chapter 7

10.8K 146 30
                                    

💗💗💗💗💗💗
         SON RAI
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

             ~NA~

*AYSHA  A BAGUDO*

     ~DEDICATED TO~  
      HAJIYA MARYAM 

     _(JIKAR KULU )_

*Tun a  farkon tafiyar nasan ke din masoyiya ce  ,na saudakar da wannan labari gareki domin  Kin cancaci fiyye da haka agurina ,kin nuna min kauna ta gaskiya ,kin soni da zuciyarki da gangar jikinki ,babu abinda zance sai godiya 👏🏻 Allah ya barmu taren tare, Allah  ya rabamu da sharrin mayun media , Allah ya raya mana mardau's"*

warning!!!

don't read my  novel , if you know ,you are not married... ❌❌❌coz  oll my  book contains only for mature people ,
if you   read it, is for   your own risk  ooooooo ......🙅🏼‍♀️

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim 


Page 7

"Wallahi umma  ba turaren kowa ne a jikina ba, Wanda nake amfani dashi "

"Karya kike yi , dan ubanki wannan ba  kamshi turarenki bane ,ta jijigata tare da  makata akan kujerar three sister har school bag dinta na fad'uwa  "ni zaki yiwa karya yesmin ?
"Yesmin bin maza kika fara?
" ko wasa da maza kike yi school ?

Cike da matsanancin tsoro da gigita  tace "Allah umma ba..bana bin maza "Kuma bana wasa da maza "

"To kamshi  turaren uban wa nake ji a jikinki, wannan dai ba kamshin turaren da muke amfani dashi bane a gidan nan , zaki gaya min gaskiya ko kuwa  sai shake miki wuya  na kasheki ?

Jikinta na tsuma while hankalinta ya sake tashi, ganin mahaifiyarta na k'ok'arin ,gano wani Abu a  dangane daita "kiyi hakuri ..!
"kiyi hakuri !! umma , ni dai bansan nayi amfani da wani turare bayanmu wanda na fesa daga gida ..

Aiko mahaifiyata tayi kanta gadan gadan tana k'ok'arin take Mata gefen ciki ,sai ga habib ya sanyo Kai cikin parlour'n, da sauri ya k'arasa ya shiga tsakani "kina hauka ne hafsat  ko me ?
"Yar tawa guda da Allah ya mallaka min duniya da lahiri kike k'ok'arin kashe min ta ?

Hafsat  mahaifiyar yesmin ,ta tsaya tana dubansa ranta idan yayi dubu to ya sake 'baci , gabad'aya ilahirin jikinta rawa yake taji haushin dawowarsa ,taji haushi da bata ci kaniyarta ba kafin ya shigo ,dan tasan babu abinda ya tsana a rayuwarsa  kamar dukan yaran , bare yesmin  daya d'auki soyayyar duniya ya d'aura mata "

"Kin yi shiru kina kallona kashe min ita zakiyi ko kike nufi ?

Naunayen ajiyar zuciya ta sauke saboda ganin yadda ransa ya  'baci ,sannan ta girgiza masa Kai al'amun a'a kana  ta soma magana cikin fushi  "yesmin bata jin magana .....
"Zataji da izinin Allah "
 

" kullun furucinki  bai wuce bata jin magana  ,ta'ba jin magama ba , dukan da kike mata  bashi zai sa taji ba ,nasiha shine farko ,ni dai gaskiya bana son wannan duke duke duke , ya k'arasa maganar yana duban yesmin  dake rawar jiki "me kika mata take neman kashe min ke ?

Yesmin ta sunkuyar da kanta  tana zubar da hawaye sannan muryarta can kasa kasa tamkar mai koyon magana tace "dady Wai ...Wai ...sai Kuma  tayi shiru ta kasa k'arasawa "Wai me ?

Tayi shiru taki cewa komai ,sai numfashi da sheshekar kukanta ke tashi a parlour'n ,habib ya waigo inda hafsat  take tsaye cike da matsanancin jin haushinsa  yace "me tayi miki ?

"Sai yanzu zaka tambayeni abinda tayi ?
"Cikin ni daita wa yafi cancaci ka tambaya tukuna ?
"Gata nan sai ta fad'a maka abinda tayi "tana gama fad'ar haka ta juya ta  shige d'akinta ta banko kofar da karfi tana haki ..

SON RAI Where stories live. Discover now