai kace ba'@ mutuwa.

Ahaka suka rinqa kutsawa duk da yawan go slow din da yake tsayar dasu har suka shiga tasha.
Ananfa kowa ya fara qoqarin sauqa domin xuwa inda xashi.,sai fa Abdallah da Umminsa da Sukayi curko curko na rashi sanin madafar inda xasu.

"Abdallah gamu a Kano gari mai cike da mutane Wanda kowa rayuwarsa yake, yanxu INA xxamu nufa?"
Idonsa ya rufe ya bude ahankali kafin ya saita muryarsa Wanda take dauke da fargaba,domin azahiri shi tsoron yawan mutanen da yakega agarin yake balle kuma tashar ma da take cike da mutane,."kafin wanan tunanin mu nemi abinci muyi sallah Ummie domin yunwa nake ji sosai ga sallah kuma da muka Tara akanmu."
Kai ta jijjiga alamar gamsuwa kafin sun hango wata dattijuwa mai diyar da abinci Wanda mutane sukayima qawayana alamar jira.
Qarasawa kusa da ita sukayi bakinsu dauke da sallama.
Amsawa mutanen wajan sukayi kafin nan suka maida hankalinsu ga mai sai da abin cin.

"Mi kuke so abaku?"
Ta Jefa tambayar tsakanin Ummi da Abdallah Dan ganinsu da tayi ya tabbatar mata su din baqi ne.
500 Abdallah ya miqa mata gami Da Dan rusunawa "Abinci xaki bamu,ko wani iri ne bamu da xa6i."
Kallonsa take ganin fiskarsa dauke da murmushi da kuma girmamawa acikin mgnrsa.

Shinkafa da miya ta zuba musu hadda kafi Wanda da alama ta zarce yawan Adadin kudin nasu.
Sanan ta bude wata kula akusa da ita ta miqo musu robar zo6o mai sanyi guda biyu.,
"Gashi kuje can kuci akwai ruwa da makewayi idan kuna buqatar yin sallah." Ta fada musu fiskarta dauke da fara'a Dan sosai mutanen suka shiga ranta duk da ba wani mgn sukayi da ita na tsawan lokaciba.

Godiya suka shiga yi mata Dan wanan karamcin yasa sun samu wani qarfin gwuiwa akan lallai sun shigo kano da qafar dama.
Karo na farko an girmamasu an kuma yi musu maganar cikin fara'a da sananin kimarsu....

_Tofa rider's gamu acikin Kano ga kuma sauqaR da aka fara yima Abdallah.,da alama qarshen wahlarsa ta xo....._

_Ku dai ci gaba da bibbiyata amma kuyi hqr ganin page gajere sbd muna fama da rashin NEPA_
*Marsalar Dan 9ja kenan 🤥*

HADIN GWARMAI CompletedDonde viven las historias. Descúbrelo ahora