AƘIDA TA CHAPTER 15

640 37 0
                                    

_*AƘIDATA*_

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

PART1
Page 15

ELEGANT ONLINE WRITER'S

Turus Yusuf yayi ya rasa me yakamata yayi? Me zeyi wanda zesa Widad ta yadda da shi, Amal ma da ta ƙaraso domin cimma Yusuf, tana ganin Widad itama tayi Turus ta shiga rarraba ido kamar an sacewa karya 'ya' ya.

Widad tayi wa Yusuf alama da hannu ya biyo ta, ji yake kamar ƙasa ta tsage ya shige, haka ya bi bayan Widad zuwa part ɗin ta, gaba ɗaya ya saddaƙar yana jiran jin ruwan masifa daga bakin Widad.

Ta kalle shi tace "nayi list na abubuwa da nake buƙata ne, za kaje ka siyomin, ka lura da duka abunda na rubuta bana buƙatar product ɗin basu nace ba"

Jiki ba ƙwari ya jinjina mata kai, ta ɗakko paper ta miƙa masa tare da ATM card, a sanyaye yasa hannu ya ksrɓa, amma harya juya zefita beji tace masa komai akan ganinsa ya fito daga sashin su Amal ba.

Har ze fita ya tsaya ya juyo ko zata yi magana, amma yaga tana danna wayarta, tana ɗaga ido suka yi ido huɗu dashi ta kalle shi tace

"Lafiya? Ka tafi mana"

Ya kalle ta yace "bakomai"

Ya juya ya fita yana sake waiwayen Widad ko zata yi magana.

Fahad ne keta shirya kayansa a trolley, Anwar ya kalleshi yace "Fahad ji nake kamar in bika mu koma Nigeria tare, amma ba yadda zanyi, munzo tare ka rigani kammaluwa"

Fahad yace "Ai kai ba komawa Nigeria ce ta dame ka ba, zuwa kaga wannan yarinyar ne ya dame ka"

"ƙwarai kuwa faɗi ka ƙara Fahad, ni kaɗai nasan abunda nake ji game da ita, nima ina nan dawowa ai Insha Allah, inga farincikin zuciya ta"

"Allah yayi maka magani, dan kaibnaga abun naka ka afka da yawa"
"kadai bari kawai, dan Allah Fahad kayi ƙoƙari ka samo min lambar ta idan kaje Nigeria"
Yatsuna fuska Fahad yayi yace "gaskiya ban maka Alƙawari ba, dan tamin rashin mutunci marinta zanyi"
Anwar yayi dariya yace
"da kuwa ka ƙare rayuwar ka a prison"
"kaini ka isheni da zancen yarinyar nan haba"

Ƙarshe Fahad ya fice ya barwa Anwar ɗakin, dan ba ƙaramin haushi yake bashi ba idan yana zancen Widad.

***********************************

"Ana ƙoƙarin a hallaka min ɗan uwana, sannan kuna min barazana da rayuwa ta, gefe guda ga yarinyar nan itama ta sakoni gaba, anya Alhaji Haruna kunmin adalci kenan?"

Alhaji Haruna yace "Adalci ɗaya za muyi maka Sale, kayi aiki nan na ƙarshe da muke so, in ba haka ba da kai da ɗanuwanka haka zaku ƙare kuyi biyu babu, tabbas muka samu abunda muke so zamu fidda ɗan uwanka, sannan baku ba na kusa da kuma seya azurta"

Saleh ya fesar da iska yace "kamar yaya? Yanzu dai ta tabbata kune kuja bawa ɗan uwana abunda yasa rashin lafiya ta kama shi, don ku kasheshi karya tona muku asiri"

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now