Z E E Y A D

50 4 0
                                    

*Z E E Y A D*
'''[The Abandoned Prince]'''

                  *NA*
*JIDDAH BINT MUHAMMAD*


*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION*



_Da yawan ku na cewa wahalar ZEEYAD tayi yawa a sassauta masa, sai dai fah ku sani ba zan canza koh da (A) bane daga cikin labari na, idan zaku karanta a yadda tsarin labarin yazo ku karanta, idan kuma baiyi muku ba na ajiye abina, dama dan ku karanta nakeyi idan kuma kunce bakwa so toh nima kun kawo min sauƙi, sai na ajiye shi kawai, dan haka ku bar ni na tafiyar da abuna yadda na tsara shi please👏🏽, babu abinda zan canza a ciki._



*012...*



...........Koh da sukaje asibiti gwaje-gwaje akayi mata sosai, nan dai aka gano babu wata matsala tattare da ita sannan kuma ba'a yi mata fyaɗe ba, illa ciwon da taji kawai da akayi mata dressing ɗin shi.

Sosai zuciyoyin kowa ya cika da mamaki jin ba'a yiwa DEENAH fyaɗe ba, nan kuma aka fara tuhumar ta akan mai ZEEYAD ɗin yayi mata.

Cikin kuka tace "Babu abinda yayi min, shine yace wai na ɗaga masa skirt ɗina" ta faɗa tana goge hawayen fuskar ta da hannu ganin Kawu na zare mata ido ta baya.

"Yayi attempting yin fyaɗen ne kenan, duk da haka yanada laifi sannan kuma sai hukuma ta hukunta shi da izinin Allah" cewar ɗan Sanda.

"Toh ai shikenan, mu godewa Allah da bai kai ga lalata mata rayuwa ba, ke kuma Fatima ki dinga kula, shiyasa nace zan ɗau yarinƴar nan na kai ta chan ƙauye wurin Uwar gida ta Rakiya amma kika ƙi, da achan take yanzu da babu abinda zai sameta" cewar Kawu.

Shiru kawai Umma tayi tana mai yin hamdala a ranta ganin ba'a lalatawa ƴar ta rayuwa ba.

Sallamar su akayi daga asibitin inda ɗan Sanda yace zasu cigaba da tuhumar ZEEYAD har sai sun gano wasu bayanan game dashi.

Gida suka dawo, abinci kawai Umma ta zuba mata ta bata magani ta sha sannan ta kwanta, har yanzun bata bar kuka ba, A haka bacci ya ɗebe ta anan wurin.

Bata farka ba sai bayan Azahar, dan haka sallah kawai tayi ta zauna ta sake dasa wani sabon kukan.

Zuwa Umma tayi ta zauna kusada ita tace "Menene kuma ƴar albarka, akwai inda keyi miki ciwo ne?."

Kai kawai ta girgiza mata tana cigaba da kuka.

"Toh maiyasa kike kuka?."

"Umma ni babu abinda yayi min ai baiyi min fyaɗen ba tukun kice a fito dashi dan Allah."

Shiru Umma tayi tana janƴo ta jikin ta ta share mata hawaye tace "Yi shiru toh haka nan ki daina kuka kar kisa wa kanki ciwon kai, ai koh bai kai ga yi miki wani abin ba ai yanada laifi tunda yana ƙoƙarin aikatawa ne aka kama shi, kinga dai da abinda ya saka miki koh?, da zuciya ɗaya kika ɗauke shi, kinyi masa halacci ba tare da sanin koh wanene shi ba, yanzu da ya kai ga lalata miki rayuwa fah?, dole ne a hukunta shi sabida gaba, yi shiru haka nan kinji?."

Jafar dai kawai da idanu yake bin su, amma sam bai yarda da abinda DEENAH ta faɗa ba, haka kuma bai yarda da Kawu ba, ganin yadda yake ta rawar ƙafa tunɗazu yana zuwa ya tambayi lafiyar DEENAH abinda bai ta6a yi ba kenan.

Rarrashin ta Umma tayi har saida tayi shiru kafin kuma ta fice zuwa ɗaki.

Sauƙowa Jafar yayi zuwa inda take zaune yace da ita "Kiyi haƙuri DEENAH ki daina kuka haka nan kinji, ai kince baiyi miki komai ba koh?."

Kai ta jinjina masa, nan yace toh "Idan baiyi miki komai ba, waye ne yayi miki, kuma mai ya kai ki wurin shi?."

Shiru tayi bata basa amsa ba tana cigaba da kuka.

ZEEYADWhere stories live. Discover now