BABI NA SHIDA

139 3 0
                                        

😭😭 *K'ANWAR MAHAIFINA* 😭😭

®☄
*GASKIYA WRITER'S ASSOCIATION* ✍

{Gaskiya d'aya ce daga k'inta sai b'ata, burinmu mu faɗakar da al'umma domin ribantar duniya da kuma lahira. }

              🎐 G• W• A🎐
*GASKIYA DOKIN K'ARFE*🏇


*LABARI*: MISS XERKS🌺

*RUBUTAWA DA TSARAWA*:

SERDEYERH LERWAN
( *UMMU HANASH* )

~Wattpad @ Deeyam2781~

*SADAUKARWA GA*:
*IYAYE MAZA*.❤
('''Allah ya saka muku da gidan aljannah''')

📓 *2019* 📓

*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*

'''Dukkanin abinda zakuji a cikin wannan littafin gaskiya ne, bawai kagahhe bane, dukkan al'amarin da zai faru acikinsa kama daga arzik'i ko talauci gaskiya ne babu batun k'arya sunaye kawai zan canja sai dan abinda baza'a rasa ba. '''

*Mai gwaza nd maman adnan (masoyiyar) ummu hanash na mik'a gaisuwa gareku*

~Am Back~

*BABI NA SHIDA*




*__________📖* Sak'on sa na biyu ya shigo wurin k'arfe 1, ina dubawa naga, ina cikin wani hali ni Abida.

Da sauri na fita daga b'angaren message na kirashi, maganarsa k'asa-k'asa ya masa min sallaman da nayi masa, sai naji muryar na ta sauyamin ba kamar yadda na saba ji ba.

Tambayarsa nayi sai naji yamin shiru, can sai naji muryarsa alamun yana kuka, hankalina a tashe nake tambayar sa, duk tambayoyin dana masa masa d'aya ya bani ta cewa.

"Bakomai".

Ban gaji dayi masa magana ba, nan na k'ara ce masa.

"Kaje gida lafiya?".

"Lafiya k'alau".

Tambaya na sake masa nace.

"meya faru naga Umma tana kiran ka"?.

"Bakomai,daman bak'i mukayi ne daga pataskum shine takemin wanann kiran nazo suna tambayata".

"Ayya ayi musu sannu da zuwa, amma dai da safe zaki zo ko, kuma dan Allah ina rok'onka kada kada wani abu a zuciyar ka".

Nan dai mukayi sallama irin ta masoya.

Washe gari dana tashi da safe ba kuwa a gidan, domin Abba har sun  tafi police station, yasa an kama Umma Asiya akan dole sai ta fadi dalilin da yasa ta aikata haka.

Anan cikin haka aka samu wani yaje ya sanar da Kakarmu abinda yake faruwa, nan take kakar mu ta kira Abbana akan cewa idan har ya sake ya tozarta mata d'iya wato (Umma Asiya)to wallahi sai ya sani, nan Abbana babu shiri ya janye k'arar da yayi.

Bayan kwana biyu da faruwar haka sai ga Abid yazo wajena,kana kallon sa kasan yana cikin damuwa sosai, tunda na kalleshi naji gabana yana fad'uwa, a cikin zuciyata na fara cewa, Allah yasa shima ba rabuwa zamuyi dashi ba.

Tab'a nin da yayi shine na dawo daga tunanin dana tafi, nan na fara jero masa tambayoyi na meke damunsa ko bak'in da akayi ne, ko kuma Umma ce tace wani abu.

Tsayawa yayi yana kallona becemin komai ba, haka naci da magana

"Abid nice ko?".

Girgizamin kai yayi alamun Aa.

Magana na k'ara masa a cikin shagwab'a cewa.

"Nasan kai ma cewa zakayi, zaka rabu dan...".

Ban k'arasa maganar ba yayi saurin juyowa ya kalleni, hannunsa yasa ya jiyo da fuskata yana kallona yace.

"Uhmmm"

Da Ummmm nace masa nasan nace.

"Nasan lokacin rabuwar mu yazo, kuma nasan kaima baraka so ka auri mai iska ba, ina maka fatan alkhairi a cikin rayuwar ka tare da samun mace ta gari wadda ta fini".

Kuka naji ya fashe dashi,nima nan take na fara masa kuka, ji nayi ya  jawoni jikinsa yana bubbuga bayana alamun nayi shiru baya son kuka da nake.

Sai da muka d'auki kusan 30 minutes a haka sannan ya sakeni, in banda ajiyar zuciya babu abinda nakeyi.

Can nai yace "Bakomai,amma maganar da kika fad'i gaskiya ne kamar kin shiga raina kinga abinda zan fad'a, akan ki Umma ta kirani tamin magana, indai tana raye ti baran aureki ba, kuma koda bayan mutuwarta bata yadda na aureki ba, bata yafemin ba idan har na auri yar....".

Saurin rufe bakinsa yayi saboda bare iya dangan ta ni da wannnn sunan ba.

Haka na tashi na shiga cikin gida na sanar da Mamana abinda ake ciki, itama cewa tayi shikenan babu damuwa Allah yasa hakan shine yafi alkhairi a gareni.

Bayan Abbana yaji abinda ya faru, nan yasa Brother d'ina yakai shi gida, da yake da zezo bezo da motar sa ba.

        

            ********

Haka rayuwa taciga da tafiya, na na yankewa kain na daina soyayya har abada saboda abubuwan da yake faruwa dani, sai dai kuma ban fitar da rai ba a wajen Ubangiji na ba, da samun sauryin da zan shiga nan ba.

Akwai wata k'awar Umma Asiya da tazo wajen Mamana take ce mata akwai dalilin da yasa Umma Asiya tayi wannna asirin.

Umma Asiya tana da d'iya mai suna Maryam, Mamarmu ce ta rik'e ta tun tana k'arama, duk wani abu da uwa zata yiwa yarta haka Mama take yiwa Maryam.  Haka muma muka taso tare bama nuna mata ban-banci a tsakanin mu, duk da ta fimu haka muke bata girmanta.

Lokacin da Umar Faruq yazo wajena yana sona, ashe Maryam shi yake so, ni duk ban sani ba.

Haka daya tafibta bishi ta sanar masa, shikuma ya nuna mata bata masa ba, ganin haka ta fad'awa mahaifiyar ta.

Shine Umma Asiya tace matuk'ar tana raye sai Faruq ya auri maryam, sai ta raba tsakanin mu dashi.

Haka ta shiga ta fita da rabamu da shi, sai Faruq ya dawo suna ta Soyayya da Maryam da yake an riga da anyi masa asiri kuma ya kamashi.

Da yake Allah ba azzalumin sarki bane, sai asirin da aka yiwa Faruq ya karye har yazo yayi aure, basu sani ba, sai bayan auren suka sani, shine tace ta d'auki alwashin barata tab'a barin nayi aure cikin gidan zanji dad'i ba, sai dai na auri talaka.


'''A kullum ni mai laifi ce agareki na rashin yi muku typing akan lokaci, ina mai baku hak'uri, sannna ban so nake yawan typing din book dina nan saboda a duk ranar dana yi typing sai ya sani kuka sosai, saboda irin abubuwan da Abinda take fuskanta''''


*Ummu Hanash ce*✍

You've reached the end of published parts.

⏰ Last updated: Jan 06, 2020 ⏰

Add this story to your Library to get notified about new parts!

K'ANWAR MAHAIFINAWhere stories live. Discover now