AƘIDA TA

939 42 2
                                    

_*AƘIDA TA*_

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

ELEGANT ONLINE WRITER'S

PART1
Page 5

Yusuf ya fita yaje yai alwala yai salla saboda lokacin salla yayi.

Widad kam tana zuwa ɗakin ta ta jefar da Jakarta da wayar ta akan gado ta fara safa da marwa a ɗakin ta

"Bulama ina ganin girman ka, ina maka kallon uba amma kana ƙoƙarin ƙetare gona da iri, kana ƙoƙarin tsallake iyakokinka, a tunanin ka yin Aure ze sa in canza ra'ayina? Daddy kunyi kuskure daga kai har Bulama, kuma bazan taɓa bari wannan kuskuren naku yayi tasiri a kaina ba, dole inyi wani abu" haka ta cigaba da surutai ita kaɗai.

Hajiya Halima ta kalli maigidan ta tace "Nikam wai Alhaji dagaske Widad zakayi wa Aure ko kuma yaya? Na kasa gane kan lamarin"

Ɗan shiru yayi sannan yace "Eh hakane, Bulama ya bani shawarar akan cewa muyi mata Aure hakan ne kawai zesa ta canza wannan halin nata, Amma yarinyar nan kin san halin ta da kafiya da taurin kai, ta tirje tace sam bata san zancen ba, Amma a wannan karon bazan canza ra'ayi ba, ina son inga ta dawo da walwalarta, wannan karon dole tayi biyayya ga umarni na"

"Amma Alhaji baka ganin yin hakan tamkar ze ƙara tunzura rashin lafiyar ta ne, zaka ƙara sawa rashin lafiyar ta ya tsanan ta, ko ka manta sharuɗan da likitoci suka gindaya ne akanta?"

Alhaji Nasir Ya numfasa sannan yace

"Shima zaman ta a hakan bakomai ze ƙara mata ba face cigaba da dawwama a cikin damuwa da rashin walwala, akwai buƙatar ko bayan raina Widad ya zama na tana da kafaɗar da zata tada kai, ya zamana tana da wanda ze kula da rayuwar ta"

"Amma Alhaji wa zaku bawa Auren ta? ina fatan wanda zaku bawa yasan yanayin larurar ta? Tunda kaga ba shiga mutane take ba balle a ce tana da wanda take so, kar a bawa wanda besan ya take ba abu yazo ya ɓaci"

Alhaji Nasir yace "Ai ba wani bane za'a aura matan, fahad ɗin Bulama ne, itace dai batayi wayon saninshi sosai ba, rabon da su haɗu tun tana yarinya ƙarama, Amma shi ya santa kuma nasan baze bamu kunya ba Insha Allah, tunda itama tamkar ƙanwa take a gurin sa"

Jinjina kai kawai tayi ba tare da ta kuma cewa komai ba.

Wajejen la'asar Amal ta shiryo cikin wata irin doguwar riga wadda ta kama jikin ta matuƙa, se zuba ƙamshin turare take wanda turaren har hawa ka yake yi saboda ƙarfin sa ta hau kan wani takalmi me uban tsini, duwatsun jikin rigarta se ƙyalli suke suna rawa.

Cikin iyayi ta ƙarasa inda Yusuf yake zaune da su Nura da sauran ma'aikatan gidan tace "Yaya Yusuf mu tafi ko na shirya"
Ba musu Yusuf ya miƙe yayi wa su Isa sallama.

Ya karɓi mukullin Motar Amal, suka shiga mota suka fice.

Yusuf na barin gurin Murtala me bawa shukoki ruwa yace
"wai kunga abunda na gani ko kuwa?"

Nura yace "mun gani, kai kaga wata irin kwarkwasa da take masa? , anya yarinyar nan Amal ba san shi take ba? Kaga wani iyayi da take yi tana fari da idi"

Murtala yace "Amma kuwa da ta faɗo, duk zuƙa zuƙan Samarin dake zuwa gurin ta? duk iya yin da wulaƙancin nata ta ƙare a direba, wallahi da tayi faɗuwar baƙar tasa"

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now