part two

3.2K 211 4
                                    

*HADIN GWARMAI🎊*

*©😘Um Nass🏇🏼*

® *NAGARTA WRI.ASSOCIATION*

PAGE 2

"Murmushi Maa tayi gami da girgiza kai "Bazaki sauya ba khaleesat,har yanzu babu abin da ya rage a tare da ke na 'kuruciya dangane da 'kiyayyar da kike ma abinci."
Mi'kewa itama tayi domin zuwa tarar mai gidan nata,adai dai lokaci kuma aka turo 'kofar falon gami da yin sallama.
Wani Hamsha'kin dattijo ya shigo fiskarsa dauke da murmushi kallo daya zaka masa kasan ko shi waye saboda yanda jikinsa da kayan da ke sanye atare da shi ya nuna asalin ko shi waye,kana ya fiddo da tsagwaran kwarjinin dake a tare da shi.
Kasan cewarsa shugaba agidan da kuma zamansa a matsayin governor Na jahar kano Alh.Muhammad Dan yaro kenan.hannunsa riqe Dana khaleesat tana faman zuba masa surutu Wanda mafiya yawanta tambaya ce akan labarin inda yaje da kuma tsarabar da ya kawo mata.

Sosai yake biyeta yana mata dariya duk da tarin gajiyar da ya kwaso ajikinsa.
Da sauri Maa ta tareshi tana 'kara fad'ad'a murmushinta ayayin da gefe daya take aikama da khaleesat harara,dauke kai tayi daga kallonta taci gaba da surutunta
"Barka da zuwa your excellence"
Murmushinsa ya fadada gami da samawa Kansa mazauni acikin manyan kujerun da suka 'kawata palon
"Barka kadai Ru'kuyya, ya na sameku?"
Ya amsa mata lokacin da ya daidaita zamansa har yanzu hannunsa ri'ke suke dana khaleesat ta 'kara cukuikuye sa kamar zai gudu ya barta.
"Alhamdullah lafiya lau.
"Da alamar ka debo gajiya,.ita kuma wanan magen zata 'kara maka wata gajiyar da shegen surutunta,da son jiki".
Murmushi yayi kana ya kai kansa ga diyar tasa Wanda maganar Maa ta sata turo baki alamar jin haushin kiranta da magen da tayi

"Dady kana jin Maa tana kirana da mage ko?"
Shafa kanta yayi yana dariya saboda yanda tayi maganar 'kiris hawaye ya zuba a idanuwanta
"Ki 'kyale maa ni Na tabbata kee ba mage bace."
Juyo da kallonsa yai ga ita ya sauya fiska
"Inaga kina takurama uwata idan bana nan Rukayya hakan yasa Sam bata Sakewa da ke,ki duba fa kamar ta shekara bata ganniba nasan kina barinta cikin kadaici kina sabgar gabanki da sauran yaranki."

Baki Maa ta saki tana ganinsa ayayin da khaleesat ta qara shigewa jikinsa tayi luff kai langare kamar marayan da ya rasa danginsa alokaci guda.
"ikuwa ba'a zageniba idan ba'a gode minba kullum ina fama da ita kamar yaron goye ko abinci kafin taci sai mun gama kewaye gidan nan da ita.,yanzu hakama mgnr muke taji shigowarka ta ruga da gudu."

Kallonsa ya Kai gareta yana girgiza kai "Assha har yanzu bakya cin abinci uwata ko asibiti zan sake fitar da kee adubaki."
Da sauri ta girgiza kai "a'a dady yau ne kawai ban ci abincinba fa shima dan ban dade da tashi abarci bane."

Ajiyar zcy y sauqe "to kinji dalilinta ai sai ki bar matsa mata."
"Kai har ka yarda kenan?"da mamaki tayi tambayar.
"Sosai kuwa uwata ai bata 'karya"
Jijjiga kai tayi "Allah ya kyauta to.Abinci zaka fara ci ko zakayi wanka ne?"
Idonsa ya kai sama kamar mai nazari can yace "wanka dai daga baya naci abincin.,"kai ta gyada sanan ta nufi hanyar da xata sadata da dakinsa hannunta riqe da "yar 'karamar jakarsa "bari Na hada maka ruwan wankan."
Tashi yake 'ko'karin yi "yauwa uwata daga ni nayi wanka ko? sai nazo muci abincin tare."
Gira ta daga masa kana ta sakeshi ba tare da tayi mgn ba.
Murmushi yayi yana girgiza kai babu wani sauyi atare da rayuwarta sai dai duk da muskilanci irin nata wani lkc tana zama suyi hira sosai."

Lokacin da ya shiga daki tuni Maa t hada masa ruwan wankan.,taimaka masa tayi wajan cire kayan jikin nasa.
Kollonta yake "Nagode Ru'kayya har yanzu babu abin da ya sauya a halayyarki,lokuta masu yawa sai nake tuna rayuwarmu a baya,inaga babu Wanda ya kaini dace da samun mace ta gari,duk da ayanzu bana Samunn lokacin zama tare da ku hakan bai hanaki gajiyawa da hidimta minba."

Murmushi tayi mai kyau"wa yake gajiya da Neman aljannarsa? har abada zan ci gaba da shimfide rayuwata wajan hidima agareka, mut'kar hakan zai saka farin ciki"
Kai ya girgiza "Na yarda da wanan.,"
Hanyar toilet din ya nufa "saura kizo ki min wankan kuma."ido ta fidda waje kafin tayi dariya sbd tuna rayuwar da ta shude abaya kafin ta fiddo masa kayan da zai saka.

HADIN GWARMAI CompletedTempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang