AƘIDATA CHAPTER 10

727 42 2
                                    


_*AƘIDATA*_

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P. W. A

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

ELEGANT ONLINE WRITER'S

PART1
Page 10

Shiru Yusuf yayi yana bin Amal da kallo, tare da nazarin maganganun ta.

"Waye ya kashe Mahaifiyar Widad? Me yasa aka kasheta!!? Meyasa ake bibiya da barazana ga dukkanin wanda yake da kusanci da ita!!!? Meye dalilin rushewar binciken wanda suka kashe mahaifiyar Widad? Meye Alaƙar kisan Mahaifiyar Widad da wanda Widad tasa aka ɗaure!!!? Meye alaƙar ciwon Widad da ƙwayar dake cikin tea ɗin da'aka kawo mata?

Wannan sune jerin tambayoyin da suka shiga kaiwa suna komowa a cikin ƙwaƙwalwar Yusuf.

Ta ɗago ta kalli Yusuf tace "let's keep this aside, Yusuf ka taɓayin budurwa? Ko kana da budurwa a halin yanzu?"

Jin tambayar Yusuf yayi wani banbarakwai, ta tuna masa da abu mafi ciwo a rayuwar sa da baze manta ba har ya koma ga Allah, ya kalle ta ya ɓoye damuwar sa yayi murmushi yace "Budurwa kuma? Wacece zata so talakan mutum kamata? Ni bani da wata budurwa ni kaɗai ne, ai nayi ƙarami inyi budurwa"
Murmushi tayi tace "ka fiye abun dariya, a haka kamar baka magana, Amma ka iya sa mutum dariya, yanzu babba da kai kace kayi ƙarami da budurwa?"
"Eh mana ko dan kin gani ƙato? Yarone ni ƙarami"
Ta sake yi masa wani murmushin tace "hmm Shikenan, kodai Widad kake so?"
Zare ido yayi kamar idon ze faɗo yace "Ni, rufamin Asiri, inani ina 'ya' yan manya, ai iyakacin talaka daku yayi muku aiki ku biyashi"
"Amma meyasa kake nuna damuwar ka a kanta haka? Dukda tarin wulaƙanci da rashin mutunci da take maka a wasu lokutan?"
"Saboda batamin wulaƙanci se idan na saɓawa umarnin ta, kuma mahaifinta yana matuƙar mutuntani, kuma kinga nine a ƙarƙashin
ta, dole inyi haƙuri da duk abunda zata yi min"
Amal ta numfasa tace "hakane, Amma ina shiga matuƙar baƙin ciki a duk lokacin da naga tana cin zarafin ka, shiyasa nake ganin meze hana ka ajiye mata aikin ta, in samo maka wani aikin ka huta da wulaƙanci?"

Yusuf yayi Murmushi yace "Inajin daɗin wannan aikin a hakan, bana so kiyi wani abu da ze ɓata ran mahaifiyar ki, Amma ina godiya da karamcinki a kowane lokaci, tunda kin gama, muje in sauke ki a gida nima in tafi, kafin Madam ta farga tare muka fita dake" yai maganar cike da ƙoƙarin basar da maganganun Amal

Amal ta jinjina kai ta miƙe, suka bar gurin.

***************************

"Bayanai sun sameni cewar, Akwai yuwuwar Bala ya tona mana Asiri, yayi iƙrarin cewa tunda aka kaishi prison babu wani ƙoƙari da muke dan fitar dashi, munawa kabmu ƙoƙarine kawai, dan haka na yanke shawarar in kiraka muyi wata magana, fatan zaka buɗe kunnenka ka saurereni"

"To Yallaɓai, ina saurarenka"

"Hashim, Abunda nake so da kai shine, So nake a zuba magani a Abincin daza'a bawa Bala, wanda ze sashi rashin lafiya, daga nan se a kaishi Asibitin doctor Mukhtar, a can nake so a ƙarasamin shi, a kauda shi daga duniyar gaba ɗaya dan baze ɓata mana shiri ba"

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now