PAGE 6

98 8 0
                                    

NIMA MATARSA CE
                     NA
      HÀBIBA ABUBAKAR IMAM
                BABI NA SHIDA
                 ****************
   Cikin matsananciyar damuwa Haj murjanatu ta cigaba da girgiza mujaheeda tana Kiran sunanta,cikin firgitacciyar murya.
    Lami ta fado dakin da sauri itama ganin abinda yake faruwa yasa ta tsuguna agaban mujaheeda itama tana Kiran sunanta ,cikin Jan Ido Haj murjanatu ta dubi lami ta bata umarnin tayi saurin taje ta sanar da direba ya fito da mota.
Fitarta yayi dai dai da lokacin da Haj murjanatu ta Mike ta tattagi mujaheeda tana nishi tayo waje da ita sauran hadiman gidan suna ganin ta Suma cike da tashin hankali suka Sanya hannu suka tayata karasawa da mujaheeda wajen mota.nan da nan aka sanyata a mota kowa cikin tashin hankali domin sun san irin wahalar da mujaheeda take sha matukar ciwon zuciyarta ya tashi.

  Haj murjanatu ta kusa tafiya asibitin babu gyale sai da lami ta tuna Mata sannan ta tsaya har lamin ta kawo mata gyalen sannan direba yaja motar a sukwane zuwa care hospital, babban asibitin kudin da mujaheeda take ganin likita a garin jigawa.
   Tun kafin su isa asibitin Haj murjanatu ta Kira Dr Balarabe tasanar dashi suna hanya dafatan Yana asibitin domin ciwon mujaheeda ya tashi. Ya tabbatar Mata da cewa yanzu yake Shirin tashi Amma dole zai tsaya ya Jira zuwansu.

   Isarsu asibitin babu bata lokaci aka ba mujaheeda gado sannan Dr Balarabe ya Fara bata taimakon gaggawa.
  Ayayinda Haj murjanatu ta koma waje ta Sami kujera ta zauna,hawaye ta samu kanta da fitarwa kwarai matuka tana matukar Jin tausayin yarta agame da lalurarta Wanda hakan Yana daya daga cikin dalilan da suka sa take tsaye da Sanya farinciki azuciyar mujaheeda bata kaunar duk wani dalili dazaisa mujaheeda damuwa,
  Hakan yasa tasha alwashin jiyar da ita dadi da gatan da zaisa natsuwa da kwanciyar hankali a rayuwarsa.
  Hakanan ta Sami kanta da addu'ar Allah yasa ba  dalilin abinda yafaru akan Kayan lefen ta bane,Wanda tasan laifinta ne.
  Ahankali ta Ciro wayarta daga cikin Jakarta, ta danna ta Kira Alh Mustapha bugu daya ya dauka Jin muryarta cikin damuwa yasa ya Fara tambayarta abinda ya faru , ahankali ta sanar da Shi suna asibiti da mujaheeda ciwonta ya tashi.
   Cikin damuwa shima ya kashe wayar ya aje komai ya baro kamfanin ya taho asibiti.
  Harya karaso asibitin mujaheeda tana nan inda take har zuwa lokacin bata farfado ba.dr Balarabe da wasu likitoci guda biyu sune akanta.zuwa lokacin kuwa Haj murjanatu taci kuka har taba uku lada, idanunta sunyi jawur.

NI MA MATARSA CE Where stories live. Discover now