Episode 8

5 1 0
                                    

*IZAYAR RAYUWA*🧟‍♀️🧟‍♀️

_*HAFSAT CHIKAJI*_✍️

*8*

   *_Bayan wasu watanni_*

   Duk wani wanda ya san Alhassan saida ya ƙaru dashi, domin duk bayan albashi saiya ware wanda zai kyautatawa al ummar musulmi da wanda zai yiwa yan uwa da makwabta hidima.

  Malam barau ya dawo daga Saudiyya inda har sunje daga chanma suka wuce wurin inna kulu...

    Abu daya dake damun Alhassan shine "matsa mishi da malam Barau yayi game da sai anyiwa hafsat aure.

  A iya saninshi hafsat batada wanda take so , kuma a nashi bangaren baijin zai iya yiwa yarsa daya tilo auren dole.

   Shiyasama kwana biyu ya rage zuwa kauyen, amma malam barau saiya sa tanimu ɗalibinshi ya kira Alhassan din a waya.

   Kamar kullum yauma yana zaune saiga kiran malam barau, a ɗiririce ya dauka "Assalamu alaikum baba"

   Tacan bangaren malam ya amsa da "wa'alaikumus salaam,

   Bayan ƴan gaishe gaishe malam barau yace "nakirane naji an turo zancen hafsatou kuwa? kasan kafin in tafi Saudiyya munyi dakai ina dawowa za'a gama komai ayi biki, to gashi kuma naga na tasamma wata biyu da dawowa amma zancen shiru.

   "Eh baba matsalar ba daga gurinmu bane , na yiwa yaron magana to sai yace babu matsala zai turo amma akwai abinda yake so ya ɗan karasa.

  "Alhassan inaga mafi a'ala kabar zancen Yaron nan, saboda naga abin nashi yanaso ya koma wasa bayan anan ga tarin masu neman aurenta sun hanani sukuni, ko zuwa nan da kuka yi bayan na dawo Saudiyya saida kusan mutum biyar suka sameni da maganar aurenta.

  Yanzu abinda za'a yi shine zan ɗan kara bashi lokaci, idan ya turo to falillahil hamd idan kuma bai Turo ba to zan ba nanan garin dama duk wanda ya riga fitowa sai ayi dashi..

  "To baba babu komai insha Allah, Nagode agaida mama.
  Ji yayi kanshi kamar zai fashe, wai meye abin takura yaga hafsat har yanzu bata cika 16 bama balle ace shekarunta sunyi yawa, gashi ya lura yanzu tana kan ganiyar son karatunta.

   "Dole na nemo mafita"
  abinda Alhassan yace kenan yaci gaba da aikinshi...
   
  Yauma kamar kullum an tashi daga makaranta, tsaye take a bakin premises din makarantar tana so ta fito ta samu adaidaita,
  Saboda tunda wata hudu ta cika driver ya daina musu aiki yace zai kawo musu kaninshi daga kauye.

  Kuma dai har yanzu bai riga ya kawo shiba.

  Wannan mutumin daya ganta kwanakine yauma rike da hannun yarinyar daya dauko ...

   Da sauri ya nufi inda yaga hafsat amma yauma cikin rashin Sa'a yana zuwa gurin yaga babu ita ba alamunta sai dai adaidaita guda biyu da yaga sun wuce .

  Tsakii yayi "mtsweews waini banida Sa'a ne tun ganin farko ban kuma ganin taba sai yau, yau dinma gashi ta ɓace min.

   Husna ce tace "Uncle menene naga ranka ya ɓaci?
  "Babu komai  banjin daɗine amma karki damu"

  "Uncle shikenan yau bazamu siyo ice cream dinba kenan?

  Cikin kosawa da surutun nata ga kuma abin dake damunsa yace "just keep quiet zan kaiki..

   Dariya tayi "yeyy thanks uncle, mota ya shiga itama ta shiga daya side din suka dau hanya.

   Koda hafsat ta isa gida a falour ta tarar da ummanta, baba indo da jikarta murja datazo daga Zaria, itama kusan sa'ar hafsat dince.

IZAYAR RAYUWA Where stories live. Discover now