AƘIDATA CHAPTER 22_23 (DESTINY)

619 47 2
                                    

_*AƘIDATA*_

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

ELEGANT ONLINE WRITER'S

PART1
Page 22_23

Yusuf yaso yabi bayan Widad dan ya duba ta, amma yasan halinta tsaf zata yanƙwanashi, dan haka ya yanke shawarar tafiya kawai.

Office ya wuce kai tsaye, ya tarar da Suleiman yana shirin fita suka gaisa Suleiman yace "Yusuf akwai wani update ne"?

"Eh yallaɓai gurinka ma nazo"

"shikenan mu koma ciki" suka juya zuwa cikin office ɗin gaba ɗayansu.

Nan Yusuf ya zayyanewa Oga Suleiman komai da yake wakana, akan harkar binciken da batun tafiyar da za suyi, da abunda Nurat ta sanar dashi.

Suleiman yace "Amma baka ganin mu haɗaka da abokan aiki, suyi muku rakiya a wata motar gudun samun matsala?"

Yusuf yace "Insha Allah babu wata matsala Oga, kasan a slide mistake yarinyar nan zata iya ganewa nikuma bana son ta gane komai a yanzu har bincikenmu ya kammala".

"shikenan Yusuf Allah yayi mana jagora, Insha Allah zakayi Nasara ana ta samun haske akan lamarin, bari ni zan fita ne yanzu zanje headquarter"

"to shikenan Yallaɓai a sauka lafiya"

Bayan tafiyar Suleiman Yusuf ya fito yana shirin tafiya, Suka haɗu da Sakina, Sakina tace

"Ashe yau ka samu ka shigo, ban samu na maka murnar ƙarin matsayi ba, Allah ya tayaka riƙo"

Yusuf yace "Ameen nagode"

"sannan ina tayaka murnar rabuwa da mugun aboki wato Abbas"

Cikin mamaki da rashin fahimta yace "kamar yaya?"

"Kamar yadda na gaya maka, Allah ne ya dube ka ya rabaku, a baya nasan koda na faɗa ba zaka yadda ba, yanzunma ban sa ran ka yadda ba amma wataran zaka ce na gaya maka, Allah ya bada sa'a ya tayaka riƙo"

Tayi gaba ta bar Yusuf a gurin yayinda ya bita da kallo.

Da Yusuf ya koma gida yayiwa Umma bayanin tafiyar da zasu yi ya raka Widad, da farko taƙi yadda tace sam bata san zance ba.

Yusuf yace "haba Umma, ya za'ayi nida na ɗau Alƙawarin Yiwa jama'a aiki aikin ya taso kice baza'ayi ba, bayan ke kike cewa inyi gaskiya a aikina? Kina so in bari a cutar da ita ne, ba zan iya jure in ga wani mummunan abu ya sameta ba"

"nifa na kasa gane meke wakana tsakaninka da wannan uwar ɗakin, ka damu da ita dayawa"

"ba wani abu da yake wakana Umman Yusuf, kawai dai mahaifinta na mutuntani ne sosai"

AƘIDA TAWhere stories live. Discover now